19/08/2025
A dai-dai lokacin da ake kashe Al'ummar Katsina Gwamna Dikko Radda na can kasar Waje Yana daukar Salfi
Rahotanni daga Jihar Katsina sun tabbatar da cewa a yau ‘yan bindiga sun sake shiga cikin wasu garuruwa, inda s**a aikata ta’addanci mai cike da tashin hankali da kisan kai.
Da safiyar yau ne aka samu labarin shigowar barayin cikin Garin Kankara, musamman a unguwar Kofar Fada, inda s**a yi ta harbin kan mai uwa da wabi, s**a hallaka wasu, tare da barin jama’a cikin tsananin fargaba da tashin hankali.
Ba su tsaya nan ba, domin daga nan sai s**a nufi Garin Maitsani da ke cikin Karamar Hukumar Dutsinma, inda s**a sake aikata irin wannan ta’addanci, s**a yi kisa, s**a lalata dukiyoyin al’umma, s**a raba jama’a da kwanciyar hankali.
Rahotanni daga Garin Dan Zangi, shima a cikin karamar hukumar Dutsinma, sun tabbatar da cewa ‘yan ta’addan sun kutsa cikin al’umma, s**a yi barna tare da yin kisa ba tare da jin tsoron hukuma ko kariya daga jami’an tsaro ba.
Yanzu haka dare ya rufe yankin, ga hadari da ruwan sama na shirin sauka, al’umma cikin duhu da fargaba, babu wanda ya san inda wadannan ‘yan ta’addan za su sake nufa. Mutane na ta rokon Allah da addu’ar samun tsira, domin lamarin ya kai matakin da hankula ke gaza dauka.
Sai dai abin takaici shi ne, a daidai wannan lokaci na tashin hankali da fargabar jama’a, rahotanni sun nuna cewa Gwamnan Jihar Katsina na can kasar waje, yana daukar hotuna (selfie) da wayar salula kamar babu abin da ke faruwa a jiharsa. Wannan ya kara tada hankalin jama’a, inda suke tambaya: “Shin haka za mu ci gaba da rayuwa kullum cikin zullumi da tsoro?”
Wannan kuka da damuwa dai ya fito daga bakin Abdullahi Gambo, ɗaya daga cikin mazauna yankin, wanda ya wallafa wannan kuka a kafafen sada zumunta, yana mai bayyana tsananin bakin ciki da damuwa da halin da al’ummar Katsina ke ciki.