Abu Nihlah As-Salafiy

Abu Nihlah As-Salafiy Researcher and Observer on Islamic Issues and Comparative Religions

01/08/2023

In ka samu ikon amfanar kai ko wasu, ba a jira, marmaza kayi me ya dace, domin ba kada tabbacin samun ikon nan gaba, ta yiwu wannan ce ɗorarriya!

01/08/2023

Kar ka jira sai ka samu dama za ka gyara kuskure, kana gane kuskure gyara shi kawai, domin damarmakin za suyi ta zuwa baka iya zaɓar ɗaya ciki ba!

It wasn't a wise idea to forbid your daughter from being dating in the name of she is studying, she may take a chance in...
01/08/2023

It wasn't a wise idea to forbid your daughter from being dating in the name of she is studying, she may take a chance in her boy friend's room imperceptibly.

24/07/2023

Taƙaici ne Mai Ƙuna Rai da Baƙanta Rai kaga MUSULMI ya mato kan wani FITACCEN ƊAN ƘWALLO ko wani SHARARREN MAWAƘI da sun tsani ADDININ ALLAH da MANZON ALLAH (S.A.W.)

YA MATSAYAR Laylah Ali Othman kan AURE?HADISI daga Sahabi Abu Sa'id Al-Khudriy (R.A.) yake cewa: Wani mutum ya zo da ɗiy...
18/05/2023

YA MATSAYAR Laylah Ali Othman kan AURE?

HADISI daga Sahabi Abu Sa'id Al-Khudriy (R.A.) yake cewa: Wani mutum ya zo da ɗiyar sa wajen Annabi (S.A.W.) sai ya ce: Haƙiƙa ƴata wannan taƙi aure, yace: sai (Manzo - S.A.W.) yace mata: "Ki yiwa Mahaifin ki Biyayya" sai ta ce: 'A'a, har sai ka bani labarin me ne haƙƙin miji a kan matarshi?' ta yita maimaita masa maganar ta, sai ya ce: "Haƙƙin Miji a kan matar shi, da za ace yana da wasu ƙuraje (fasassu) a tare da shi, sai ta lashe su, ko kuma ƙofofin hancin shi zasu riƙa kwaranyar da ruwan mugunya ko jini sannan ta lashe, bata bashi haƙƙin shi ba" sai ta ce: "Na rantse da Wanda ya aiko ka da Gaskiya, ba zan taɓa aure ba har abada, sai (S.A.W.) ya ce: "Kar ku aurar da su sai da izinin su" (Ibn Abi Shaibah)

Fa'ida: Wannan HADISI yayi nuni halarcin barin yin aure saboda uzuri, duk da abin da yafi shi ne yin auren saboda kwaɗaitarwa da Shari'ah tayi kan shi, da kuma hanin da tayi kan ƙaurace masa. Illa kawai wasu lokutan yana zama WAJIBI idan an ji tsoron afkawa Al-Fashah (ZINA).

AURE ba a bashi hukunci guda a Shari'ah domin hukuncin shi kan bambanta duba da yanayin da mutum yake ciki, saboda yana daga mafiya ƙarfi cikin abubuwan da aka shar'anta. AURE Sunnah ce ta Manzonni (A.S.) kamar yadda tarun AYOYI da HADISAI dake kwaɗaitarwa kan yin aure ke nuni. Babu kokonto bare shakku kan WAJIBCIN shi ga wanda yake da iko kuma yake da matsananciyar sha'awar da yana jiyewa kan shi tsoron faɗawa Al-Fashah, namiji ko mace, haka wanda yake a wajen da zai iya ruɗuwa ya afkawa Zina, sannan kafatanin ilahirin malamai sun haɗu kan babu Ibadah Mafi Ƙarfi irin shi ga wanda ya samu dama.

Shari'ah tayi hani ƙaƙƙarfa kan ƙauracewa yin shi. HADISI yayi hani dangane da TABATTULI wato ƙauracewa Aure domin doƙufa kan Ibadar Allah. Sa'ad bin Waqqas (R.A.) ya ce: Tabbas Manzon Allah (S.A.W.) ya mayarwa Usman bin Maz'un (bakancen) TABATTULI da yayi, da kuwa ya bashi izini, da mun fiɗiye kan mu'

Shi yasa Imam Ahmad bin Hanbal yake cewa: "Zaman Gwauranta ba ya daga cikin wani abu na Musulunci, duk kuwa wanda ya kira ka zuwa ga rashin yin aure, ya kiraye ka zuwa ga saɓanin Musulunci"

Hakan yasa, har ya ta kai ma Manzo (S.A.W.) ya barranta/nesanta wanda ya ƙauracewa aure da cewa baya tare da shi, HADISI daga Nana A'ishah (R.A.) tace: Manzon Allah (S.A.W.) ya ce: "AURE na daga Sunnah ta, duk wanda bai yi aiki da Sunnah ta ba, baya daga gare ni, kuyi aure, domin zan yiwa al'ummomi alfahari daku, duk wanda ya kasance mai hali, to yayi aure, wanda kuma bai damu hali ba, to yayi Azumi, domin Azumin zai zamar masa dandaƙa." (Ibn Majah).

Tsokaci: AURE ya kan zama WAJIBI ko SUNNAH, kuma HARAMUN ƙauracewa yin aure, koda kuwa an yi da zimmar doƙufa kan bautar Allah, bare kuma ya kasance saboda duniya, illa idan mutum yana jin tsoron sauke nauye-nauye da ke cikin shi da haƙƙoƙin shi, nan Shari'ah ta bashi dama. Idan kuma yana jin tsoron afkawa Al-Fashah, to yin auren shi ne yafi, musamman a wannan lokaci mai tsananin Fitina. Sannan ga Mace wadda ta yanke ba zata yi aure ba sai ta kiyaye iyakokin Shari'ah.

HUKUNCIN neman saki da Layla Ali Othman tayi?

In har da wata mishkila ta cutarwa ko fita daga rai ko jin ba zata iya biyayya ba, Shari'ah ta yiwa mace sassauci, amma in babu uzuri kawai saboda wannan ra'ayi ne HADISI ya zo kan haka:

"Duk macen da ta nemi mijin ta ya sake ta ba tare da wata mishkila ba, Ƙamshin Al-Jannah ya haramta gare ta" (Sunan Al-Tirmidhi)

Ƙamshin Al-Jannah ana jin shi daga wajen da ya kai tazarar shekara ɗari biyar wacce wannan ita ce tazara mafi nesa, amma saboda irin Girman Laifin da aka tafka, ya nuna mace ba zata ji Ƙamshin Al-Jannah ba ma bare kuma shigar ta.

Hajiya Uwa Aishatu Gidado Idris fatan wannan ya ƙara warware turka-turkar da ake ciki yanzu. Allah ya taimaka mana.

Ɗan Uwa Zikirullahi Abdullahi Adam inda wani tsokaci na ƙarin haske, muna cikin ƙishirwarta.

12/05/2023

AURE TUFA CE DA AKE SUTURCE KAI DA ITA!

In an saka ta, ba a cire ta, dole sai an kula domin ba ko ina ake zama ba, gudun kar ta ɓaci, saboda wata ƙazantar in ta taɓa tufa bata fita duka sai ta bar gurbi, wani tabon in ya ɗisa a tufa gurbin shi sai ya dafe, sannan ba kowanne irin sabulu za ayi amfani ba wajen wanke ta ba gudun koɗau, sannan ba a gwamutsa cikin kayan da suke bau gudun kar ta rine tayi dabbare-dabbare, miji ke matsayin tufar sama, mace kuma matsayin tufar ciki. Dole mace ta tsaftace mijin ta, domin sutura ne gare ta dake rufa mata asiri, haka dole miji ya kula wajen tsaftace matar shi domin sutura ce gare shi dake rufe masa tsiraici.

Allah ka tufatar da mu, ka kuma bamu suturta da dindindin.

26/02/2023

An bi maslahar ƙashin kai sama da maslahar al'ummar musulmi da sunan cancanta, wanda tsantsar ƙwarar kai ne

Ƙuri'ar Zaɓe ko Hannun Caffa (Mubaya'a)!Babu maraba da kaɗa ƙuri'ar zaɓe da kuma caffa da ake yi a shekarun baya, kamar ...
14/10/2022

Ƙuri'ar Zaɓe ko Hannun Caffa (Mubaya'a)!

Babu maraba da kaɗa ƙuri'ar zaɓe da kuma caffa da ake yi a shekarun baya, kamar yadda babu bambanci tsakanin naɗin muƙami a da can da kuma naɗin muƙami na siyasa a yanzu.

Wannan ke nan, ya rage gare ka/ki, yin adalci ga kai da kuma kula da tsarin shari'ar Muslunci ta sanya wajen zaɓe mutum nagari da kuma yi mishi addu'a idan yaci ta Allah ya taimaka masa wajen gudanar da mulki da tafiyar di cikin sauki, haka ya zama lalle kayi biyayya gare shi ko ga wanda Allah ya baiwa nasara ta halastacciyyar hanya ce ko ta haramtacciya matuƙar dai madafun iko sun koma hannun shi.

Lalle mu yi zaɓe don Allah domin duk wanda muka zaɓe shi ba don dalilan da Shari'a ta yarda da shi ba, Allah zai watsi damu a lamuran mu da zai janyo mana tagayyara da shiga halin ƙaƙa naka yi ga kuma fushin Ubangiji dake dakon mu gobe Al-Ƙiyama.

Kar muyi zaɓe so kuɗi, ko tsurar soyayya koda wani yafi wanda muke so cancanta, ko zallar ƙiyayya koda kuwa shi ne yafi cancanta a zahiri, ko kuma zaɓe saboda wane ake yayi ko jam'iyya kaza ake yayi, ko kuma saboda wane yana tare da namu gonin ko yana mara masa baya ko kuma saboda gonin mu ya zaɓo mana wane, muyi zaɓe don sai an tambaye mu kan wanda muka zaɓa.

Har ga Allah mun san wa yafi cancanta in mun cire tsurar soyayya ko zallar ƙiyayya mun gujewa don rai da son kai da son zuciya, to shi ya kamata mu zaɓa koda bai da kuɗi ko baya bada kuɗi ko bai tsaya a Jam'iyya mai ƙarfi ba, kar muce asarar ƙuri'a zamu yi, mu zaɓe shi, muyi addu'ar Allah ya bashi nasara.

Sau da dama, da hannayen mu muke janyowa kan mu wahala, lokacin da ni nace ba zan zaɓi wane ba don bai da wasu iyayen gida ko da wuya yaci ko Jam'iyyar shi ba tada ƙarfi, wani yayi haka, duk sai mu dare mu bar shi, mu taimaki waɗanda kowa ya san rashin ingancin su da shaharar su a ta'adi da ɓarna ga dukiyar gwamnati, wanda da ni da kai mun jajurce mun yi abin da ya kamata da ba a tsunci kai a wahala da wuya ba.

Allah ya samu gyara mu gyaru ya kuma gyara mana ƙasar mu.

TSANIN MA'AURATA 0011) Kar kiyi sakaci wata can a waje ta fiki sanin makamar mijin ki.2) Kar kiyi ƙasa a gwiwa wajen dur...
14/10/2022

TSANIN MA'AURATA 001

1) Kar kiyi sakaci wata can a waje ta fiki sanin makamar mijin ki.

2) Kar kiyi ƙasa a gwiwa wajen durƙusawa ko rissinawa miji kan sakar naki ra'ayin ki bi nashi ra'ayin.

3) Kar kiyi tirjiya ko jayayya da miji kan lamarin da ya nema madamar bai ci karo da Shari'a ba.

4) Kar kiyi ƙiwa ko ganda wajen gaggawa zuwa amsawa miji buƙatar shi a kowanne hali k**e.

5) Kar kiyi kasada da ganganci wajen sakar baki da faɗar magana ko tankawa miji lokacin da ya fusata ko yake cikin fushi.

6) Kar kiyi son rai ko nuna son kai ko bayyana don zuciya a zaman ki da mijin ki.

7) Kar kiyi lalaci ko nauyi wajen tsaftace jiki, gida, yara da abinci don kyautatawa mijin ki.

8) Kar kiyi girman kai ko kiji jinkai wajen bada haƙuri ga miji lokacin da ran shi ya ɓaci.

9) Kar kiyi wasa wajen kyautata abin ci ko abin sha na mijin ki.

10) Kar kiyi wawtar neman a sake ki ko aikata wani abu da aka sharɗanta in kin yi shi kin saku.

TUNASARWA 003Da takaici kuma da kunya...Ga hoto na raɗau, rangaɗaɗau dani a hosta, cikin fara'a da kalamin fatan alheri ...
14/10/2022

TUNASARWA 003

Da takaici kuma da kunya...

Ga hoto na raɗau, rangaɗaɗau dani a hosta, cikin fara'a da kalamin fatan alheri ga al'ummar ƙasata...

Sai dai fa, in da zan ci mulki ba zan ji kunyar kwashe kuɗaɗen su ba, da jefa su cikin musifa, anya kuwa da hankali jikina.

Koda yake in ɓera da sata daddawa da wari... Mu kan mu da akwai namu laifin...

Tun daga iyaye, ƴan uwa, yayyi da ƙanne da abokai har malamai na jira suke in naci zaɓe na sato dukiyar al-ummar ƙasa in wadata su su kaɗai, in kuwa ban yi hakan ba, baƙar gaba zamu ƙulla dasu, kuma matsananciyar tsana zasu ɗauka dani...

Duk mu bamu kunya mu da muke mulki suma da ake mulkar basu kunya...

Aƙidar mu ɗaya ce, wato: Ruwan da ya dake ka shi ne ruwa... Saboda da arzuƙi a gidan wasu gwara a namu gidan, a namun ma, a ɗakin mu, a ɗakin ma a hannun mu, a hannun ma mallaki na...

Mun daina kula da ta ina kuɗi yazo mana, kawai za a samu kuɗi to muna cikin wannan harkar fa dumu-dumu, ba ayi ba mu ba, sai iya inda ƙarfin mu ya ƙare...

Yaushe kake jiran tsammanin samun gyara da daidaiton al'amurra? Yau ko Gobe ko Jibi ko Gata ko Chitta ...? Babu rana sam-sam.

Bamu yanke zato ba, ko ɗebe tsammani ba ko kwashe haso sai dai ƙa'idar Shari'ah Allah bai gyarawa mutane sai sun yi nasu yunƙurin da ƙoƙarin, sai ya sauya musu alheri...

Ni dai har yanzu ban tunanin a ɗabi'u irin namu na kasancewar da daman mu ko kusan dukan mu illa ƴan ƙalilan mazambata ne, maha'inta ne, macuta ne, mamugunta ne, maƙetata ne, mahassada ne, maƙaryata ne, mayaudara ne, madamfara ne, zuciyoyin mu a ƙeƙashe suke a bushe suke wajen yin komai don samun duniya ba tare da la'akari da nazarin munin abun ba, wai wani jagora a siyasa zai iya mayar damu kan tsari komai ya daidaita kowa ya saisaita.

Ina ka karanta ka fahimta sai kowa yayi nashi hoɓɓasar wajen yin gyara a karan kan shi da duk wanda yake da iko kan shi.

Allah Maɗaukaki ya taimake mu kan gyarawa da shiryuwa. Amin.

14/10/2022

TUNASARWA 002 daga

Yi taka tsantsan da kaffa-kaffa ka zama mai ɗari-ɗari... Duk gudun kar ka cutar da wani ta... Daka yi ganganci da kasadar cutar wani gwamma kayi sakaci kai a cuce ka...

Wallahi! Tallahi! Billahi! Ba zaka tafi da wani haƙƙi ba zuwa lahira face sai Allah ya ƙwatarwa mai shi kuma kar kayi tunanin da abin da ka ɗauka za a biya shi face ayyukan ka na lada za a kwashe a biya shi, in kuma baka da su ko sun yi ƙaranci su biya sai kwaso laifukan shi a jifga maka a lafta maka su.

Komai yayi farko to yana da ƙarshe...Duk rashin daɗin abu da damuwar da ka shiga kan shi wataran sai labari in aka yi ha...
14/10/2022

Komai yayi farko to yana da ƙarshe...

Duk rashin daɗin abu da damuwar da ka shiga kan shi wataran sai labari in aka yi haƙuri, babu abun da yake dawwama a duniyar nan a hali ɗaya la daɗi wala wuya, shi yasa kullum masu haƙuri ke cin ganiya da moriya na haƙurin da s**a yi, koyi yadda ake haƙurtar da kai domin da hakan ne zaka sabarwa kan ka haƙuri, haƙuri farkon shi ɗaci gauraye da ƙuna, tsakiyar shi bauri sirke da ɗimi, ƙarshen shi zaƙi cakuɗe da daɗi.

Yi haƙuri duk irin cutuwa da ciwo da za kaji, yi haƙuri duk irin sosuwar rai da ƙunar rai da ɓacin rai da ƙunci da damuwa ko baƙin ciki da zulumi da a za ka shiga, mafita ɗaya in ka jure ka daure kayi dangana zai zo ya wuce kamar ba ayi ba...

Akwai lokacin da matsin da zaka ji daga mafi kusanci ne, ko amini da ka aminta ko laminta dashi, a lokacin haƙuri yafi wuya da wahalarwa, amma yau da gobe da mantuwar da Allah ya sanya maka zata mantar da kai wannan abun, illa wasu lokutan in ka tuna ko kaji ɓacin rai, ko abun ya saka raha, ko ya baka dariya, alal aƙalla zaka samu darasi da zai amfane ka a gaba.

Kar ka ƙyamaci haƙuri zaton ka ragonta ce yin shi, ba wanda ke iya haƙuri sai jarumi mai ƙarfin rai da dakakkiyar zuciya da zurfin tunani da hangen nesa da kaifin hankali...

Ya ishi haƙuri fakhari kasancewar shi Siffa ga Mahalicci kuma Siffa ga Annabawan Allah.

Ba hanya mafi tasiri wajen cimma buri irin ta yin aiki da haƙuri a aiwace musamman ka haɗa shi da addu'a, ba abin da in ka tunkara ba zaka same shi ba.

Allah ya musu tanadi maras iyaka kuma yana tare da su kuma yana taimakon su kan dukkan lamuran su matuƙar suna kan ɗabi'ar haƙuri.

Duk wanda yake zuga ka kar kayi haƙuri, lalle ka nesance shi domin asararre ne, taɓaɓɓe ne, ko kuma ace halakakke domin umarni da haƙuri na cikin ɗabi'un rabautattun mutane.

Allah ka sanya mu masu haƙuri a komai namu, ka bamu gwaggwaɓan lada mara iyaka, ka tashe mu cikin tawagar mahaƙurta. Amin.

30/09/2022
14/09/2022

ذكر عيوب الخاطب بين الإباحة والوجوب

عقد الزواج رباط وثيق، ومن ثم فلا بد من المصارحة التامة حتى يكون كلا الطرفين على بينة من أمره إن شاء أمضى وإن شاء أعرض، ومن استشير في أمر مخطوبة، أو خاطب، فعليه أن يذكر كل ما يعرف من صفات حميدة كانت، أو ذميمة، ولا يعد هذا غيبة، ولا يجوز لمن استشير أن يكتم أمرًا رغبة في التوفيق بين الطرفين، فهذه أمانة سوف يسأل عنها بين يدي الله يوم القيامة، وفي الحديث الذي رواه الطبراني وصححه السيوطي قال صلى الله عليه وسلم: «المستشار مؤتمن، فإذا استشير فليشر بما هو صانع لنفسه».

قال البهوتي: وَعَلَى مَنْ اُسْتُشِيرَ فِي خَاطِبٍ أَوْ مَخْطُوبَةٍ أَنْ يَذْكُرَ مَا فِيهِ مِنْ مَسَاوِئَ أَيْ عُيُوبٍ وَغَيْرِهَا وَلا يَكُون غِيبَةً مُحَرَّمَةً إذَا قُصِدَ بِهِ النَّصِيحَةُ. كشاف القناع.

بل إنّ ذلك من واجب النصيحة، فلا يجوز لك السكوت في مثل هذه الحالة.

قال البجيرمي: وَيَجِبُ ذِكْرُ عُيُوبِ مَنْ أُرِيدَ اجْتِمَاعٌ عَلَيْهِ لِمُنَاكَحَةٍ أَوْ نَحْوِهَا كَمُعَامَلَةٍ. حاشية البجيرمي على الخطيب.

والأصل في مثل هذه الأمور أن يقتصر على قدر الحاجة فيكفي نصحه باجتناب خطبتها أو كونها لا تصلح له، لكن إذا لم يكف ذلك ولم ينفع إلا بذكر المساوئ صراحة فلا حرج فيه بل هو الواجب عليك.

قال الدمياطي: وقوله وجوبا محله إذا لم يندفع إلا بذكر العيوب فإن اندفع بدونه بأن اكتفى بقوله له هو لا يصلح أو احتيج لذكر البعض دون البعض حرم ذكر شيء منها في الأول وشيء من البعض الآخر في الثاني. إعانة الطالبين.

جاء في الموسوعة الفقهية الكويتية: من استشير في خاطب أو مخطوبة فعليه أن يذكر ما فيه من مساوئ شرعية أو عرفية ولا يكون غيبة محرمة إذا قصد به النصيحة والتحذير لا الإيذاء، لقوله صلى الله عليه وسلم لفاطمة بنت قيس رضي الله تعالى عنها لما أخبرته أن معاوية وأبا جهم رضي الله عنهما خطباها: أما أبو جهم فلا يضع عصاه عن عاتقه، وأما معاوية فصعلوك لا مال له؛ ولقوله صلى الله عليه وسلم : إذا استنصح أحدكم أخاه فلينصحه، وعنه صلى الله عليه وسلم أنه قال: المستشار مؤتمن وقال: الدين النصيحة، وقد روى الحاكم أن أخا لبلال رضي الله عنه خطب امرأة فقالوا: إن يحضر بلال زوجناك، فحضر فقال: أنا بلال وهذا أخي، وهو امرؤ سيئ الخلق والدين. قال الحاكم : صحيح الإسناد. انتهى.

قال النووي عند شرحه للحديث السابق: أما أبو جهم فلا يضع عصاه عن عاتقه. وفيه دليل على جواز ذكر الإنسان بما فيه عند المشاورة وطلب النصيحة، ولا يكون هذا من الغيبة المحرمة بل من النصيحة الواجبة. وقد قال العلماء إن الغيبة تباح في ستة مواضع أحدها الاستنصاح.

السؤال السادس من الفتوى رقم ‏(‏9895‏)‏‏.‏

س6‏:‏ هل تحذير الناس من رجل ظاهر الفسق ومعروف بفسقه، يعتبر غيبة يسأل عنها الإنسان يوم القيامة‏؟‏

ج6‏:‏ إذا كان الواقع كما ذكر، وكان ذكره بما فيه لتحذير الناس من شره حتى لا يغتر به من لم يعرفه جاز، وإن كان ذلك للتشهي والتسلية ونحوهما لم يجز‏.‏ وبالله التوفيق، وصلى الله على نبينا محمد وآله وصحبه وسلم‏.‏

اللجنة الدائمة للبحوث العلمية والإفتاء

الرئيس‏:‏ عبد العزيز بن عبد الله بن باز

نائب الرئيس‏:‏ عبد الرزاق عفيفي

عضو‏:‏ عبد الله بن غديان

ما يذكر عن الخاطب أو المخطوبة للبيان هل يعتبر غيبة‏؟‏

السؤال الثالث من الفتوى رقم ‏(‏6316‏)‏‏.‏

س3‏:‏ في حالة خطبة المرأة فإنه في معظم الأحيان توصف المرأة للرجل، ولابد من ذكر عيوبها ومحاسنها؛ كالطول والجمال وإلى آخر ذلك، فهل مثل هذه الأوصاف تدخل تحت باب الغيبة‏؟‏ وكذلك غالبا ما يسألون عن الفصل والأصل، ويكثر ذلك عند السؤال عن الرجل والمرأة على السواء، مما يجعل المجيب في وضع حرج، إذ قد يغتاب الشخص من حيث لا يدري‏.‏

ج3‏:‏ لا يعتبر ذكر أوصاف الخاطب والمخطوبة للتعريف بهما والنصح لهما حتى يكون كل منهما على بينة من الآخر قبل عقد الزواج- لا يعتبر ذلك من الغيبة التي حرمها الله ورسوله، بل من النصح المأمور به في حديث‏:‏ صحيح البخاري الحدود ‏(‏6440‏)‏، صحيح مسلم الحدود ‏(‏1698‏)‏، سنن الترمذي الحدود ‏(‏1433‏)‏، سنن النسائي آداب القضاة ‏(‏5411‏)‏، سنن أبو داود الحدود ‏(‏4445‏)‏، سنن ابن ماجه الحدود ‏(‏2549‏)‏، مسند أحمد بن حنبل ‏(‏4/115‏)‏، موطأ مالك الحدود ‏(‏1556‏)‏، سنن الدارمي الحدود ‏(‏2317‏)‏‏.‏ الدين النصيحة‏.‏‏.‏ الخ، ومن التعاون على البر والخير، وقد قال تعالى‏:‏ سورة المائدة الآية 2 ‏{‏وَتَعَاوَنُوا عَلَى الْبِرِّ وَالتَّقْوَى‏}‏‏.‏ وبالله التوفيق، وصلى الله على نبينا محمد وآله وصحبه وسلم‏.‏

اللجنة الدائمة للبحوث العلمية والإفتاء

الرئيس‏:‏ عبد العزيز بن عبد الله بن باز

نائب الرئيس‏:‏ عبد الرزاق عفيفي

عضو‏:‏ عبد الله بن غديان

عضو‏:‏ عبد الله بن قعود

ونختم بقول الشيخ:

الذم ليس بغيبة في ستة *** متظلم ومعرف ومحذر

ولمظهر فسقا ومستفت ومن *** طلب الإعانة في إزالة منكر

Address

Kano
700321

Telephone

08133338700

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Abu Nihlah As-Salafiy posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Practice

Send a message to Abu Nihlah As-Salafiy:

Share

Share on Facebook Share on Twitter Share on LinkedIn
Share on Pinterest Share on Reddit Share via Email
Share on WhatsApp Share on Instagram Share on Telegram