Suleiman Nura Sa'idu

Suleiman Nura Sa'idu دَعَوَاهُمْ فِيهَا سُبْحَـٰنَكَ ٱللَّهُمَّ وَتَحِيَّتُهُمْ فِيهَاسَلاَمٌ.
(2)

Arramma عبدالرحيم منصور يلوة Addu'a Zamu Maka Da Kuma Fatan Allah Ya Karba Addu'ar Da Zamuyi MakaArramma Allah Ya Maka A...
08/08/2025

Arramma عبدالرحيم منصور يلوة Addu'a Zamu Maka Da Kuma Fatan Allah Ya Karba Addu'ar Da Zamuyi Maka

Arramma Allah Ya Maka Albarka Allah Ya Qara Wa Rayuwar Ka Albarka Allah Yasa A Rabu Da Iyaye Lafiya Amin Ya Rabbil Alamin

Wannan Hidima Da Kake Wa Addinin Musulunci Allah Ya Qara Maka Jajurcewa Akai Amin In Sha Allah Kaine Magajin Malamin Professor Mansur Isa Yelwa

ادعُ بالخير لغيرك، يُدعى لك كذلك. ♥️🙏
Dalibin Prof Mansur Isah Yelwa ✍️

Idan ka san ba aurenta za kayi ba, don Allah ka daina yaudararta. Su kan shiga mawuyacin hali idan s**a ji labarin za ku...
08/08/2025

Idan ka san ba aurenta za kayi ba, don Allah ka daina yaudararta. Su kan shiga mawuyacin hali idan s**a ji labarin za kuyi aure bayan kunyi musu alkawarin zaku aure su. Ba zaka so ayi wa ‘yarka ko ‘yar uwarka ba.

Allah Ya shirye mu

✍️
Dr. Jabir Sani Maihula

SALLAR NAFILA LOKACIN  DA LIMAN YA HAU MINBARI RANAR JUMU'AH1) Idan mutum ya shiga masallaci ranar Jumu'ah liman yana ak...
08/08/2025

SALLAR NAFILA LOKACIN DA LIMAN YA HAU MINBARI RANAR JUMU'AH

1) Idan mutum ya shiga masallaci ranar Jumu'ah liman yana akan minbari, zaiyi sallah raka'ah biyu, amma ya gajarta. (Bukhari da Muslim)

2) Idan mutum ya taradda ana kiran sallah kafin a fara khutbah, zaiyi sallah lokacin da ake kira bazai jira a gama kiran sallah ba, saboda sauraron khutbah wajibi ne amma sauraron maikiran sallah Sunna ne. ( Ibn Uthaimeen)

3) Idan mutum bai samu shiga masallaci ba ya tsaya a harabar masallaci, bazaiyi sallah ba lokacin da liman ke khutbah, saboda sallar ta Tahiyyatul masjid ce, bata wajaba sai ga wanda ya shiga masallaci.

4) Mutane da yawa s**anyi kuskure sai su zata akwai wasu raka'ah biyu da akeyi kafin Jumu'ah, sai kaga mutum yazo yana wajen masallaci ya kabbarta sallah alhali liman yana khutbah. Wannan kuskure ne, matsayin sa kamar wanda ya tashi a cikin masallaci ya kabbarta sallah alhalin liman yana khutbah.

5) Duk wanda ya shiga masallaci wajibi ne (a kan zance mafi inganci) yayi sallah raka'ah biyu kafin ya zauna. Wannan hukuncin da ranar Jumu'ah da Assabar da sau ran ranaku duka daya ne. Dalili akan hakan shine, cewar da Manzon Allah S.A.W. yayi: Idan dayanku ya shiga masallaci kada ya zauna sai yayi sallah raka'a biyu. (Bukhari da Muslim)

Ya kamata ayi fadakarwa da mutane akan wannan hukuncin, saboda da yawa akan saba.

Allah yasa mudace da sunnah.

✍🏽 Dr. Jabir Sani Maihula HAFIZAHULLAH

ASSALAM ALAIKUM MUTANAN SOKOTO,MUTANAN SHEHU, ZA A YI WA'AZI DA HAUSA.RANAR LITININ 11/8/2025BAYAN MAGARIBA, A MASALLACI...
08/08/2025

ASSALAM ALAIKUM MUTANAN SOKOTO,
MUTANAN SHEHU, ZA A YI WA'AZI DA HAUSA.
RANAR LITININ 11/8/2025
BAYAN MAGARIBA,
A MASALLACIN JUMMA'A NA PROF, AA GWANDU.
IN SHA ALLAH.

Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa (hafizahullah)

I've just reached 30K followers! Thank you for continuing support. I could never have made it without each one of you. 🙏...
08/08/2025

I've just reached 30K followers! Thank you for continuing support. I could never have made it without each one of you. 🙏🤗🎉

07/08/2025

IDAN AKACE ALLAH YACE KO ANNABI YACE MIQA WUYA AKE - KO YA YI DAIDAI DA HANKALINKA KO BAIYI DAIDAI DA HANKALINKA BA

07/08/2025

Ku taskance matanku, domin mata bata da abokin miji.

Two ladies from Moscow converted to Islam May Allah keep them steadfast on Islam.🤲
07/08/2025

Two ladies from Moscow converted to Islam

May Allah keep them steadfast on Islam.🤲

Wato ita rayuwa kullum ka yi ƙoƙari ka bi Allah da ManzonSa sannan ka yi riƙo da gaskiya, sauran kuma ka bar ma Allah.✍️...
07/08/2025

Wato ita rayuwa kullum ka yi ƙoƙari ka bi Allah da ManzonSa sannan ka yi riƙo da gaskiya, sauran kuma ka bar ma Allah.

✍️ Umar Shehu Zaria
12 Safar, 1447
(06/08/2025).

ALHAMDULILLAH Addini Ya samu karuwa Yanzu daga Masallacin Usman Bin Affan Gadon Kaya ta hannun Babban Mallamin mu Dr. Ab...
06/08/2025

ALHAMDULILLAH

Addini Ya samu karuwa Yanzu daga Masallacin Usman Bin Affan Gadon Kaya ta hannun Babban Mallamin mu Dr. Abdallah Usman Gadon Kaya

Muna Addu’ah Allah Ya Tabbatar dashi acikin Musulunci Ameeen

Salis Muhammad Naseer Taraba

Ka saba da yawan furta Subhanallahi wa bihamdihi a kowanne lokaci, musamman idan kana hutawa ko tafiya.Wannan zikirin ya...
06/08/2025

Ka saba da yawan furta Subhanallahi wa bihamdihi a kowanne lokaci, musamman idan kana hutawa ko tafiya.

Wannan zikirin yana goge zunubi, kamar yadda wani hadisi ya ce: "Duk wanda ya ce Subhanallahi wa bihamdihi sau 100 a rana, za'a gafarta masa zunubansa ko da kuwa sun kai kamar kumfar teku."

Yana daga cikin hanya mafi sauki da ake samun lada mai yawa da kusanci da Allah.

ABUBUWAN DA ZAKA YI SANNAN KUMA ZAKA MORE A RAYUWAR KA DUNIYA DA LAHIRA MATUKAR KAYI AIKI DA ABIN DA NA FADA MAKAN NAN S...
05/08/2025

ABUBUWAN DA ZAKA YI SANNAN KUMA ZAKA MORE A RAYUWAR KA DUNIYA DA LAHIRA MATUKAR KAYI AIKI DA ABIN DA NA FADA MAKAN NAN SUNE KAMAR HAKA.

Kana bukatan Lada ba tare da Ka Wahala bah, Kayi sharing domain Al Umma su Anfana da Kai Kayi Sadakatul Jariya Lada Mai Gudana Kai ma.

• Abubuwa bazasu taɓayi maka daidai ba har sai ka chanja rayuwarka

• Idan ka shagaltu da rusa waninka ' babu ranarda zaka gina kanka

• Kada ka zamo mai shagaltuwa da faɗin Aibobin mutane, hakan bazai bari ka taɓuka komaiba

• Kada kayi gãbã da hassada saboda yana janyo karayar Arziki da talauci da tsiya

• Kada ka kullaci kowa Azuciyarka - saboda mummunar ɗabi'ace dake gadar da dawwamammiyar wahala tsawon rayuwa

• Kada kayi bakinciki don ɗan uwanka ya samu wata ni'ima, idan kayi bakinciki saboda falalar Allah akan wani bawansa, za'a shafemaka samun ni'ima makamancinta tawon rayuwarka

• Bazaka taɓa zama nagartaccen mutum ba har saika chanja rayuwarka - Babu wanda zai kasance ya zama mumini har sai wanda tsoron Allah ta zauna a zuciyarsa

• Kada ka riki wata kungiya ko ɓangaranci da niyyar hura wutar kiyayyah Atsakanin Al'ummah - duk wanda yake kawo rabuwarkai A tsakanin Al'ummar musulmi hakika yana tawaye daga abinda manzon Allah (ﷺ) ya zantar da Alami (Al'muslim Akhul Muslim)

• Kamar yadda samaniya ta nisanta da ƙasa toh ka nisanci waɗannan Abubuwa guda 5

1. Girman kai
2. Karya
3. zalunci
4. chin Amana
5. Maula da roko

: itace tushen laifuka kuma itace silarda tasa sheɗan yazama korarre daga rahamar allah ma'abota girman kai jagoransu sarkinsu shaiɗan ne iblis

: Karya tana cikin jerin manyan laifuka wadda Allah ta'ala bayaso Anaimata kallon karamin laifi alhalin zunubinta mai nauyi ne A mizani

: Allah ta'ala ya haramta wa kansa zalunci saboda haka ya maisheta haramun Atsakankanin halittunsa

: Duk wani maci Amana mataccen me rai ne kuma yana ɗauke da babbar Alama ta halaka

: tana gadarda mutuwar zuciya da raunin imani wanda ya buɗewa kansa kofar maula ko roƙo ba tareda wata karɓaɓɓen daliliba bashakka ya buɗewa kansa kofar talauci

Allah ta'ala ya tsare mana imaninmu... Ameen.



゚viralシfypシ゚viralシalシ


Salihi Ahmad Ibrahim ✍️

Address

No. 3 Ali Master Street, Unguwan Suleiman, Barwa
Kaduna

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Suleiman Nura Sa'idu posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Practice

Send a message to Suleiman Nura Sa'idu:

Share