Jibwis Wauru Jabbe

Jibwis Wauru Jabbe Wannan shafi namaganane akan Kitabu was Sunna,
aikinsa shine nemo labarai na alkhairi kamar yadda
kowane shafi na JIBWIS keyi. Allah yataimakemu,
Ameen.

AN SAMU 'YAN GYARA DANGANE DA SANARWA DA MUKA FITAR DA SAFE.1- Wa'azin Dare a Ranar Asabar Tsakanin Magrib zuwa Isha ne ...
07/07/2021

AN SAMU 'YAN GYARA DANGANE DA SANARWA DA MUKA FITAR DA SAFE.

1- Wa'azin Dare a Ranar Asabar Tsakanin Magrib zuwa Isha ne kuma a Masallacin Juma'a na Doubeli za'a yi ba a Capital ba Kamar yadda muka sanar.

2- Aikin Hijama da kuma Medical outreach za'a soma sune tun daga karfe 8:00am na safe har zuwa karfe 4:00pm na yamma, inda za'a fara tun daga Ranar Juma'a har zuwa Asabar.

-Medical Outreach a Hannatu Ngilari Clinic Demsawo

-Hijama a Bakari Bole Clinic Shagari Phase 1 ne ba Phase 2 ba Kamar yadda muka sanar a baya.

3- Wa'azin Mata na Jam'iyyatu Nisa'us Sunnah za'a gabatar dashi ne a FOMWAN da Misalin karfe 10am na safe zuwa 12:00pm Insha Allah.

17/11/2017

JUMU'ATUL MUBARAK.

31/10/2017

ALJANNAH A SAUWAKE****
Idan kanason aljanna a saukake to Kada ka taba kwana da fushin wani musulmi aranka.

12/09/2017

Innaa lillahi wa'innaa ilaihi raji'uun. Ajiyane
Allah yayiwa malam Abubakar (hamma habu) rasuwa, wanda gidanshi yake opp. Wauru jabbe jumu@ masji amadadin jibwis w/jabbe muna meka ta'aziyarmu ga iyalensa Allah ya gafarta masa ameen.

DAURIN AURE! DAURIN AURE!! DAURIN AURE!!!Iyalan Marigayi Malam Dahiru  Ahmadda naMarigayi Mallam Abdullahisuna farin cik...
26/04/2017

DAURIN AURE! DAURIN AURE!! DAURIN AURE!!!

Iyalan
Marigayi Malam Dahiru Ahmad
da na
Marigayi Mallam Abdullahi
suna farin cikin Gayyatan Yen uwa da Abokan Arziki
zuwa wurin Daurin Auren 'ya 'yansu
MALLAM YA'U D. AHMAD (El-Hajj)
da Amaryar sa
MALAMA HASSANA ABDULLAHI
wanda za'ayi kamar haka
Rana: 28 April, 2017
Lokaci: 07:30am prompt
Wuri: Walawol kusa da Massallacin Mallam Idris, wauru Jabbe, Yola South LGA, Adamawa State.

Allah ya bada ikon Halarta Ameeeeeen

Sanarwa: Jibwis Social Media Adamawa State

10/03/2017

ALHAMDULILLAH, ALLAH YAKARBI ADDU'AN BAYINSA, BAYAN MASU BAKIN CIKI SUNYI MASU ADAWA DA RAYUWAR SUMA SUNYI, AMMA ALLAH BARUWANSA HM ALLAH KENAN, ALLAH KAKARAWA SHUGABAN KASARMU LAFIYA DA NISAN KWANA, ALLAH KAI KAKEYI MANA KOMAI BAMU DA WAYO SAI ABUN DA KAYANKE MANA.

05/03/2017

Assalamu alaikum, Innaa Lillahi Wa'innaa ilaihiraaji'uun. Allah yayiwa Malam Iliya Rasuwa jiya, Limamin Massallacin Nafan Wauru-Jabbe, Anyi masa Sutura kamar yadda musulunci yatanada. Wannan malamine dake da Dalibai masu yawa, na Al'qur'ani Da Littattafai daga cikinsu akwai Ya'u D. Ahmad, Abdurra'uf, Musa Sulaimaan, Auwal Bajoga dadai sauransu Muna fatan Allah ya jikansa ya gafarta masa. Ameen

DAURIN AURE  DAURIN AUREIYALAN ALHAJI SAHABI UMAR DANA MALAM MAGAJI UMAR suna farin cikin gayyatan yen uwa izuwa daurin ...
03/01/2016

DAURIN AURE DAURIN AURE

IYALAN ALHAJI SAHABI UMAR DANA MALAM MAGAJI UMAR suna farin cikin gayyatan yen uwa izuwa daurin auren ya' yen su
ABUBAKAR SAHABI (SABO DAN AGAJI) tare da ZULAIHAT MAGAJI

RIDWAN MAGAJI tare da FATIMA SAHABI

RANA: 08/01/2016
LOKACI: 06:30 am
VENUE: GIDAN MALAM HARUNA dake daura da makarantan IMAM MALIK ISLAMIC FOUNDATION CENTER dake jimeta
LIYAFA: zaigudana ne bayan kammala daurin auren in-shaa Allah

Allah ya bada ikon halarta, tare da zuriya dai'yiba Ameeen thumma Ameeen

jibwis social media Adamawa state
Khalifa Bello Dahiru
©2016

04/12/2015

SAKON TA'AZIYYA

Sheikh Ali Mamman Shu'aibu, Shugaban Majalisar Mallami na Kungiyar Izala rashen Yola ta Arewa, a madadin Kungiyar Izala reshen Yola ta Arewa na Mika sakon 'aziyya ga ilahirin 'yan Uwa Ahlusunnah na jihar Adamawa baki daya a bisa babban rashi da kungiyar tayi na shugaban Majalisan Mallamai na Yola ta kudu Mallam Halilu Isa.

Mallamin ya rasu ne a yammacin laraba da ta gabata a Babban Asibitin koyarwa dake Gombe.

Muna Addu'a Allah Ya gafarta Mishi Yasa mutuwa hutu ce a gare mu baki daya.

23/04/2015

LABARIN ABUN NASRI
***********************
Abun Nasri wani babban 'dan kasuwa ne. yana
da wani yaronsa wanda yake kula masa da
harkokin kasuwancinsa agarin basra.
Shi wannan yaron nasa yana da wata mata
kyakyawa. tunda Abun Nasri ya ganta, yake so
yayi zina da ita. Don haka ya aiki mijinta wani
gari mai nisa, kuma ya sanyashi wani aiki mai
wahala wanda sai yayi kwanaki bai gama ba.
Da dare yayi sai Abun Nasri ya shigo wajen
wannan Matar yaron nasa. Ya nuna mata
bukatarsa.. har ma ya gaya mata wani adadin
kudi mai yawa wanda zai bata udan ta amince
masa. Sannan ya umurceta cewa ta kulle
dukkanin kofofi da tagogin gidan.
Bayan ta gama kukkullewa sai ya tambayeta
"Shin kin kulle Kofofin gaba daya? Sai tace masa
"EH NA KULLE SU GABA DAYA. SAI DAI AKWAI
WATA KOFA GUDA 'DAYA ITA CE TA GAGARENI
KULLEWA".
Sai yayi mamaki. yace mata "Wacce Kofa kenan?
Nunw min ita in kulle da kaina".
Sai tace masa "KOFAR NAN WACCE ALLAH
UBANGIJIN TALIKAI YAKE GANINMU TA
WAJENTA... Idan kaga zaka iya kullewa ka
hanashi ya ganmu, to shikenan"..
Daga jin wannan kalamai sai Abun Nasri ya
fashe da kuka! yana ta kuka yana tuba zuwa ga
Ubangiji har ranar mutuwarsa bai dena
nadamar wannan abun ba.
Da wannan nake jan hankalin Samari da 'yan
mata da matan aure wadanda shaitan ya rudesu
s**a afka cikin tsrkon nan na ZINA, cewa kuji
tsoron Allah domin yana tare daku aduk inda
kuke aikata Masha'a. Yana kallonku yana jinku.
kuma akwai ranar da zai tattaroku ku tona ma
kanku asiri agaban dukkan halittunsa..

29/06/2014

BUDE TAFSIRI!

Kungiyar Jama'atul Izalatul Bidi'ah
WaIkamtissunnah JIHAR ADAMAWA na
sanar da daukakin al-umman musulmai
cewa Babban Mallamin da kungiyar izala ta
kasa ta turo Adamawa SHEIKH DR LAWAN
ABUBAKAR SHU'AIB KANO DA ALARAMMA
USMAN BIRNIN KEBBI. Yau za a bude
tafsirinsu kamar haka:

Wurin wa'azi: Masallacin jumma'a na
Demsawo.

Lokaci:9:00pm

Manyan shuwagabannin kungiya ana sa
ran halartan su.

SOCIAL MEDIA TA SHIRYA TSAF DON KAWO
MUKU LIVE UPDATE NA WANNAN KARATU
INSHA ALLAH.

Allah ya bada ikon Halarta ameen

28/06/2014

SAKON RAMADAN DAGA: ASH-SHEIKH IMAM
ABDULLAHI BALA LAU (Shugaban Kungiyar
na Kasa).
Da sunan Allah mai Rahama mai Jinqai. Dukkan
godiya ta tabbata ga Allah madaukakin sarki, muna
gode masa, kuma muna neman taimakon Sa, da
gafarar sa. Muna neman tsarin sa daga dukkan
sharri.
Ina so inyi amfani da wannan lokaci mai albarka
domin in gabatar da gaisuwa, tunatarwa da addu'a
ga dukkan mutanen wannan kasa mai albarka
(musamman musulmai), kuma a wannan wata na
Ramadan mai tarin albarka da falala.
Allah madaukakin sarki yana cewa: "Watan Ramadan
wanda a cikinsa aka saukar da Al-Qur'ani, shiriya ga
mutane, kuma bayyanannar shaida ta shiriya
da...." [Qur'an:185].
Wannan wata na Ramadan wata ne mai daraja, falala
da muhimmanchi a Musulunchi. Shine watan Al-
Qur'ani, watan azumi, watan albarka, alfarma,
gafara, falala da fa'idodi masu yawan gaske. A
takaice, shine watan da yafi ko wane wata
muhimmanchi da fa'idodi cikin watanni goma sha
biyu na shekara.
A cikin wannan wata ne Allah ya saukar da Al-
Qur'ani, kuma a cikinsa ne daren "Lailatul Qadri"
yake fadowa, wanda ya fi watanni dubu falala.
Kuma watan Ramadan wata ne da musulmai ke zage
damtse wurin tausayi, kyautatawa, kame kai daga
barin alfahsha, haquri, sadaqa da 'yan uwantaka.
Cikin wannan wata ne ake samun dukkan alkhairi.
Wannan wata babban bako ne da duk musulmi na
kwarai ke kosawa da marhaba da zuwansa. A wurin
bayin Allah na gari kuwa, watannan dama ne na
'kara kusantar Allah. Kuma ga masu son shiriya,
wannan wata dama ne na barin alfahsha, al-kaba'ir,
da munanan ayyuka domin komawa ga Allah. Don a
wannan watan duka shai'danu an 'daure su kuma an
kulle su.
Saboda haka, ina so in tunatar da shugabanni da
wadanda ake shugabanta na wannan kasa da suyi
amfani da wannan wata mai albarka don kara
tausayi, gaskiya, amana, adalchi da tuhuman
kawunanmu kan ayyukanmu.
Sannan kuma har yanzu ina amfani da wannan dama
domin jawo hankalinmu da mu guji ta'addanchi,
ha'inchi, chin zali, rashin 'da'a, chin amana, fasadi,
alfahsha, fadace-fadace, tada hamkula, izgili, qazafi,
sharri da chin hanchi da rashawa!
Ina mai horon dukkan musulmi ba tare da la'akari da
matsayi, kudi, kabila, gari, ko jinsi ba, da mu dauki
wannan watan na Ramadan a matsayin bako da ke
zuwa sau daya a shekara. Wata ne na 'yanchi, gafara,
rahama, tuba da zage damtse wurin bautan Allah.
Ina kira a garemu da mu tuba, tuba na gaskiya ga
Allah, kuma mu inganta dangantakarmu da Allah ta
hanyar yin azumi, sallolin nafila, karatun Qur'ani,
sadaka, kyauta, 'da'a, da yawaita addu'o'i. Saboda an
bamu wannan wata ne domin mu inganta imaninmu
da kara tsoron Allah. Allah yana cewa a cikin Suratul
Bakara, aya ta 183:"Ya ku wadan da kuka yi imani,
an wajabta (sanya) muku azumi kamar yadda aka
wajabta wa wadanda s**a gabaceku domin ko zaku
samu tausayi da tsoron Allah."
daga 'karshe, a cikin wannan wata mai albarka,
kasarmu Nigeria tana bukatar addu'o'inmu managrta
daga dukkan bakunanmu. Domin Allah ya zaunar
damu lafiya, kuma ya karemu daga dukkan sharrin
masu sharri!
Ina addu'a Allah ya zaunar damu lafiya, ya yafe mana
zunubanmu, ya kyautata zamantakewarmu, kuma ya
karemu daga fitintinun da kasarmu ke ciki wadanda
s**a hada da rashin tsaro, rashin adalchi, rashin
amana, kashe rayukan da basu ji ba basu gani ba,
chin hanchi da rashawa da sauransu!
Allah ya taimake mu, ya kare mu, ya sada mu da
dukkan alkhairan wannan wata mai albarka, ya bamu
lafiya da zama lafiya.
Ameen Summa Ameen!!!
Ash-Sheikh Imam Abdullahi Bala Lau
(Shugaban Kungiyar Jama'atu Izalatil Bidi'ah Wa
Iqamatis Sunnah Nigeria).
jibwisnigerian@yahoo.com

12/06/2014

Speak the truth – Al Qur’an 3:17
Speak straight – Al Qur’an 33:70
Speak justice – Al Qur’an 6:152
Speak kindly – Al Qur’an 2:83
Speak politely – Al Qur’an 17:53
Speak fairly – Al Qur’an 17:28
Speak gently – Al Qur’an 20:44
Speak graciously – Al Qur’an 17:23
Speak not in vain – Al Qur’an 23:3
Speak no lie – Al Qur’an 22:30

11/06/2014

18 ANSWERS OF THE HOLY PROPHET - MUST READ AND FORWARD*


A traveler once came to the masjid to see the Prophet Muhammad (S.A.W) after greeting the prophet, he was asked where he was from. The traveler replied that he came from very far just to get a few questions answered.
Following is the dialogue between the traveler and the Prophet.

Traveler : I do not want adhaab (punishments) to be written in my account.
*Prophet : Behave well with your parents *

Traveler : I want to be known amongst people as an inteligent person.
*Prophet : Fear Allah (Jalla Jalalu), always. *

Traveler : I want to be counted amongst Allah's favourites.
*Prophet : Recite Quran every morning and evening. *

Traveler: I want my heart to always be enlightened. ( Munawer )
*Prophet : Never forget death. *

Traveler: I never want to be away from Allah's blessing.
*Prophet : Always treat fellow creatures well. *

Traveler: I never want to be harmed by my enemies.
*Prophet : Always have faith in only Allah. *

Traveler: I never want to be humiliated.
*Prophet : Be careful of your actions. *

Traveler: I wish to live long.
*Prophet : Always do sile rahm. (Goodness towards blood Relations) *

Traveler: I want my sustenance to increase.
*Prophet : Always be in wudhoo. *

Traveler: I wish to stay free of adhaab in the grave.
*Prophet : Always wear pure (paak) clothes. *

Traveler: I never want to be burned in hell.
*Prophet : Control your eyes and tongue. *

Traveler: How do I get my sins forgiven?
*Prophet : Always ask forgiveness from Allah with a lot of humility.

Traveler: I want people to respect me always.
*Prophet : Never extend your hands of need at people. *

Traveler: I want to always be honoured.
*Prophet : Never humiliate or put down anyone. *

Traveler: I don't want to be squeezed by fishare qabr.(Squeezing in the grave)
*Prophet : Recite Surat Al Mulk (The Dominion) often. *

Traveler: I want my wealth to increase.
*Prophet : Recite surat el Waqiah (The Inevitable) every night. *

Traveler: I want to be safe and at peace on Day of Judgment.
*Prophet : Do zikr (Praises) of Allah from dusk to night. *

Traveler: I want to be in full attention & concentration during prayers.
*Prophet : Always do wudhoo with concentration and attention. *

*Kindly do forward to all Mu-mineens.

01/06/2014

ALLAH YABADA LADA

Ayaune Adamawa State Org. Sec. Alh. Adamu Misa Kojoli, tareda mataimakinsa Hassan Yusha'u Miga, s**a kawo mana ziyara Division na Yola West dan kara karfafa guiwar 'Yan agaji waje gudanar da aiyuka dafatan Alkhairi gawannan Div. Mai Albarka, muna fatan Allah ya saka musu da Alkhairi.

Address

Yola
Yola
YOLANIGERIA

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jibwis Wauru Jabbe posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share