Al-Ihsan Islamic Chemist

Al-Ihsan Islamic Chemist Muna sayar da magungunan Musulunci Wanda suka hada da ciwon Ulcer, Sahihin maganin Basir, Typhoid da

18/06/2022

SHAIKUL ISLAM IBNU TAIMIYYA YAYI BABBAN KUSKURE DA TA TUHUMI SAYYIDUNA ABDULLAHI DAN UMAR (RA) DA NUNA CEWA DAN BIDI'A NE (CIGABA)
To amma kuma duk da haka, ]aya daga cikin wa]ansu magabatan malamai, wanda duniya ta yi masa shaida a kan }o}arin bincike ta fuskar ilimi, a fannona da dama, babban malami Shaikhul Islami Ibnu Taimiyya, wanda ya rubuta tarin littattafan da shafukan littattafan su ka haura dubu arba’in (40,000) a fannona da dama, to, shi kam a irin na shi hange da kuma irin fahimtarsa, Abdullahi [an Umar, bai wuce ]an bidi’a ba. Sannan kuma a bayyane ne yayi k**a da aikin Annabi to, sai dai a manufarsa, ya fi k**a da Yahudawa ne. Wannan maganar, tana da matu}ar ha]ari ga daliban ilimi irin mu. Saboda haka, idan da so samu ne, da k**ata yayi manyan malamai su ri}a barin irin wa]annan matsalolin can a tsakaninsu, ta yadda ba ma za su iya isowa zuwa gare mu ba, b***e har su iya saka mu a cikin ru]ani da kuma fitina, wanda ni ke ganin cewa, k**ar yin hakan bai dace ba.
Idan shehin malami Ibnu Taimiyya ya mayar da martani a kan wani malmamin da s**a yi zamani tare da shi, ya kuma jingina wata maganar s**a zuwa gare shi a kan kowace irin mas’ala ce, to muna iya fahimtar wani abu a nan, ba tare da lura da wanda ke bisa daidai ko kuma wanda ya dare a kan hanyar kuskure a tsakaninsu ba. A’a, abin lura a nan kawai shi ne, malamai ne kuma tsarakun juna, wanda faruwar hakan a tsakaninsu, ba wani abin mamaki ba ne.
Za mu cigaba In Sha Allah.
📝 SHEIKH MUNTAKA MUHAMMAD USMAN BILBIS

12/06/2022
AKWAI BUKATAR AMSA TAMBAYOYIN MUNTAKA BILBIS DANGANE DA MASU CEWA IYAYEN MANZON ALLAH (SAW) SUNA CIKIN WUTA KAMAR YADDA ...
29/05/2022

AKWAI BUKATAR AMSA TAMBAYOYIN MUNTAKA BILBIS DANGANE DA MASU CEWA IYAYEN MANZON ALLAH (SAW) SUNA CIKIN WUTA KAMAR YADDA IBNU TAIMIYYA YA TAFI A KAN SA
Tambayoyin da zan iya gabatarwa a nan kuwa, su ne:
Shin mene ne dalilin da ya sa Ibnu Taimiyya ya ta}aita bayaninsa a kan waccan ruwayar ta Imamu Muslim kawai, wadda kuma ita ka]ai ce ruwayar da ta nuna cewa iyayen Manzon Allah kafirai ne, duk da cewa akwai wata ruwayar da ba haka ta nuna ba?
Shin a she, a tattaro ruwayoyin baki ]aya, sannan a shimfi]a bayanan da magabata s**a yi a kan ruwayoyi, musamman ganin cewa, maganar tana da matu}ar girman ha]arin gaske, yayin da ta shafi makomar iyayaen Manzon Allah a wurin Ubangiji, shin yin hakan ba shi ne abin da ya fi dacewa ba?
Shin idan dai har ya tabbata cewa, Manzon Allah (S.A.W) ya gaya ma mutumin da ke tambaya game da makomar iyayensa mushirikai, sai Manzon Allah ya gaya masa cewa, a duk lokacin da ya wuce wani }abarin mushiriki, to ya yi masa albishir da shiga wuta. Idan kuwa har haka ne, a lokacin da Manzon Allah ke tsaye a }abarin mahaifiyarsa wadda ruywa ta nuna cewa kafira ce, mene ne ya hana Manzon Allah ya yi ma ta bushara da wuta, a madadin haka, sai kawai ya fashe da kuka?
Shin abin da ruwayar ta bayyana na cewa Manzon Allah ya fashe da kuka, wanda har hakan ya sa mutanen da ke gefensa s**a fashe da kuka, shin wanan yana daga cikin halayyar da ta dace da halayen Manzon Allah?
Idan dai har ya tabbata cewa mahaifiyar Manzon Allah kafirace k**ar yadda ruwayar ta bayana, shin a kan mene ne Manzon Allah yake tsananta kuka, wanda har tsananin kukansa ya sa mutanen da ke gefensa s**a fashe da kuka?
Shin saboda tausaya ma mahaifiyarsa ne wadda ta mutu a matsayin kafira, k**ar yadda ruwayar ta nuna, musamman don masaniyar da yake da ita kan cewa kafiri ba zai samu gafara ba?
Ko kuwa a a, yana tsananta kuka ne domin mai yiwuwa Allah Ya tausaya masa Ya ba shi damar neman mata gafara daga baya, ta yadda za ta iya samun rahamar Ubangiji?

Address

205 College Road
Kaduna

Telephone

+2348083568778

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Al-Ihsan Islamic Chemist posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Practice

Send a message to Al-Ihsan Islamic Chemist:

Share