Hausa 24

Hausa 24 Ku kasance da (Hausa 24) domin samun ingantattun labarai cikin harshen hausa

Da Dumi-Dumi DSS sun saki WalidaGwamnan jihar Jigawa, Umar Namadi, ya karbi Walida Abdulhadi Ibrahim, yarinyar da aka ce...
26/02/2026

Da Dumi-Dumi

DSS sun saki Walida

Gwamnan jihar Jigawa, Umar Namadi, ya karbi Walida Abdulhadi Ibrahim, yarinyar da aka ce ta bace daga jihar, wadda ta kasance a hannun jami’an DSS.

Gwamnan ya bayyana cewa dukkan batutuwan da s**a shafi zargin sace ta za su bi hanyar doka, yana mai jaddada cewa kotuna ne za su yanke hukunci kan lamarin.

Ya kuma ba da tabbacin cewa za a tabbatar da adalci, tare da tabbatar wa jama’a cewa gwamnati za ta bar doka ta yi aikinta yadda ya kamata.

~ DCL Hausa

Idan za muyiwa tinubu adalci mulkin sa na shekara uku ya nunka mukin Buhari da muke ta cewa ai masa uzuri a bashi lokaci...
25/02/2026

Idan za muyiwa tinubu adalci mulkin sa na shekara uku ya nunka mukin Buhari da muke ta cewa ai masa uzuri a bashi lokaci har na tsawon shekaru 8 to Tinubu a shekara uku ya samar da cigaba a fannin tsaro fiye da Buhari nesa ba kusa ba, wannan idan fa zamuyi adalci mu fadi gaskiya kenan, domin Buhari da casa'in cikin 100 na gwamnatin sa yan Arewa ne, ance sunyi kokari amma dai mu abin da muka gani shine sunbar abubuwa sun rincaɓe da gangan a yankin su tsawon shekaru 8~Prof Maqari.

Allah yasa Abba yaji Sakon Shugaban Kasa ya cire Mana Jarhular mu ~ Samir Rufai Hanga Kamar yadda mai girma shugaba Tinu...
24/02/2026

Allah yasa Abba yaji Sakon Shugaban Kasa ya cire Mana Jarhular mu ~ Samir Rufai Hanga

Kamar yadda mai girma shugaba Tinubu yace yaji dadin ganin Mai Girma Alhaji Abba Kabir a cikin su amma sai dai har yanzu da Jar hula a kanshi, wannan sako ne Tinubu ya aikawa Gwamna, Allah yasa yaji ya cire mana Jar hular mu.

Mezakuce?

'Yan Bindiga Sun Buƙaci Malamai Su Biya Harajin Naira Miliyan 100 Kafin Su Basu Izinin Yin Tafsirin Ramadan A Garin Utou...
23/02/2026

'Yan Bindiga Sun Buƙaci Malamai Su Biya Harajin Naira Miliyan 100 Kafin Su Basu Izinin Yin Tafsirin Ramadan A Garin Utouno Dake Ƙaramar Hukumar Ngaski A Jihar Kebbi

KO KUNSAN MASIFAR DA SHEIK SANI KHALIFA KE CIKI TAFI WACCE EL-RUFAI KE CIKI👇Juyin Mulki (Coup)Juyin mulki ana daukarsa a...
23/02/2026

KO KUNSAN MASIFAR DA SHEIK SANI KHALIFA KE CIKI TAFI WACCE EL-RUFAI KE CIKI👇

Juyin Mulki (Coup)
Juyin mulki ana daukarsa a matsayin:
-Barazana ga tsaron kasa
-Cin amanar kasa
-Yunkurin kifar da gwamnati

A kasashe da dama, hukuncinsa na iya kaiwa:
-Daurewa na dogon lokaci
Rai da rai (life imprisonment)
-Ko hukuncin kisa a wasu kasashe

Misali:
A Nigeria, juyin mulki ana daukarsa babban laifi na cin amanar kasa.

A Turkey bayan yunƙurin juyin mulki na 2016, an daure dubban mutane.

Satar Kudi (Financial Crime / Corruption)
Satar kudi ma babban laifi ne, amma yawanci:

-Ana iya samun beli
-Ana iya daure mutum shekaru
-Wani lokaci ana iya kwato kudin a rage hukunci

Misali:
A Brazil an daure manyan shugabanni kan zargin cin hanci.

A South Africa ma an gurfanar da tsofaffin shugabanni kan cin hanci.

Don haka wa yafi shiga matsala?

✔ Idan aka tabbatar:
- Juyin mulki yafi hadari kuma hukuncinsa yafi tsanani.
- Satar kudi ma laifi ne mai tsanani,

amma yawanci baya kaiwa matakin hukuncin juyin mulki....

ALLAH SARKI: Mawaƙi Sani Mai Bango Kenan Wanda Ya Yi Waƙar Nan Mai Taken 'Ina Ma, Ina Ma, Ina Ma Da Naira, In More Arzik...
23/02/2026

ALLAH SARKI: Mawaƙi Sani Mai Bango Kenan Wanda Ya Yi Waƙar Nan Mai Taken 'Ina Ma, Ina Ma, Ina Ma Da Naira, In More Arzikina' Cikin Yanayi Na Rashin Lafiya

Kungiyar mawakan Hausan nan mai suna 'Murya Daya' karkashin jagorancin Ali Jita sun kai masa ziyara har gidansa dake Gadar Tamburawa a Kano, inda s**a kai masa tallafin kayan abinci.

Na san da yawanku sun san wannan wakar tasa a shekarun baya "Ina ma ina ma, ina ma da naira, in more arzikina, Allah Ka aiko da naira in more arzikina, Allah ba ni in bada in yi sadaka in yi kyauta inji dadin rayuwata".

TSAKA MAI WUYA 🔥: Rahotonni Sun Tabbatar Da Cewar Hukumar Efcc Tasake Gayyatar Tsohon Gwamnan jihar Kaduna Nasiru Ahmad ...
20/02/2026

TSAKA MAI WUYA 🔥: Rahotonni Sun Tabbatar Da Cewar Hukumar Efcc Tasake Gayyatar Tsohon Gwamnan jihar Kaduna Nasiru Ahmad El Rufa'i Domin Yadawo Yaci Gaba Da Amsa Tambayoyi, Rahoton Ya Nuna Yanzu Haka Jami an Hukumar Suna Jibge A Kofar Shiga Hukuma ICPC Wurinda Tsoron Gwamnan Yake Tsare Domin Da Zarar Sun Sallame shi Efcc din Su kara Komawa Dashi ofishin sa, Zarge Zargen Al mundahanar Kudade Ne S**a Da Bai Baye Tsohon Gwamnan jihar Kaduna.

Wanda kuka ji yana min Izgili saboda ina yawan ambaton Allah, Allah ne ya matsa bakin sa, kuma ina so ko Ranar Alƙiyama ...
20/02/2026

Wanda kuka ji yana min Izgili saboda ina yawan ambaton Allah, Allah ne ya matsa bakin sa, kuma ina so ko Ranar Alƙiyama Allah ya matsa bakinsa yaimin irin wannan shaidar

Inji Malam Ibrahim Shekarau

Inna Lillahi Wa Inna Ilaihi RajiunAllah Ya Yi Wa Farfesa Umma Abdulwahid Rasuwa Fittacciyar Farfesa Ta Rasu Ne A Sanadiy...
19/02/2026

Inna Lillahi Wa Inna Ilaihi Rajiun

Allah Ya Yi Wa Farfesa Umma Abdulwahid Rasuwa

Fittacciyar Farfesa Ta Rasu Ne A Sanadiyar Hatsarin Mota Ne A Kusa Da Kura A Hanyar Kano Zuwa Kaduna.

Allah Ya Jiƙan Ta Da Rahama.

DA DUMI DUMI: Kungiyoyin Matasa Magoya Bayan Tsohon Gwamnan jihar Kaduna Malam Nasiru Ahmad El Rufa'i Sun Umurci Membobi...
17/02/2026

DA DUMI DUMI: Kungiyoyin Matasa Magoya Bayan Tsohon Gwamnan jihar Kaduna Malam Nasiru Ahmad El Rufa'i Sun Umurci Membobinta Na Dukkanin Fadin Jihar Kaduna Da Su Fara Aiwatar Da Alqunut Acikin Sallar Isha i da Asuba Daga Yau 17/2/2026 Don Addu'ar Allah Ya Karya Makiyan Malam, Alh Mansur Sani Tudun Wada Zariya Yace Tuni Shugabannin Kungiyoyin S**a Bayar Da Umurnin Cikin Gaggawa Domin Dakile Ƙoƙarin Zaluncin Da Ake Shirin Yiwa Tsohon Gwamnan, Shugabancin Ƙungiyar Kuma Yace Babu Gudu Babu Jada Baya Wajen Tsare Mutuncin Malam.

Wasu dagacikin sojojin America da s**a shigo Nigeria, sun sauka Maiduguri jahar Borno.
16/02/2026

Wasu dagacikin sojojin America da s**a shigo Nigeria, sun sauka Maiduguri jahar Borno.

Akwai abin kunya ace kullum da kalaman siyasa ake kada tunanin ayi chan dakai ayi nan dakaiNasiru elrufai wanda akafi za...
14/02/2026

Akwai abin kunya ace kullum da kalaman siyasa ake kada tunanin ayi chan dakai ayi nan dakai

Nasiru elrufai wanda akafi zarga akan batan Dadiyata sabo da ya kware wajen s**ar gwamnatin sa kuma Dan garinsa marar ra'ayinsa

Elrufai Bai taba jajen Dadiyata ga iyalansa ba ko a gwamnatance b***e ya tofa wani abu akansa, ba ruwansa da batan sa kwata kwata

Kwankwaso shine mutumin da yafi kowa a kasar nan cikin manya shiga lamarin batan Dadiyata kasancewar sa Dan kwankwasiyya

wata Rana cikin alhini yake cewa ya tuntubi duk wata kafa ta tsaro a nigeria sun tabbatar masa Dadiyata baya hannunsu

amma duk da tsanin adawa dake tsakanin su bai zargi ganduje akan batan sa ba wanda kuma na tabbata da akwai kishin kishin hannun ganduje da sai ya fada ko mai zai faru kuwa

Elrufai yana cikin masifa don sai sun kamashi yanzu yana Neman abokin mutuwa ko Shima ya samu gabar da zai shako wani su tafi tare tunda Shima da karya da gaskia zaa tuhumeshi

Kowaye yake da hannun muna addua Allah ya tona masa asiri ko waye, amma dai mu a yan adam muna yiwa mutum hukunci da abinda yake a record din sa na rayuwa

Daga Muhammad Muzammil Mandawari

Address

Abuja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa 24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Share on Facebook Share on Twitter Share on LinkedIn
Share on Pinterest Share on Reddit Share via Email
Share on WhatsApp Share on Instagram Share on Telegram