Dr. Dambazau TV

Dr. Dambazau TV My name is Dr. Abdurrahman kamilu Dambazau (MBBS BUK/AKTH). Am a Medical Doctor, content creator, and Health influencer.
(1)

Inba uwa ba, wa zai ma yaro haka???Allah ya saka ma iyayen mu da gidan Aljanna.Waɗan da iyayen su s**a rasu Allah ya gaf...
08/01/2026

Inba uwa ba, wa zai ma yaro haka???

Allah ya saka ma iyayen mu da gidan Aljanna.

Waɗan da iyayen su s**a rasu Allah ya gafarta musu.

Dr Abdurrahman Dambazau

Mun amsa tambayoyi sama da ɗari huɗu (400) a shirin da muka gabatar muku na amsar tambayoyin ku ajiya....Sakamakon yawa ...
06/01/2026

Mun amsa tambayoyi sama da ɗari huɗu (400) a shirin da muka gabatar muku na amsar tambayoyin ku ajiya....

Sakamakon yawa da tambayoyin s**ai yasa wasu basu samu amsa ba, amma insha Allahu zamuyi iya ƙoƙarin mu wajen ƙara sa amsa muku.

Dr Muhammad shine likitan da ya taya Ni amsa muku tambayoyin, muna masa Godiya, Allah ya saka masa da alkairi.

Ga waɗan da basu sanshi ba, tare mukai karatun likitanci(MBBS) dashi a jami'ar Bayero dake kano, sakamakon ilimi da Allah ya bashi sosai akan abun da ya shafi lafiya yasa na tilasta shi buɗe facebook account don ya dunga faɗakar damu.

Ga shafin sa nan Muhammad Isah ku bishi domin tabbas zaku amfana.

Dr Abdurrahman Dambazau@top fans

AMSA TAMBAYOYI...Ni tare da Dr Muhammad Isah insha Allahu za mu amsa muku tambayoyi, wanda zaku rubuto mana a ɓangaren k...
05/01/2026

AMSA TAMBAYOYI...

Ni tare da Dr Muhammad Isah insha Allahu za mu amsa muku tambayoyi, wanda zaku rubuto mana a ɓangaren koment.

Domin samun amsa, Tambayar ta zama ta lafiya kuma me ma'ana.

Sannan kar aman ta ayi sharing wannan rubutun don wasu ma su amfana.

Mu je zuwa...

Dr Abdurrahman Dambazau@top fans

04/01/2026

Kina chushe chushe agabanki da sunan kayan mata, Sannan Kuma kice kinason ki rabu da INFECTION?
‎Lallaikam ALJUNUNU FUNUNU..

TABBAS YA KAMATA MU KULA!!!!Wani lokaci ina ɓangaren bada agajin gaggawa (Emergency) aka shigo da wata yarinya a hannu, ...
04/01/2026

TABBAS YA KAMATA MU KULA!!!!

Wani lokaci ina ɓangaren bada agajin gaggawa (Emergency) aka shigo da wata yarinya a hannu, sanye da uniform na islamiyya jikin ta, wanda bana ji yarinyar ta wuce shekara sha biyar.

Tun kan a sauke yarinyar kan gado jikina ya bani ba lallai yarinyar na da rai ba.

Ina taƙaice muku labari mukai duk wani dube dube da zamuyi, yarinya dai babu rai, ta rasu.
Da mu ka tambayi me ya faru da yarinyar sai ake cema, sun fito sallah ne wajen ƙarfe huɗu a makarantar islamiyyar su, sai yarinyar ta yanke jiki ta faɗi ƙasa, malamin su da yazo sai yace ai Aljanune, agurin ya fara karanta mata addu'o'i, bayan ya ɗau lokaci yana mata, sai yasa aka ajjiye ta awani aji, yace da aljanun sun cika ta zata farfaɗo.
Dab da za atashi Islamiyya malami ya tura aje a taso ta, wanda anan ne aka ga alamun bata numfashi, kuma aka rugo da ita asibiti.
Ko da ace lokacin da ta faɗi ƙasan aka kawo ta asitibin, tabbas tunda kwanan ta ya ƙare sai ta rasu. Amma dai darasin da nake so mu ɗauka shine "Bakomai ne fa aljanu ba".

Allah ya jiƙan musulmai
Pls ayi sharing don wasu ma su amfana.

Dr Abdurrahman Dambazau

03/01/2026

Sai a shekara biyu ana yawo da mara lafiya gun me maganin gargajiya, amma da anga ya doshi lahira sai akawo manashi asibiti, jama'a likita fa baya hana mutuwa.

TABBAS MUNA BINNE ƳAN UWAN MU DA RANSU.....Da anga alamun mutum baya numfashi shikenan sai ace mutum ya mutu, kuma ahanz...
03/01/2026

TABBAS MUNA BINNE ƳAN UWAN MU DA RANSU.....

Da anga alamun mutum baya numfashi shikenan sai ace mutum ya mutu, kuma ahanzar ta sanar da jana'iza tare da binne shi cikin ƙanƙanin lokaci.
Saurin me muke?????????
A musulunce ana so a hanzar ta binne mamaki, amma kuma ba ya na nufin cewa baza akai shi asibiti don a tabbatar cewa ya rasu ba.

Ban da ɗe a aikin likitan ci ba amma dai sau ba adadi ina ganin ana kawo mara lafiya da tunanin cewa ya rasu, wanda sai mun duba sai muga bai rasu ba.

Wasu doguwar suma suke, wasu kuma zuciyar su ce ke tsaya wa wanda tallafi kaɗn suke buƙata don dawowa hayyacin su.

Akwai labari da zan baku anan gaba wanda zai tabbatar muku da cewa muna binne ƴan uwan mu da ransu.

Allah dai ya kyauta mana kuma ya gafar ta ma mamatan mu....

Dr Abdurrahman Dambazau

MATA DAKE SHAN FARAR ƘASAShaye shaye na farar ƙasa ba abune na burgewa ko jindaɗi ba, rashin lafiya ne ko nace alamune n...
01/01/2026

MATA DAKE SHAN FARAR ƘASA

Shaye shaye na farar ƙasa ba abune na burgewa ko jindaɗi ba, rashin lafiya ne ko nace alamune na cewa jikin ki na neman taimako na wasu sinadaran jiki da muke cema micronutrients.

Masana lafiya sun tabbatar da cewa farar ƙasa na ɗauke wasu sinadarai (Lead, Arsenic, Mercury) Wanda kan iya lalata ma mace, mahaifa, ƙwaƙwalwa da kuma ƙoda.
Wani lokacin har jaririn da ke ciki farar ƙasa na iya illatar wa yayin da yakasan ce me ciki na shan ta.

A lokacin da kika ji kina sha'awar shan farar ƙasa kisani bawai jikin ki lallai farar ƙasar yake buƙata ba, micronutrients yake buƙata wanda zaki same su cikin ƙwai, kayan ganyayyaki, nama, kifi da sauran abubuwa masu gina jiki.

Ƴar uwa ta ki guji farar ƙasa, da kinji sha'awan ta ki nemo abincika masu gina jiki kici.

Shin kin taɓa shan farar ƙasa? Ya kika ji bayan kin sha?? Kuzo mu tattauna.

Dr Abdurrahman Dambazau

KUZO MU TAYA TA MURNADr. Maryam Ahmed Almustapha likitace da ta shahara a kafofin mu na sada zumunta, wajen faɗakar wa t...
31/12/2025

KUZO MU TAYA TA MURNA

Dr. Maryam Ahmed Almustapha likitace da ta shahara a kafofin mu na sada zumunta, wajen faɗakar wa tare da ilimar wa, akan abubuwa da s**a shafi lafiyar mu.

Abunda mutane da yawa basu sani ba kan Dr Maryam shine, an haife ta garin bauchi a shekarar 1996, tayi jarabawar ƙarshe ta secondary a Abuja(Capital Science Academy), shekarar da ta gama ta tafi ƙasar Bahrain, inda tayo karatun ta na likitanci(MBBS) Kuma ta kammala wannan karatu da lambar yabo.

Shekaru kaɗan bayan dawowar ta Nigeria, ta fara karatun ƙwarewa a aikin likitanci(Residency training) inda watan da ya gabata ta ci jarabawar ƙarin matsayi (part 1) wanda yanzu haka takai matsayin senior registrar a ɓangaren chutukan ƙoda(kidney) na asibitin tarayya Abuja (FMC Abuja).

Amadadin duka ƴan arewacin Nigeria muna taya ki murna Dr maryam.

Congratulations!! Allah yasa albarka.

Dr Abdurrahman Dambazau@top fans

NAGA TASHIN HANKALI JIYAJiya juma'a, uzuri ya kaini wani gari da ke ƙarƙashin jahar bauchi wanda ya kai ga sai na kwana ...
27/12/2025

NAGA TASHIN HANKALI JIYA

Jiya juma'a, uzuri ya kaini wani gari da ke ƙarƙashin jahar bauchi wanda ya kai ga sai na kwana a garin.
Aka kira mun gidajen kwana na garin(hotels) inda s**a ce basu da ɗaki ko gida wanda babu kowa, sakamakon yanayi na kirsimeti ko ina a cike yake.
Sai hotel guda ɗaya da s**a ce suna da wani ƙaramin ɗaki(short term room).
naje hotel ɗan na karɓi mukulli na shiga ɗakin.
In taƙaice muku labari wannan da kuke gani hoton ƙasan gadon ɗakin ne, ɗauke da kororon roba(condom) da yawa, taba sigari, kwalaye na magungunan karfin maza da sauran su.
Me mutane suke nema a wannan duniya fisabilillahi?
Wannan nadaga cikin dalilin da yasa a asibitocin mu muke samun yawai tar masu ciwon ƙanjamau, ciwon hanta da sauransu.
Ka kwanta da macen da Allah ne kaɗai yasan yawan mazan da s**a kwana da ita..
Kin kwanta da namijin da Allah ne kaɗai yasan yawan adadin matan da ya kwana da su..
Dole kwa ki faɗa ko kafaɗa masifa ta cutuka.
Allah ya kyauta, kuma ya shirya.
Amma dai gwamnati ya kamata ta duba lamarin, bauchi garine na Musulunci, manyan malamai da shehunnai.

Dr Abdurrahman Dambazau. fans

WASU IYAYEN SUKE KASHE JARIRAN SU DA HANNUN SU....Nayi aiki a ɗakin jarirai na wata uku, a matsayin ƙaramin likita, wand...
15/12/2025

WASU IYAYEN SUKE KASHE JARIRAN SU DA HANNUN SU....

Nayi aiki a ɗakin jarirai na wata uku, a matsayin ƙaramin likita, wanda a wannan ɗan lokacin da na zauna naga jarirai biyu da s**a mutu, wanda muna kyautata zato cewa sanadiyyar zane(bille) s**a mutu.
-Jariri na farko yasa mu wata ƙwayar cuta tetanus daga wannan zane(bille).
-Jariri na biyu yasamu ƙwayar cuta acikin jinin sa(sepsis) ta wannan zane da aka masa.
Kuma duka yaran iyayene s**a kai su gun wanzamai aka musu.

Wannan hoto da kuka gani hoton yaron farko ne da yarasu sanadiyyar tetanus daga wannan zane.

Tambaya ta anan shine...

-Dan Allah meye amfanin wannan zanen da ake ma jarirai?

Allah ya kyauta mana.

Dr Abdurrahman Dambazau
Pls ayi sharing dan wasu ma su amfana.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Dr. Dambazau TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Share on Facebook Share on Twitter Share on LinkedIn
Share on Pinterest Share on Reddit Share via Email
Share on WhatsApp Share on Instagram Share on Telegram