YUSAN TV

YUSAN TV yusan television Kafar zamani domin ilman tarwa, fadakarwa, da nisha Dantarwa. muna maraba da kowa domin tallata maku hajarku a duk inda kuke a Fadin Duniya.

Tauraruwar Sanata Marafa Ta Fara Haskawa Akan Zama Gwamnan Zamfara
10/03/2026

Tauraruwar Sanata Marafa Ta Fara Haskawa Akan Zama Gwamnan Zamfara

ALHAJI MUSA USMAN FUNTUAADC STATE CHAIRMAN KATSINA STATEJagora mai hangen nesa, ginshiƙin adalci da gaskiya a siyasa.Mut...
10/03/2026

ALHAJI MUSA USMAN FUNTUA
ADC STATE CHAIRMAN KATSINA STATE

Jagora mai hangen nesa, ginshiƙin adalci da gaskiya a siyasa.
Mutumin da ya ɗauki nauyin gina jam’iyya da haɗa kan al’umma domin cigaban Katsina State.

Alhaji Musa Usman Funtua — gwarzon shugabanci, mai ƙarfi wajen tsayawa kan gaskiya, kuma madubin nagarta ga matasa da manya.

Jagora mai kishin ƙasa, wanda zuciyarsa ke bugawa da burin ganin talaka ya samu ci gaba.
A karkashin jagorancinsa, ADC na ƙara haskawa kamar tauraro a sararin siyasar Najeriya.

Funtua ba wai suna kaɗai ba ne — alama ce ta jajircewa, amana da hangen nesa.

Allah ya ƙara basira da ikon jagoranci domin cigaban jam’iyya da al’ummar Katsina baki ɗaya.

Follow ADC MEDIA TV 📺

Hon Nasiru Zurmi Commissioner of land and housing, ya mika takardar sa ta tabbatar da barinsa jam’iyar PDP, zuwa jam’iya...
10/03/2026

Hon Nasiru Zurmi Commissioner of land and housing, ya mika takardar sa ta tabbatar da barinsa jam’iyar PDP, zuwa jam’iyar APC domin nuna goyon bayan sa ga Mai Daraja Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal,

Ya hannunta takardar shedar shiga jam’iyar APC ga Ciyamomin ward gona sha ɗaya dake karamar hukumar mulki ta Zurmi, Haka Suma shugabanin Jam'iyyar PDP Sun Bayyana barin Jam'iyyar PDP Bisa dalilin Kwamishinan Duk da Kasan cewar Basu taɓa wani party ba bayan pdp.

10/03/2026

Ramadan Tafsir: 21 | Imam (Dr). Aminu Ibrahim Daurawa

Masallaci: Hakimin Doma
Unguwa: Jeka da Fari

21 Ramadan 1447
10 March 2026

Wamban Shinkafi Ya Gudanar da Buda Baki Tare da Al’ummar Jihar ZamfaraAn gudanar da taron buda baki tare da al’umma a gi...
10/03/2026

Wamban Shinkafi Ya Gudanar da Buda Baki Tare da Al’ummar Jihar Zamfara
An gudanar da taron buda baki tare da al’umma a gidan Dr. Sani Abdullahi, Wamban Shinkafi, inda ya gayyaci al’ummar Jihar Zamfara domin yin buda baki tare a wannan wata mai alfarma na Ramadan.

Taron wanda ya gudana a gidansa, ya samu halartar mutane da dama daga sassa daban-daban na jihar, ciki har da manyan baki, abokai da magoya baya. An gudanar da buda bakin cikin yanayi na zumunci da hadin kai, inda mahalarta s**a samu damar yin ibada tare da kuma tattauna muhimman batutuwa da s**a shafi al’umma.

A yayin taron, mahalarta sun yaba da wannan kyakkyawan shiri na Dr. Sani Abdullahi Wamban Shinkafi, inda s**a bayyana cewa irin wannan haduwa tana kara dankon zumunci da hadin kan al’umma musamman a watan Ramadan.

Taron ya kuma kasance dama ta yin addu’o’i na musamman domin samun zaman lafiya da cigaban Jihar Zamfara da kuma kasa baki daya.

10/03/2026

Hon Nasiru Zurmi Commissioner of land and housing, ya mika takardar sa ta tabbatar da barinsa jam’iyar PDP, zuwa jam’iyar APC domin nuna goyon bayan sa ga Mai Daraja Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal,

Ya hannunta takardar shedar shiga jam’iyar APC ga Ciyamomin ward gona sha ɗaya dake karamar hukumar mulki ta Zurmi, Haka Suma shugabanin Jam'iyyar PDP Sun Bayyana barin Jam'iyyar PDP Bisa dalilin Kwamishinan Duk da Kasan cewar Basu taɓa wani party ba bayan pdp.

10/03/2026

Ramadan Tafsir: 21 | Imam (Dr). Aminu Ibrahim Daurawa

Masallaci: Mai Unguwa Doma
Unguwa: Jeka da Fari

21 Ramadan 1447
10 March 2026

21/GA/RAMADAN Shugaban Karamar Hukumar Mulkin Bungudu Hon Nura NU Ya Kaddamar Da Bada Tallafin Kayan Abinci Wadan Hukuma...
10/03/2026

21/GA/RAMADAN

Shugaban Karamar Hukumar Mulkin Bungudu Hon Nura NU Ya Kaddamar Da Bada Tallafin Kayan Abinci Wadan Hukumar Warwala Da Jindadi Al'ummar S**a Kawoma Karamar Hukumar Bungudu

Wannan Bada Tallafin Yabiyu Bayan Ganin Yadda Shugaban Karamar Hukumar Bungudu Yake Fadi Tashi Don Ganin Al'ummar Bungudu, Ba'a Barsu A Baya Ba, Wajan Samun Abubuwa Na More Rayuwa Da Kawo Tallafin Acikin Mazabun Mu Goma Shadaya (11)

Haka Zalika Shugaban Yayi Kira Ga Wadan Da S**a Amfana Da Wannan Tallafin, Da Suyi Aiki Dasu Kamar Yadda Yadace, Basuje Susaida Suba Ko Akasin Haka Ba.

Umar Faruk
Media Aide To Executive Chairman Bungudu Local Government

10/03/2026

21- Ramadan - 1447 AH
10th- February- 2026

Alhamdulillah.!!!
🌹🌹🌹🌹🌹🌹
📚📚📚📚📚📚📚

Tafsirin Alkur'ani Mai Girma kenan Daga Zawiyyar Sheikh Muhammad Balarabe Gusau.
🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌

Day - 21
Rana ta Ashirin Da Daya.

Tare Da Mai Gabatarwa:
Dr. Atiku Shehu Balarabe Zawiyya Gusau

Daukar nauyi dan Majalisar dokokin tarayya Hon Kabiru Amadu Mai Palace

# #

10/03/2026

An interview with Dr Sani Abdullahi Wamban Shinkafi about Dr Dauda Lawal dump pdp for Apc

Tattaunawa da Dr. Sani Abdullahi (Wamban Shinkafi) Kan Batun Ficewar Gwamna Dauda Lawal Daga PDP Zuwa APC

A wata tattaunawa ta musamman, Dr. Sani Abdullahi Wamban Shinkafi ya yi tsokaci kan rade-radin da ake yi cewa Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, na shirin ficewa daga jam’iyyar People's Democratic Party (PDP) zuwa jam’iyyar All Progressives Congress (APC).

Da yake amsa tambayoyi daga manema labarai, Wamban Shinkafi ya bayyana cewa a tsarin dimokuradiyya, sauya sheƙar jam’iyya hakki ne na kowane ɗan siyasa idan ya ga hakan zai amfani al’ummarsa da kuma tafiyar siyasa. Ya ce siyasa tana tafiya ne da yanayi da kuma muradun jama’a, don haka bai kamata a dauki batun sauya jam’iyya a matsayin abin mamaki ba.

Dr. Sani Abdullahi ya kara da cewa idan har Gwamna Dauda Lawal ya yanke shawarar sauya sheƙa daga PDP zuwa APC, to wajibi ne a duba dalilan da s**a sa ya dauki wannan mataki. A cewarsa, wani lokaci shugabanni kan dauki irin wannan mataki ne domin samun karin hadin kai da kuma goyon bayan gwamnatin tarayya domin kawo ci gaba ga jiharsu.

Ya kuma jaddada cewa al’ummar Zamfara suna bukatar zaman lafiya, cigaba da kuma shugabanci nagari fiye da komai. Saboda haka duk wata shawara da za ta kawo ci gaba ga jihar ya kamata a yi ta ne cikin hikima da tuntuba.

Wamban Shinkafi ya bukaci ‘yan siyasa da magoya baya da su rika gudanar da harkokinsu cikin lumana tare da guje wa kalaman da ka iya jawo rikici. Ya ce siyasa ba fada ba ce, kuma babban abin da ya kamata a sa gaba shi ne ci gaban al’umma..

A karshe, ya jaddada cewa lokaci ne kawai zai bayyana gaskiyar batun sauya sheƙar jam’iyyar, amma abin da ya fi muhimmanci shi ne a tabbatar da cewa duk wani mataki da shugabanni za su dauka zai amfani al’ummar Jihar Zamfara baki daya.

10/03/2026

21: Tafsirin Alqu’arni Mai girma

10/03/2026

WAMBAN SHINKAFI IFTAR

KAITSAYE DAGA GIDAN DR SANI ABDULLAHI WAMBAN SHINKAFI WURIN YIN BUDA BAKI DA AL'UMMAR JIHAR ZAMFARA

Address

GUSAU
Gusau

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when YUSAN TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Share on Facebook Share on Twitter Share on LinkedIn
Share on Pinterest Share on Reddit Share via Email
Share on WhatsApp Share on Instagram Share on Telegram