14/03/2026
Rikici ya ɓarke tsakanin shugabar ALGON da Alhassan Ado bayan rasuwar jami'in tsaro a wajen "rabon shinkafa"
Rikicin da ke ruwa tsakanin shugabar karamar hukumar Tudun Wada kuma shugabar ƙungiyar kananan hukumomi ta Jihar Kano (ALGON), Hajiya Sa’adatu Salisu da dan majalisar wakilai mai wakiltar Doguwa da Tudunwada, Alhassan Ado Doguwa ya fito fili.
Daily Nigerian Hausa ta gano cewa rikicin ya baiyana ne sak**akon rasuwar wani jami'in hukumar tsaron fararen hula, wato Civil Defense a yayin taron rabon shinkafa da kudade da Alhassan Ado ya shirya a Tudunwada.
Daily Nigerian Hausa ta jiyo cewa jami'in, wanda kawo yanzu ba mu samu sunan sa ba, ya rasu ne bayan an kawo su don tabbatar da zaman lafiya a wajen taron.
Sai dai kuma a wani sako da wallafa a shafin ta na Facebook, Hajiya Sa'adatu ta zargi Alhassan Ado da hannu a kisan jami'in tsaron, inda har ta yi kira ga shugaban ƙasa da ya shiga maganar don ganin an yi hukuncin da ya dace.
A sakon, Sa'adatu ta yi kira ga gwamnatin Tltarayya da ta Jihar Kano da su gaggauta shiga lamarin da ya faru a Tudun Wada domin tabbatar da adalci da kare rayuka da mutuncin al’umma.
Ta kuma yi kira da a dakatar da Hon. Alhassan Ado Doguwa daga duk wasu harkokin siyasa da tarurruka har sai an kammala binciken da ake buƙata.
Ta ce rasuwar matashin babban rashi ne ga iyalansa da al’ummar yankin baki ɗaya, inda ta yi addu’ar Allah Ya jikansa, Ya gafarta masa, tare da bai wa iyalansa, abokansa da daukacin al’ummar Tudun Wada ƙarfin jure wannan babban rashi.
Hajiya Sa’adatu ta jaddada cewa al’umma ba za su ci gaba da kallon irin waɗannan abubuwa na rashin tsaro da asarar rayuka ba tare da ɗaukar matakin da ya dace ba.
Sai dai kuma a nasa martanin, Alhassan Ado ya baiyana takaici kan kisan, inda shi ma ya yi kira ga hukumomin da su ka dace da su gudanar da bincike akan lamarin.
Sai dai kuma Doguwa, wata sanarwa da ya sanya wa hannu ya kuma fitar ga manema labarai, ya nuna bacin ran sa ga wasu maganganu da su ke danganta shi da kisa