Hausa 24

Hausa 24 Ku kasance da (Hausa 24) domin samun ingantattun labarai cikin harshen hausa

“Tsaro Ne Na Farko a Ajandar Tinubu” ~ Inji Ministan Yada LabaraiMinistan ya bayyana cewa gwamnati ta mayar da hankali s...
06/04/2026

“Tsaro Ne Na Farko a Ajandar Tinubu” ~ Inji Ministan Yada Labarai

Ministan ya bayyana cewa gwamnati ta mayar da hankali sosai kan harkar tsaro, tare da ɗaukar matakai don kare rayuka da dukiyoyin ƴan Najeriya.

Ya ce wannan shi ne babban abin da Shugaba Tinubu ya fi bai wa muhimmanci a yanzu.

Ina Nan Lafiya, Babu Wanda Ya K**a Ni, Inji Sadiq Sani Sadiq, Bayan Jita-Jitar K**a Shi Da Ake Yadawa Allah ya kare ka y...
02/04/2026

Ina Nan Lafiya, Babu Wanda Ya K**a Ni, Inji Sadiq Sani Sadiq, Bayan Jita-Jitar K**a Shi Da Ake Yadawa
Allah ya kare ka ya tsare Na gari Da mugun iri

Ku sanya jam’iyyar APC cikin addu’a a wannan dare, domin kusan dukkan manyan jiga-jigan jam’iyyar sun hallara a Eagle Sq...
28/03/2026

Ku sanya jam’iyyar APC cikin addu’a a wannan dare, domin kusan dukkan manyan jiga-jigan jam’iyyar sun hallara a Eagle Square, Abuja, don halartar babban taron kasa wato National Convention.

A wannan taron ne za a zaɓi sabbin shuwagabannin jam’iyyar a matakin ƙasa.

Lamarin babbar dama ce kuma babbar jarabawa ga jam’iyyar, don haka suna buƙatar addu’unku da goyon baya daga gareku ƴan Najeriya

~ Shugaba Bola Ahamed Tinubu.

DSS sun kubutar da sakataren ƙaramar hukumar Kibiya tare da k**a waɗanda su ka yi garkuwa da shiJami’an hukumar tsaron f...
26/03/2026

DSS sun kubutar da sakataren ƙaramar hukumar Kibiya tare da k**a waɗanda su ka yi garkuwa da shi

Jami’an hukumar tsaron farin kaya na DSS sun k**a wadanda s**a yi garkuwa da Sakataren mulki na Karamar Hukumar Kibiya a Kano Hon. Hamza Musa Durba inda s**a kuɓutar da shi k**ar yadda jaridar Arewa Updates ta rawaito.

Bayanan da Arewa Updates ta samu sun nuna cewa jami’an sun kubutar da sakataren ne a wani daji da ke Kibiya bayan da aka soma tattaunawa da wadanda s**a yi garkuwa da shi ta waya.

Jamiʼan sun k**a 2 daga cikin inda aka same su da bindiga ƙirar Ak47.

Ana ci gaba da bincike kan lamarin.

KA JI RABO: Wata tsaleliyar budurwa ta shiga addinin Musulunci a hannun su Malam Adam Ashaka inda ta canza sunanta daga ...
26/03/2026

KA JI RABO: Wata tsaleliyar budurwa ta shiga addinin Musulunci a hannun su Malam Adam Ashaka inda ta canza sunanta daga Joy zuwa Aisha.

Ta bayyana wa Malam Ashaka cewa duka ƴan'uwanta kiristoci ne, tana so ya sama mata mutumin kirki wanda zai aure ta ya koyar da ita Musulunci kuma ta yi ibada cikin kwanciyar hankali.

Kada wanda ya tuntuɓe mu, Malam Ashaka za a tuntuɓa.

Allah ya tabbatar da ita kan sunnar Manzon Allah ya albarkaci rayuwarta.

Saudiyya Ta Umarci Masu Umrah Su Fice Kafin 18 ga Afrilu
24/03/2026

Saudiyya Ta Umarci Masu Umrah Su Fice Kafin 18 ga Afrilu

Duk me yin Azumi yau Alhamis to ya sani wani yake yiwa Azumin ba Allah ba, domin an riga da anga wata a Nijar, inji Shei...
19/03/2026

Duk me yin Azumi yau Alhamis to ya sani wani yake yiwa Azumin ba Allah ba, domin an riga da anga wata a Nijar, inji Sheikh Ayuba Musa Lukuwa.

Me za ku ce?

Wata Babbar Kotun Tarayya ta yanke hukunci a rikicin cikin gida na NNPP, inda ta soke bangaren da ke karkashin jagoranci...
19/03/2026

Wata Babbar Kotun Tarayya ta yanke hukunci a rikicin cikin gida na NNPP, inda ta soke bangaren da ke karkashin jagorancin Rabiu Musa Kwankwaso mai alamar littafi.

Kotun ta kuma tabbatar da sahihancin bangaren jam’iyyar mai alamar kayan marmari, karkashin jagorancin Boniface Aniebonam.

Hukuncin ya kara fito da bangaren shari’a a rikicin siyasar cikin jam’iyyar, tare da nuna cewa kotu ce ke da ikon karshe wajen tantance sahihancin shugabanci a jam’iyyu.

Dakarun Juyin juyi halin musulunci Ƙasar Iran na ruwaSun sami Nasaran k**a jirginl Ruwan yakin haramtaciyar Ƙasar Isra''...
19/03/2026

Dakarun Juyin juyi halin musulunci Ƙasar Iran na ruwa
Sun sami Nasaran k**a jirginl Ruwan yakin haramtaciyar Ƙasar Isra''ila da dukkan Sojojin ruwan isra''ila Dake cikin jirgim ruwan
sun dauka Dakarun iran din suna bacci ne yau kwana 13 kenan da fara yakin kusan kullum Amùrkà da isra''ila suna daukar kaskanci Allah ya kara baiwa Iran nasara Allah zai cika haskensa koh da kafurai da munafukai basa so

- Engr Danladi S kaduna

WATA SABUWA: Hassada Da Munafurci Kedamun Yan Arewa, Kowa In Aka Bashi Shinkafar Nan Karba Zaiyi, Amma Saboda Son Zuciya...
17/03/2026

WATA SABUWA: Hassada Da Munafurci Kedamun Yan Arewa, Kowa In Aka Bashi Shinkafar Nan Karba Zaiyi, Amma Saboda Son Zuciya Gashi Yan Arewa Suna Cewa An Nada Wani Sarkin Shinkafar Ƙasar Hausa, To Saura Sarkin Munafikan Kasar Hausa, Karkusa Nuhu Abdullahi Yayi Fushi Yadaina Karbo Mana Shinkafar Nan Dai~ Rabi'u Daushe.

Malamin addinin Musulunci, Abduljabbar Nasir Kabara, ya rubuta takardar ƙorafi zuwa ga shugaban kotun ɗaukaka ƙara na Na...
16/03/2026

Malamin addinin Musulunci, Abduljabbar Nasir Kabara, ya rubuta takardar ƙorafi zuwa ga shugaban kotun ɗaukaka ƙara na Najeriya inda ya zargi cewa ana shirin yi masa makarkashiya a Kano.

A cikin takardar, Sheikh Abduljabbar ya bayyana cewa shirin da ake yi na rushe Gidan Yarin Kurmawa na iya zama wata dabara da za ta haifar da bacewar muhimman takardun shari’ar da ake yi da shi.

Malamin ya nuna damuwa cewa rushe gidan yarin na iya shafar yadda za a adana ko kuma samun wasu muhimman bayanai da s**a shafi karar da ake yi a kansa.

A halin yanzu dai gwamnatin Kano na ci gaba da shari’a da Sheikh Abduljabbar kan zargin batanci ga Fiyayyen Halitta, Annabi Muhammad (SAW).

A baya kotu ta yanke masa hukuncin kisa kan wannan zargi.

Sai dai ana sa ran kotun daukaka kara za ta duba korafin da malamin ya gabatar tare da yanke hukunci kan batutuwan da ya gabatar.

Rikici ya ɓarke tsakanin shugabar ALGON da Alhassan Ado bayan rasuwar jami'in tsaro a wajen "rabon shinkafa" Rikicin da ...
14/03/2026

Rikici ya ɓarke tsakanin shugabar ALGON da Alhassan Ado bayan rasuwar jami'in tsaro a wajen "rabon shinkafa"

Rikicin da ke ruwa tsakanin shugabar karamar hukumar Tudun Wada kuma shugabar ƙungiyar kananan hukumomi ta Jihar Kano (ALGON), Hajiya Sa’adatu Salisu da dan majalisar wakilai mai wakiltar Doguwa da Tudunwada, Alhassan Ado Doguwa ya fito fili.

Daily Nigerian Hausa ta gano cewa rikicin ya baiyana ne sak**akon rasuwar wani jami'in hukumar tsaron fararen hula, wato Civil Defense a yayin taron rabon shinkafa da kudade da Alhassan Ado ya shirya a Tudunwada.

Daily Nigerian Hausa ta jiyo cewa jami'in, wanda kawo yanzu ba mu samu sunan sa ba, ya rasu ne bayan an kawo su don tabbatar da zaman lafiya a wajen taron.

Sai dai kuma a wani sako da wallafa a shafin ta na Facebook, Hajiya Sa'adatu ta zargi Alhassan Ado da hannu a kisan jami'in tsaron, inda har ta yi kira ga shugaban ƙasa da ya shiga maganar don ganin an yi hukuncin da ya dace.

A sakon, Sa'adatu ta yi kira ga gwamnatin Tltarayya da ta Jihar Kano da su gaggauta shiga lamarin da ya faru a Tudun Wada domin tabbatar da adalci da kare rayuka da mutuncin al’umma.

Ta kuma yi kira da a dakatar da Hon. Alhassan Ado Doguwa daga duk wasu harkokin siyasa da tarurruka har sai an kammala binciken da ake buƙata.

Ta ce rasuwar matashin babban rashi ne ga iyalansa da al’ummar yankin baki ɗaya, inda ta yi addu’ar Allah Ya jikansa, Ya gafarta masa, tare da bai wa iyalansa, abokansa da daukacin al’ummar Tudun Wada ƙarfin jure wannan babban rashi.

Hajiya Sa’adatu ta jaddada cewa al’umma ba za su ci gaba da kallon irin waɗannan abubuwa na rashin tsaro da asarar rayuka ba tare da ɗaukar matakin da ya dace ba.

Sai dai kuma a nasa martanin, Alhassan Ado ya baiyana takaici kan kisan, inda shi ma ya yi kira ga hukumomin da su ka dace da su gudanar da bincike akan lamarin.

Sai dai kuma Doguwa, wata sanarwa da ya sanya wa hannu ya kuma fitar ga manema labarai, ya nuna bacin ran sa ga wasu maganganu da su ke danganta shi da kisa

Address

Abuja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa 24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share