26/02/2026
Da Dumi-Dumi
DSS sun saki Walida
Gwamnan jihar Jigawa, Umar Namadi, ya karbi Walida Abdulhadi Ibrahim, yarinyar da aka ce ta bace daga jihar, wadda ta kasance a hannun jami’an DSS.
Gwamnan ya bayyana cewa dukkan batutuwan da s**a shafi zargin sace ta za su bi hanyar doka, yana mai jaddada cewa kotuna ne za su yanke hukunci kan lamarin.
Ya kuma ba da tabbacin cewa za a tabbatar da adalci, tare da tabbatar wa jama’a cewa gwamnati za ta bar doka ta yi aikinta yadda ya kamata.
~ DCL Hausa