Nisa'is Sunnah Khairiyya

Nisa'is Sunnah Khairiyya Jam'yyatun Nisa'is Sunnah Alkhairiyya Kungiya CE ta Mata dake garin Jimeta, Yola fadan jihar Adamawa

Kungiyar Nisau Sunnah Na Neman Taimako Saboda Gina Makarantar IslamiyaA shekarar da ta gabata Kungiyar Nisau Sunnah a ji...
29/06/2020

Kungiyar Nisau Sunnah Na Neman Taimako Saboda Gina Makarantar Islamiya

A shekarar da ta gabata Kungiyar Nisau Sunnah a jihar Adamawa ta sanar da samun filaye har guda bakwai a wurare mabanbanta a jihar Adamawa inda kungiyar ta sanar zata gina makarantun Islamiya don karfafa ilimi a kauyukan da filayen suke.

Zuwa yanzu, kungiyar ta samu nasar fara gini a daya daga cikin filayen kamar yanda kuke gani a hoto, a unguwar Badirisa dake karamar hukumar Girei a jihar Adamawa.

Ameera H. Dan Umma ta bayyana cewa kungiyar su na neman tallafi daga hannun al'umma na kudi ko kayan aiki don samun karasa wannan gagarumin aiki, wanda duk wanda ya taimaka zai zama sadakatul jariya.

Ana iya aikawa da taimako ta asusun kungiyar ko kuma a tuntubi daya daga cikin wadannan malaman

1. Malam Malami Garba
08060509073

2. Malam Mamman Nasir
+234 803 812 6777

3. Ameera Habiba Dan Umma
0803 770 1504

Banki: Zenith Bank

Sunan Asusu: Jibwis Woemen Da’awa Committee

Lambar Asusu: 1013563272

Allah ya albarkaci abunda zaku bayar.

GIDAUNIYAR NEMAN TAIMAKON GINA MASALLACIKungiyar Addinin Musulunci mai suna Nisa'us Sunnah Foundation tana sanar da kadd...
25/12/2019

GIDAUNIYAR NEMAN TAIMAKON GINA MASALLACI

Kungiyar Addinin Musulunci mai suna Nisa'us Sunnah Foundation tana sanar da kaddamar da neman taimako na musamman don ƙarasa ginin masallaci a kauyen Tashan Turmi, karamar hukumar Girei, jihar Adamawa.

Kaman yanda kuke gani a hoto, kungiyar Nisa'u, tare da taimakon al'umman musulmai zata ƙarasa ginin masallacin tare da samar da Haraba yalwatacce. Ko a baya kungiyar ta tona rijiya a kauyen na tashar Turmi, inda yanzu kuma take so ta samar da ingantaccen wurin ibada.

A saboda haka kungiyar Nisa'u Sunnah Foundation na neman taimako daga al'umman musulmai saboda yin wannan gagarumin aiki na SADAƘATUL JARIYA.

Za'a iya taimakawa ta asusun banki na ƙungiyar kamar haka:

ZENITH BANK
NAME: Jibwis Women Da'awa Committee
Account Number: 1013563272

TRUSTEES
1. Sheikh Ali Mamman Shu'aibu
0803 616 5429

2. Alh Ahmad Muhammad
08039184558

3. Ameera Nisa'u Sunnah
0803 770 1504

NISA'U SUNNAH FOUNDATION
NO32 BANGSHIKA STREET DAUBELI, JIMETA YOLA.

MARAYU: Kungiyar Nisau Ta Raba Kayan Abinci Da Na Sakawa Ga Marayu Don Bikin Sallah*An Yi Waliman Sallah Wa MarayunDaga ...
05/06/2019

MARAYU: Kungiyar Nisau Ta Raba Kayan Abinci Da Na Sakawa Ga Marayu Don Bikin Sallah

*An Yi Waliman Sallah Wa Marayun

Daga Mahmud Isa Yola

Shahararriyar kungiyar Mata Musulmai ta Nisa'u Sunnah Foundation ta gabatar da shirin tallafawa marayu na musamman a karshen azumi da kuma bayan sallah. Kungiyar ta raba buhunan shinkafa, atamfofi, yadi da kayan yara ga marayu sama da 500 kafin sallah.

Kazalika kungiyar ta gabatar da walima na musamman ga marayun a yau laraba don cin abinci da murnan bikin sallah.

Kungiyar ta samu tallafi ne daga wasu bayin Allah ta hannun shugaban kungiyar Izala na kasa Ash-Sheikh Dr. Abdullahi Bala Lau. An gabatar da tallafin ga marayun a garin Jimeta-Yola, fadan jihar Adamawa.

A ranar 29 ga watan Ramadaan, kungiyar ta gabatar da rabe-raben kayan sallah da buhunan abinci ga marayu a ofishin ta dake Daubeli, jihar Adamawa.

A yau laraba kuma kungiyar ta gayyaci marayun zuwa waliman sallah, inda aka dafa abinnci na musamman saboda su. An gabatar da waliman ne a gidan shugaban Sheikh Bala Lau inda mai dakin shehin malamin ta kaddamar da walimar tare da Ameera na Nisa'u Sunnah.

Ko a cikin azumi ma, kungiyar ta Nisa'u ta bi kauyuka ta raba kayan sakawa da abinci ga marayun a wurare mabanbanta.

Ramadaan: Nisa'us Sunnah Visits Tashan Turmi, Commisioned New WellBy Mahmud Isa YolaAs part of its Ramadaan tour, Nisa'u...
02/06/2019

Ramadaan: Nisa'us Sunnah Visits Tashan Turmi, Commisioned New Well

By Mahmud Isa Yola

As part of its Ramadaan tour, Nisa'u Sunnah Foundation, a women organization for propagating Islam, visited Tashan Turmi Village in Girei Local Government Area of Adamawa State.

The organization is touring some villages in Adamawa state to interact with people who are less privileged and to distribute relief materials to them.

At Tashan Turmi, the organization with the aid of one of its members (name withheld) had drilled a new well after it was learned that they lacked source of water in the whole village.

Speaking shortly after the commissioning, Hajiya Habiba Dan Umma said they learned that the whole village lacked access to clean water on their first visit. She said they immediately took it upon the organization to ensure that a source of water was provided for the village.

"I am using this opportunity to appeal to Muslims everywhere to engage themselves in charitable activities towards the needy, as the end of ramadaan looms large, let us extend our helping hand to the poor. Let us join hands, this is a joint activity and we welcome collaborations from anyone who's interested. We accept donations through our bank accounts and we deliver it to the needy as you can see." She said.

Speaking at the event, mai anguwa Abubakar thanked the organization for establishing a source of water for the village. He said apart from this project, the Nisa'u Foundation is currently taking care of and elderly person who is suffering from chronic high blood pressure. "They took him to the hospital and now that he was discharged, they bring nurses to chake him from time to time. So we are thankful to them." He said.

Abubakar also appealed to the organization to assist them in completing their mosque (photos attached) which is under construction and could not be completed due to insufficiency of funds.

J AM'IYYATUN NISA'IS SUNNAH ALKHAIRIYYA, kungiyar mata musulmai masu da'awa da ke jihar Adamawa ta kaddamar da ginin mak...
08/01/2019

J AM'IYYATUN NISA'IS SUNNAH ALKHAIRIYYA, kungiyar mata musulmai masu da'awa da ke jihar Adamawa ta kaddamar da ginin makarantar Islamiya a anguwan Badirisa Lainde By-Pass dake karamar hukumar Girei Jihar Adamawa. Idan baku manta ba dai kungiyar ta gabatar da taro a baya inda ta kaddamar da gidauniyar asusun gina makarantun islamiya a filaye guda 8 wanda aka mallakawa kungiyar a wurare daban daban. [ 146 more words ]
https://nisausunnah.wordpress.com/2019/01/08/kungiyar-nisau-ta-kaddamar-da-ginin-islamiya/

J AM’IYYATUN NISA’IS SUNNAH ALKHAIRIYYA, kungiyar mata musulmai masu da’awa da ke jihar Adamawa ta kaddamar da ginin makarantar Islamiya a anguwan Badirisa Lainde By-Pass dake kar…

NEMAN TAIMAKON DON GINA MAKARANTUN ISLAMIYA Assalamu Alaikum JAM'IYYATUN NISA'IS SUNNAH ALKHAIRIYYA, kungiyar mata musul...
11/11/2018

NEMAN TAIMAKON DON GINA MAKARANTUN ISLAMIYA Assalamu Alaikum JAM'IYYATUN NISA'IS SUNNAH ALKHAIRIYYA, kungiyar mata musulmai masu da'awa da ke jihar Adamawa na neman taimako na kudi ko kayan aiki daga mutane da kungiyoyi/ma'aikatu don gina ajujuwan karatun islamiya a filaye guda takawas mallakar kungiyar a jihar Adamawa. Kungiyar JINSA ta samu filayen ne daga mutane da kungiyoyi don gina ajujuwan karatu. [ 166 more words ]
https://nisausunnah.wordpress.com/2018/11/11/neman-taimakon-don-gina-makarantun-islamiya/

NEMAN TAIMAKON DON GINA MAKARANTUN ISLAMIYA Assalamu Alaikum JAM’IYYATUN NISA’IS SUNNAH ALKHAIRIYYA, kungiyar mata musulmai masu da’awa da ke jihar Adamawa na neman taimako na kud…

- BUILDING OF ISLAMIYYA PRIMARY SCHOOLS Assalamu Alaikum Wa Rahmatullah Wa Barakaatuh JAM'IYYATU NISA'IS SUNNAH ALKHAIRI...
11/11/2018

- BUILDING OF ISLAMIYYA PRIMARY SCHOOLS Assalamu Alaikum Wa Rahmatullah Wa Barakaatuh JAM'IYYATU NISA'IS SUNNAH ALKHAIRIYYA, a women da'awa organization based in Adamawa state is here by soliciting for donation/Contribution in cash or Kind from all and sundry in order to build classes at the organization's various plots in Adamawa state. The plots were allocated to JINSA by different individuals and organization for the purpose of building classes that will serve as primary islamic education centers in eight different places viz: [ 183 more words ]
https://nisausunnah.wordpress.com/2018/11/11/request-for-donation/

– BUILDING OF ISLAMIYYA PRIMARY SCHOOLS Assalamu Alaikum Wa Rahmatullah Wa Barakaatuh JAM’IYYATU NISA’IS SUNNAH ALKHAIRIYYA, a women da’awa organization based in Adamawa sta…

TATTAUNAWA DA DARAKTAN AGAJI Hajiya Hauwa Hamisu Hamma Joda ita ce daraktan Agaji na kungiyar JINSA. A tattaunawar ta da...
06/11/2018

TATTAUNAWA DA DARAKTAN AGAJI Hajiya Hauwa Hamisu Hamma Joda ita ce daraktan Agaji na kungiyar JINSA. A tattaunawar ta da wakilin Ummahaat ta bayyana ayyukan da su mata suke yi a bangaren Agaji. Wakilinmu: Assalamu Alaikum, ko menene dalilin kafa bangaren Agaji na mata a karkashin kungiyar ku Haj. Hauwa: Wa’alaikumussalam. Hakika mun bude bangaren Agaji ne saboda mun lura mata ma ba’a bar su a bay aba wajen baiwa addini gudunmawa. [ 239 more words ]
https://nisausunnah.wordpress.com/2018/11/06/yan-agaji-mata-na-nisau/

TATTAUNAWA DA DARAKTAN AGAJI Hajiya Hauwa Hamisu Hamma Joda ita ce daraktan Agaji na kungiyar JINSA. A tattaunawar ta da wakilin Ummahaat ta bayyana ayyukan da su mata suke yi a bangaren Agaji. &nb…

01/11/2018

nisau100363559.wordpress.com/2018/07/03/taimako/

Hotuna: Yayinda kungiya ta sake kawo Haruna Isma'il Haruna Asibiti don duba lafiyar sa. Likita ya bayyana cewa yana samu...
03/07/2018

Hotuna: Yayinda kungiya ta sake kawo Haruna Isma'il Haruna Asibiti don duba lafiyar sa. Likita ya bayyana cewa yana samun sauki, kamar yanda kuke gani yana iya takawa kadan-kadan. Muna fata Allah SWT ya bashi lafiya.

*Alhamdulillah*A yau Kungiyar Nisa'us Sunnah ta mayar da Haruna Isma'il gidan sa bayan an sallame shi daga Asibiti.Idan ...
22/06/2018

*Alhamdulillah*

A yau Kungiyar Nisa'us Sunnah ta mayar da Haruna Isma'il gidan sa bayan an sallame shi daga Asibiti.

Idan baku manta ba, kungiya ta ci karo da Haruna ne a lokacin da ta fita da'awa kusa da kauyen da yake. Kungiya ta nema masa taimako inda kai tsaye aka kai shi asibiti ya kwana biyu. Likitoci sun duba shi sun bashi magunguna kuma lokaci lokaci zai na zuwa ana duba shi Insha Allah.

Kungiya tana mika godiya ga wadanda s**a taimaka da dukiyar su, da wadanda s**ayi addu'o'i. Allah ya mana tarayya a ladan duka.

Kunyiyar Nisa'u Sunnah Ta Rufe Karatun Ramadaan A Kauyukan Tapare Da Dagri*Ta Raba Tallafin MarayuKungiyar mata masu hid...
12/06/2018

Kunyiyar Nisa'u Sunnah Ta Rufe Karatun Ramadaan A Kauyukan Tapare Da Dagri

*Ta Raba Tallafin Marayu

Kungiyar mata masu hidiman addinin musulunci Jam'iyyatun Nisa'is Sunnah Alkhairiyya ta rufe karatu da ta tura wakilanta suna yi a kauyukan Dagri da Tapare na watan Ramadaan.

Kazalika kungiyar ta raba kayan tallafi ga marayu a kauyen Dagri.

Wanna ya biyo bayan kaddamar da rabon kayan marayun wanda kungiyar tayi a garin Jimeta makonni biyu da s**a gabata.

Wannan na daga cikin himman da kungiyar take bayarwa wajen ganin iyaye mata a jihar Adamawa sun ilmantu da addini.

Masha Allah
23/04/2018

Masha Allah

Address

No 33 Bangshika Street, Doubeli
Jimeta

Telephone

8106792663

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Nisa'is Sunnah Khairiyya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share