Hausa 24

Hausa 24 Ku kasance da (Hausa 24) domin samun ingantattun labarai cikin harshen hausa

Babu Abinda zai hana Tinubu cin zabe a 2027>>Inji Dan majalisa Abdulmumin Jibrin
05/09/2025

Babu Abinda zai hana Tinubu cin zabe a 2027>>Inji Dan majalisa Abdulmumin Jibrin

DA DUMI-DUMI: Yan Vigilanti (yan sa-kai) sun tura sakon gaggawa zuwa ga Bello Turji idan ya isa ya fadi inda yake su kum...
31/08/2025

DA DUMI-DUMI: Yan Vigilanti (yan sa-kai) sun tura sakon gaggawa zuwa ga Bello Turji idan ya isa ya fadi inda yake su kuma za su dauko shi cikin awa 12

Ku yada (sharing) ko a dace ya ga wannan sakon 😆

Ranar HAUSA ta duniya
27/08/2025

Ranar HAUSA ta duniya

Sojoji ba zasu iya magance rashin tsaron arewa ba--Gwamnan KadunaGwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya bayyana cewa yaƙin s...
20/08/2025

Sojoji ba zasu iya magance rashin tsaron arewa ba--Gwamnan Kaduna

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya bayyana cewa yaƙin sojoji da sauran hukumomin tsaro kaɗai ba zai wadatar wajen kawo ƙarshen ta’addanci da ƙungiyoyin masu tayar da kayar baya a Arewacin Najeriya ba.

Yayin wani taron ƙoli na jihohin Arewa maso Yamma da aka gudanar a Kaduna kan rige tsattsauran ra’ayi, gwamnan wanda kwamishinan tsaro na cikin gida, Sule Shuaibu, ya wakilta ya ce tushen matsalar rashin tsaro ya samo asali ne daga talauci, rashin adalci, cin hanci, rashin shugabanci nagari da kuma rashin damar samun aiki ga matasa.

Sani ya jaddada cewa har sai an magance waɗannan dalilai, nasarorin soji za su kasance. Ya yi kira da a ɗauki matakan haɗin gwiwa, haɗa kan al’umma, girmama haƙƙin ɗan adam da tabbatar da adalci wajen yaki da ta’addanci.

Shugaban Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci ta Ƙasa (NCTC), Adamu Laka, ya goyi bayan wannan ra’ayi, inda ya ce ana bukatar tsari na al’umma da ya dogara da bayanan sirri wajen magance matsalar.

Rahotanni sun nuna cewa a cikin shekaru biyu da Gwamna Sani ya shafe a kan mulki, mutane 485 aka kashe yayin da sama da 1,700 aka yi garkuwa da su a Kaduna.

A dai-dai lokacin da ake kashe Al'ummar Katsina Gwamna Dikko Radda na can kasar Waje Yana daukar Salfi Rahotanni daga Ji...
19/08/2025

A dai-dai lokacin da ake kashe Al'ummar Katsina Gwamna Dikko Radda na can kasar Waje Yana daukar Salfi

Rahotanni daga Jihar Katsina sun tabbatar da cewa a yau ‘yan bindiga sun sake shiga cikin wasu garuruwa, inda s**a aikata ta’addanci mai cike da tashin hankali da kisan kai.

Da safiyar yau ne aka samu labarin shigowar barayin cikin Garin Kankara, musamman a unguwar Kofar Fada, inda s**a yi ta harbin kan mai uwa da wabi, s**a hallaka wasu, tare da barin jama’a cikin tsananin fargaba da tashin hankali.

Ba su tsaya nan ba, domin daga nan sai s**a nufi Garin Maitsani da ke cikin Karamar Hukumar Dutsinma, inda s**a sake aikata irin wannan ta’addanci, s**a yi kisa, s**a lalata dukiyoyin al’umma, s**a raba jama’a da kwanciyar hankali.

Rahotanni daga Garin Dan Zangi, shima a cikin karamar hukumar Dutsinma, sun tabbatar da cewa ‘yan ta’addan sun kutsa cikin al’umma, s**a yi barna tare da yin kisa ba tare da jin tsoron hukuma ko kariya daga jami’an tsaro ba.

Yanzu haka dare ya rufe yankin, ga hadari da ruwan sama na shirin sauka, al’umma cikin duhu da fargaba, babu wanda ya san inda wadannan ‘yan ta’addan za su sake nufa. Mutane na ta rokon Allah da addu’ar samun tsira, domin lamarin ya kai matakin da hankula ke gaza dauka.

Sai dai abin takaici shi ne, a daidai wannan lokaci na tashin hankali da fargabar jama’a, rahotanni sun nuna cewa Gwamnan Jihar Katsina na can kasar waje, yana daukar hotuna (selfie) da wayar salula kamar babu abin da ke faruwa a jiharsa. Wannan ya kara tada hankalin jama’a, inda suke tambaya: “Shin haka za mu ci gaba da rayuwa kullum cikin zullumi da tsoro?”

Wannan kuka da damuwa dai ya fito daga bakin Abdullahi Gambo, ɗaya daga cikin mazauna yankin, wanda ya wallafa wannan kuka a kafafen sada zumunta, yana mai bayyana tsananin bakin ciki da damuwa da halin da al’ummar Katsina ke ciki.

DA DUMI-DUMI 👉 Najeriya ta kori 'yan China su 42Hukumar Shige da Fice ta Najeriya (NIS) ta kori ƴan kasar China da Phili...
18/08/2025

DA DUMI-DUMI 👉 Najeriya ta kori 'yan China su 42

Hukumar Shige da Fice ta Najeriya (NIS) ta kori ƴan kasar China da Philippine su 42 da aka same su da laifin damfarar mutane ta intanet ta mayar dasu kasashen su.

Me za ku ce?

Jami'ar Wudil Ta Yi Allah-wadai Da Abinda Wasu Dalibai Mata S**a Yi Na "Ranar Cikin Ƙarya" (Fake Pregnancy Day)Jami’ar K...
14/08/2025

Jami'ar Wudil Ta Yi Allah-wadai Da Abinda Wasu Dalibai Mata S**a Yi Na "Ranar Cikin Ƙarya" (Fake Pregnancy Day)

Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote da ke Wudil a Kano ta yi Allah-wadai da mummunar dabiʼar da wasu ɗalibai mata s**a yi da sunan ʼRanar Cikin Karyaʼ wato “Fake Pregnancy Day” ba tare da izini ba.

Arewa Updates ta rawaito wannan na cikin sanarwar da shugaban sashen kula da harkokin dalibai na jami’ar, Farfesa Abdulkadir Muhammad Dambazau, ya fitar a ranar Laraba 13 ga Agusta 2025.

Sanarwar ta ce wannan abin ya saba ka’idojin ɗabi’ar dalibai kuma ya sabawa ƙa’idojin jami’ar, tare da jawo wa makarantar mummunar illa da ɓata suna da martabarta.

Ta kuma ce jami’ar za ta gano duk wanda ya shirya ko ya taka rawa a wannan abin, tare da ɗaukar matakin ladabtarwa.

Jami’ar ta kuma yi kira ga dukkan dalibai da su kasance jakadu nagari na jami’ar, tare da neman izini kafin gudanar da kowanne irin aiki a nan gaba.

Me za ku ce?

Na kasa samun cikakkiyar nutsuwa ina ji a jikina kamar za'a yaudare ni a zaɓen 2027—Tinubu
12/08/2025

Na kasa samun cikakkiyar nutsuwa ina ji a jikina kamar za'a yaudare ni a zaɓen 2027—Tinubu

Idan baka da rabo: Bayan shekaru 12, James Howells a ƙarshe ya hakura da neman rumbun kwamfutarka da ya jefar da gangan ...
04/08/2025

Idan baka da rabo: Bayan shekaru 12, James Howells a ƙarshe ya hakura da neman rumbun kwamfutarka da ya jefar da gangan a cikin shekarar 2013 wanda ke riƙe da Bitcoin 8,000, yanzu yana buga kusan dala miliyan 950.

A shekara ta 2030, ana iya kimanta shi a dala biliyan 8

Da dumi'dumi: Dangote ya bayyana 'yan 'yansa mata uku amatsayin jagororin kasuwancin sa yanzu.Shahararren ɗan kasuwan Na...
31/07/2025

Da dumi'dumi: Dangote ya bayyana 'yan 'yansa mata uku amatsayin jagororin kasuwancin sa yanzu.

Shahararren ɗan kasuwan Najeriya kuma hamshakin attajirin Afrika Aliko Dangote ya shigar da ‘ya’yansa mata guda uku cikin daular kasuwancin sa.

hamshakin attajirin nan na Najeriya Alhaji Aliko Dangote, wanda Bloomberg ta kiyasta cewa Dukiyarss ta kai dala biliyan 28.5, a ranar 28 ga Yuli, 2025 ne ya fara yin murabus daga wasu rassan Kasuwancin sa.

A watan Yuni, dan kasuwan mai shekaru 68 ya yi ritaya daga aikin hukumar matatar s**ari ta Dangote. A ranar Juma’ar da ta gabata ma ya ajiye mukaminsa na shugaban kamfanin siminti na Dangote, wanda kuma sune kan gaba a kamfaninsa, kafin kaddamar da matatar man da ya kai dala biliyan 20.

Ƴan Bindiga Sun kashe mutane 38 bayan karɓar Miliyan 50 a ZamfaraMutane 38 ne s**a rasa rayukansu a ƙauyen Banga da ke ƙ...
28/07/2025

Ƴan Bindiga Sun kashe mutane 38 bayan karɓar Miliyan 50 a Zamfara

Mutane 38 ne s**a rasa rayukansu a ƙauyen Banga da ke ƙaramar hukumar Kaura Namoda a jihar Zamfara, duk da cewa an biya kuɗin fansar su har naira miliyan 50 ga ‘yan bindigar da s**a sace su.

Shugaban ƙaramar hukumar Kaura Namoda, Mannir Haidara Kaura, ya shaida wa Channels TV cewa ‘yan bindigar sun sace mutum 56, amma daga baya s**a saki 18 kacal. Wadanda aka sako an kwantar da su a asibiti sakamakon azabar da s**a sha a hannun masu garkuwar.

Kaura ya ce gwamnatin jihar ta na shirin kai ziyara domin jajantawa ga iyalan mamatan da lamarin ya shafa.

A cewar wani mazaunin ƙauyen, Ibrahim Banga, ‘yan bindigar sun kai hari watanni baya inda s**a sace mutane 53, sannan s**a buƙaci a biya Naira miliyan ɗaya kan kowane mutum.

Ya ce bayan dogon lokaci da wahala, al’ummar ƙauyen s**a tattara kuɗin s**a kai wa ‘yan bindigar, amma abin takaici mutum 18 ne kawai aka sako.

“Da s**a dawo, sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun yanka sauran mutum 35 ɗin ɗaya bayan ɗaya,” in ji Banga.

Za'a dawo da gawar Fir'auna zuwa Najeriya
24/07/2025

Za'a dawo da gawar Fir'auna zuwa Najeriya

Address

Abuja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa 24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Share on Facebook Share on Twitter Share on LinkedIn
Share on Pinterest Share on Reddit Share via Email
Share on WhatsApp Share on Instagram Share on Telegram