24/02/2023
Ina yi masa kyakykyawan zato tare da tarin hujjoji da dalilai wadda ko gaban Allah zan faɗi hujjar neman arziki na mabayin da nake dasu su dangwala masa kuri'a ranar asabar .
Har cikin zuciyata na gamsu da cancantarsa da kuma kokarinsa, tare manufofin da yake tafe dasu domin alheri ne ga al'ummar najeriya, Allah muna roƙonka ka bawa Dr.Rabiu Musa Kwankwaso Mulkin kasar mu najeriya 2023.
duk yan Nigeria da s**a yadda da fifikon nagartar Kwankwaso akan sauran zasu taru su zabe shi ranar Asabar, ba tare da kallon girma ko kankantar jam’iyyar sa ba, da ratar da zai bawa Tinubu da Atiku ba yar kadan bace.
Mu tabbatar munyi zabe da kyakyawan manufa babu ruwanka da abun da abokan adawar sa suke fadi cewa ba baici zabe ba , duk mai cikakken imani yasan cewa mulki dai Allah yake ba dashi alokacin daya ga dama .
Masu cewa ba zai ce zabe ba wata kila Ubangiji yana shawara dasu shiyasa suke fadin hakan .
Mu zabe nagari domin cigaban kasar mu najeriya.
©️BELLO ABDULLAHI SALEH
Gombe North Peace Ambassador Youths Awarenesses Forum.