Taskar Murtala Kawo

Taskar Murtala Kawo لِكُلِّ دَاءٍ دَوَاءٌ
(1)

GANYEN OREGANO GA LAFIYA;DAGA Taskar Murtala Kawo KARKASHIN CIBIYAR MAGUNGUNAN MUSULUNCI DA GARGAJIYA TA Daru-Shifa Prop...
07/01/2026

GANYEN OREGANO GA LAFIYA;

DAGA Taskar Murtala Kawo KARKASHIN CIBIYAR MAGUNGUNAN MUSULUNCI DA GARGAJIYA TA Daru-Shifa Prophetic $ Herbal Medicine Store WHATSAPP 08037624598

Tabbas Allah Maɗaukaki bai halicci komai a banza ba. Duk abin da Ya fitar daga ƙasa, Ya sanya masa amfani ga rayuwar ɗan Adam, ko a fili ko a ɓoye. Daga cikin irin waɗannan ni’imomi akwai ganyen oregano, wanda likitancin gargajiya ya dade yana amfani da shi wajen warkar da cututtuka da dama.
Domin dama ubangiji ya Sanar Damu Cewa;
Allah "Shi ne Wanda Ya fitar da tsirrai daga ƙasa, Mun fitar da su domin amfanin ku.”
(Suratul An‘am: 99)

Haka Malamai sun bayyana cewa:
“Asalin dukkan tsirrai halas ne, kuma ana amfani da su a matsayin magani muddin ba su cutar da mutum.”
(Ka’ida daga Tibb – Ilimin magani a Musulunci)

Shi dai Amfanin wannan Ganyen na Origano a a binciken masana gargajiya Yana da yawa Daga Cikin amfanin shi an tabbatar da cewa Yana ƙarfafa garkuwar jikin Dan'adam. Haka kuma yaana taimakawa wajen yaƙar ƙwayoyin Cututtuka kala daban daban. Sannan wannan Ganyen Yana sauƙaƙa Matsalolin numfashi da tari.
Yana kuma gyara matsalar rashin narkewar abinci da Matsalolin ciki.
Wannan Ganyen tabbas Yana rage zafi da kumburi. tabbas wannan kaɗan ne Daga Ayyukan wannan Ganyen maganin shiyasa ma Manzon Allah (s.a.w) ya ce:
“Allah bai saukar da wata cuta ba face Ya saukar da maganinta.”
(Bukhari da Muslim)

Imam Ibn Qayyim (Rahimahullah) ya ce:
“Yawancin magungunan da Allah Ya halitta a cikin tsirrai sun fi dacewa da jikin mutum fiye da magungunan da aka sarrafa, idan aka yi amfani da su da ilimi.”
(Tibbun Nabawi)

Sheikhul Islam Ibn Taymiyyah (Rahimahullah) ya ce: “Magani yana da hukunci k**ar abinci; idan yana amfanar jiki ba tare da cutarwa ba, to yana cikin abin da Allah Ya halatta.”

Imam Malik (Rahimahullah) ya ce:
“Babu laifi mutum ya yi magani da abin da aka sani yana warkarwa muddin bai saɓa wa Shari’a ba.”
Shiyasa kullum muke cewa abi tsarin amfani da magungunan musulunci da Gargajiya domin Samun lafiya kada Kaji ance Habbatu Saudah tana magance dukkanin Cuta kaje ka k**a dirka ba tare da Ilmin yanda Ake sarrafa ta ba, Daga Karshe kazo kana karyatawa bayan kaine makaryacin tunda kayi amfani da ita batare da Ilmi ba.
Yan'uwa shi wannan Oregano Yana da hanyoyin da Ake sarrafa shi ta hanyar Ilmin magungunan Misali: ana iya tafasa ganyen a sha k**ar shayi Kuma ana iya busar dashi a daka a haɗa cikin zuma ana Sha.
Haka ana iya amfani da man oregano wajen shafawa domin magance Matsalolin fata.

Yaku Bayin Allah shi yasa Allah Ta’ala Ya ce:
“Ku ci daga abin da ke cikin ƙasa, halal ne kuma mai kyau.”
(Suratul Baqara)
Sannan ana iya hada wannan Ganyen na Origano da wasu tsirrai k**ar su citta kanumfari da su yansun da Sauran su domin magance Matsalolin Sanyi dashi.

Amma kusani wannan dukkanin su ana yine Bisa kwarewa da sanin Ilmin magungunan musulunci da Gargajiya domin kada mutum yayi Abun da zai Cutar da lafiyar shi da kanshi musulunci Bai yarda da Hakan ba shiyasa ma Manzon Allah (s.a.w) ya ce: “Jikinka yana da haƙƙi a kanka.” (Bukhari)

Saboda haka, a yi amfani da oregano Karkashin umurnin masana Ilmin magungunan musulunci da Gargajiya.

Ganyen oregano hujja ne cewa Allah Ya cika duniya da magani da hikima.

Yin amfani da shi bisa ilimi, da imani da tsoron Allah hanya ce ta samun lafiya da yardar Allah.

Zaku iya bibiyar wannan Shafin ta hanyar WhatsApp ta Link k**ar haka:

https://whatsapp.com/channel/0029VaMZkNdDjiOhBlBqLo46

WANDA S**A FARA BADA NASU SADAKATUL JARIYA NA SAKA SOLER A MASALLACI DOMIN GUDANAR DA IBADAN RAMADAN CIKIN KWANCIYAR HAN...
07/01/2026

WANDA S**A FARA BADA NASU SADAKATUL JARIYA NA SAKA SOLER A MASALLACI DOMIN GUDANAR DA IBADAN RAMADAN CIKIN KWANCIYAR HANKALI

1. WANI BAWAN ALLAH N50,000

2. Wani Bawan Allah Ya Saka Sadakatul Jariya Na Kudin Soler N10,000

3. Haka wata baiwar Allah itama ta Saka Sadakatul Jariya N1000

4. Wani Bawan Allah N500

5. Wani Bawan Allah Yasa N1000

Yanzun muna da N67,500 a kasa Allah ya Karo mana irin su masu Neman yardar Allah.

TOTAL KUDIN SAKA SOLER MASALLACIN DAI N535,500 NE

KUMA MUNA MARABA DA WANDA ZAI IYA DAUKAR NAUYIN AIKIN FISABILILLAH

Muna Addu'ar Allah Ubangiji Ya Biya masu Bukatar su na alkhairi.

Yasa Sanadiyar Aljannah ce ya kara daukaka da arziki Mai albarka.

Muna Kira da bayin Allah da su taimaka Fisabilillah Domin Samar Da Wannan aikin alkhairi na Saka soler a wannan Masallaci Fisabilillah.

Tabbas AIKIN mune masallata Babu Wanda zai iya yi mana irin wannan ayyukan sai dai mu da kanmu da dukiyoyin mu, kada mu Raina abun da zamu Saka Fisabilillah.

BANK DETAILS

MONIEPOINT MFB

KHAIRUL UMMA FOUNDATION SERVICES

ACCOUNT NUMBER; 6458095114

A TAIMAKA MANA DA SHARED

06/01/2026

S***M BOOSTER NA GARGAJIYA – Domin INGANTA LAFIYAR MANIYYI!

Shin kana fama da raunin maniyyi, kaɗan yawan maniyyi, ko matsalar ingancin s***m?
Ga maganin gargajiya na musamman da aka sarrafa daga tsirrai masu ƙarfi domin inganta lafiyar maniyyi daga tushe!

Abubuwan da yake taimakawa a kai:

Ƙara yawan maniyyi (s***m count)

Inganta ingancin maniyyi (motility & quality)

Taimakawa wajen ƙarfafa maniyyin da yake da rauni

Tsaftace jiki daga abubuwan da ke lalata s***m

100% na gargajiya ne!
Ba sinadarai, ba illa, lafiya ce cikakkiya ta halitta!

Idan lafiyar maniyyi ce matsalar ka – wannan shi ne abin da kake nema!

A samu yanzu daga:
DARU-SHIFA PROPHETIC AND HERBAL MEDICINE STORE, KAWO KADUNA
WhatsApp 08037624598

SADAKATUL JARIYA DONATIONS – MOSQUE SOLAR SYSTEM PROJECTMOSQUE ADDRESS NO 1 KARAMA ROAD MANGWARON AGWAI MALALIN GABAS IG...
05/01/2026

SADAKATUL JARIYA DONATIONS – MOSQUE SOLAR SYSTEM PROJECT

MOSQUE ADDRESS NO 1 KARAMA ROAD MANGWARON AGWAI MALALIN GABAS IGABI KADUNA

Assalamu Alaikum Warahmatullahi Wabarakatuh

We wish to inform the Muslim community that, by the grace of Allah, we have begun receiving Sadakatul Jariya donations for the installation of a Solar System in the Mosque, in preparation for the coming month of Ramadan, for the purpose of:

Qur’anic recitation,

Ramadan Tafsir,

Prayers, and other acts of worship.

Donations received so far:

₦50,000

₦2,000

Total: ₦52,000

Total Estimated Money N535,500

May Allah reward the donors with Al-Jannatul Firdaus, open the doors of sustenance for them, by the blessing of Prophet Muhammad ﷺ.

Qur’an Said
“The example of those who spend their wealth in the way of Allah is like a grain which grows seven ears; in every ear there are a hundred grains.” (Surah Al-Baqarah: 261)

Hadith of the Messenger of Allah ﷺ
“Whoever builds a mosque for the sake of Allah, Allah will build for him a house in Paradise.”

(Bukhari and Muslim)

We continue to call on our Muslim brothers and sisters to keep supporting fisabilillah.
Do not underestimate whatever you are able to give, for Allah accepts little and multiplies it.

We also welcome anyone who is able to fully sponsor the entire project.

Account Details:

Moniepoint MFB

Account Number:
6458095114

Account Name:
Khairul Umma Foundation and Services

For more information: 08037624598

Please help by sharing, so that Allah may enable others to also support.

NEMAN TAIMAKO – SADAKATUL JARIYAKhairul Ummah Foundation and Services na kiran ’yan’uwa Musulmi da su taimaka domin siya...
04/01/2026

NEMAN TAIMAKO – SADAKATUL JARIYA

Khairul Ummah Foundation and Services na kiran ’yan’uwa Musulmi da su taimaka domin siyan Solar System ga Masallacin JIBWS MUS’AB BN UMAIR MASJID, dake No. 1 Karama Road, Mangwaron Agwai, Malalin Gabas, Igabi LGA, Kaduna.

Manufa: Samar da ingantacciyar wuta domin Sallah, Tafsirin Azumin Ramadan, Karatun Al-Qur’ani da sauran ibadu.

Adadin kuɗi ₦535,500.00

Ko kuma wanda Allah Ya h**e masa, zai iya zuwa ya sanya Solar ɗin gaba ɗaya a matsayin Sadakatul Jariya Fisabilillah.

Domin Allah (s.w.a) yana Cewa a ciki suratul Baqara aya ta 261

“Misalin waɗanda suke ciyar da dukiyarsu saboda neman yardar Allah, k**ar hatsi ne da ya tsiro ya fitar da zarraki bakwai, a kowace zara akwai hatsi ɗari.”

Haka Hadisin Manzon Allah (s.a.w) Shima Yana cewa “Idan ɗan Adam ya mutu, aikinsa yana yankewa sai abubuwa uku: Sadakatul Jariya, ilimi mai amfani, ko ɗa nagari da ke masa addu’a.” (Muslim)

ACCOUNT DETAILS

Bank: Moniepoint

Account Name: Khairul Ummah Foundation Services

Account Number: 6458095114

Ƙarin bayani: 08037624598

Allah Ya karɓi wannan aiki a matsayin Sadakatul Jariya, Ya saka wa duk mai taimako da alheri mai yawa a duniya da Lahira. Ameen.

SUPPORT ORPHANS 50 Days to RamadanAs the blessed month of Ramadan draws near, we humbly invite you to support orphans an...
31/12/2025

SUPPORT ORPHANS
50 Days to Ramadan

As the blessed month of Ramadan draws near, we humbly invite you to support orphans and the less privileged with whatever amount Allah places in your heart.

Your kindness will bring hope, relief, and smiles to those in need during this sacred season.

May Allah (SWT), in His infinite mercy, reward you abundantly, accept your charity, and grant you the greatest of rewards.

“I and the one who cares for an orphan will be together in Paradise like this.”
(Prophet Muhammad ﷺ – Bukhari)

BANK DETAILS
Bank Name: Moniepoint Microfinance Bank
Account Number: 6458095114
Account Name: Khairul Ummah Foundation Services
For Orphans & the Less Privileged

28/12/2025

Babban Matsalolin Musulmi a Najeriya: Rashin Haɗin Kai da Raunin Shugabanci

Babban matsalolin da Musulmi ke fuskanta a Najeriya su ne rashin haɗin kai da kuma rashin tsayayyen shugabanci daga bangaren Musulmi.

Alhali Allah Maɗaukaki ya riga ya umarce mu da haɗin kai, Ya ce:

“Ku riƙe igiyar Allah gaba ɗaya, kada ku rarrabu.” (Suratu Āli-Imrān: 103)

A fili yake yadda sauran al’umma ke dunkulewa a ƙarƙashin jagoranci guda, suna tsayawa kan muradunsu ba tare da rauni ba.

Amma a bangaren Musulmi, abin takaici ne yadda ake raina ko rage matsayin Sarkin Musulmi a matsayin jagoran Musulmi gaba ɗaya.

Duk da haka, shi ma jagora yana da alhakin tsayawa tsayin daka wajen kare Musulmi da ƙarfafa su,

k**ar yadda Annabi ﷺ ya nuna:
“Kowannenku makiyayi ne, kuma kowannenku za a tambaye shi game da abin da ya kula da shi.”
Bukhārī da Muslim

Wannan rarrabuwar kai da sabanin ra’ayi ne ya sa ake raina Musulmi, ana tauye musu haƙƙoƙinsu, a ƙasar da su ne mafi yawa. Allah ya yi gargadi kan hakan:

“Kada ku yi sabani, don kada ku yi rauni, ƙarfinku ya tafi.”
(Suratu Al-Anfāl: 46)

Maimakon Musulmi su tsaya tsayin daka wajen kare addininsu da martabar al’ummarsu, sai aka rungumi son kai, bangaranci da neman shugabanci domin amfanin kai.

Annabi ﷺ ya yi kashedi kan irin wannan hali, ya ce: “Wanda ya kira zuwa ga son bangaranci (asabiyya), ba ya cikinmu.” Abū Dāwūd

Hakan ya sa al’ummar Musulmi s**a rabu dangi-dangi, akida-akida, har ta kai ga ƙyama da gaba a tsakanin ’yan’uwa.

Alhali Manzon Allah ﷺ ya ce:
“Misalin muminai wajen ƙauna, jinƙai da tausayi k**ar jiki guda ne; idan wani sashe ya ji raɗaɗi, dukkan jiki yana tashi da zazzabi da rashin barci.” Muslim

Tabbas, mafita ita ce Musulmi su koma ga umarnin Allah da Manzonsa ﷺ ta hanyar haɗin kai, biyayya ga shugabanci na gari, da fifita muradin al’umma sama da na kai. Allah ya ce:

“Ku yi biyayya ga Allah, ku yi biyayya ga Manzo, da masu mulki daga cikinku.”
(Suratu An-Nisā’i: 59)

Matukar Musulmi ba su gyara kansu ba, Allah ya riga ya bayyana cewa canji ba zai zo ba:

“Lallai Allah ba Ya canza halin wani al’umma har sai sun canza abin da ke cikin kawunansu.”
(Suratu Ar-Ra‘d: 11)

Allah yasa mudace yasa mufi karfin zukatan mu Baki Daya Ameeen.

Cikin Sati Daya kachal Duk tsinkewar s***m dinka zai koma yayi kauri yayi kyau sosai da yardar Allah.Wannan maganin Mats...
25/12/2025

Cikin Sati Daya kachal Duk tsinkewar s***m dinka zai koma yayi kauri yayi kyau sosai da yardar Allah.

Wannan maganin Matsalolin S***m Mujjarab ne Wallahi da yawa Al'umma sun Samu haihuwa sanadiyyar amfani dashi.

WASU ALAMOMIN DA AKE GANE RUWAN MANIYYI MARA KYAU KO MARA HAIHUWA

Ga Alamomin k**ar haka:

1. Yana da k**anni baki-baki, rawa-rawaya ko madara-madara mai duhu.

2. Bashi da kauri ruwa-ruwa ne tsararo.

3. Yayin zubanshi Kadan Yake zuwa.

4. Baya da karfin zillo ma'ana baya tunkudan juna da karfi.

5. Idan ka zubashi a ruwan matsakaici wanda babu sanyi kuma babu zafi zakaganshi ya tarwatse maimakon ya kwanta kasan ruwan.

6. Idan aka zubashi a kasa ko a wani abu kudaje baza suci ba kwata-kwata sabo da yariga ya mutu.

Idan kana da wasu daga wannan alamun sai kayi kokarin mallakar wannan maganin namu na Inganta ruwan maniyi wato S***m Booster domin inganta lafiyar ka.

Zaku iya samu a shagonmu na Daru-Shifa Prophetic $ Herbal Medicine Store dake No, 30 Masanawa By Kudansa Road, Kusa da Gidan Hakimin Gundumar kawo dake kawo kaduna
Zaku iya kiranmu ko turo da sakon whatsapp a 08037624598

Sakon maganinmu na iya samunka a duk inda kake a fadin kasar nan cikin sa'a 24 batare da matsala ba da yardan Allah.

Alhamdulillah Masha'Allahu  Yan'uwa Musulmi Nayi Kukan farin ciki sosai game Da Samun nasarar hada kudin Gudun muwar aik...
21/12/2025

Alhamdulillah Masha'Allahu Yan'uwa Musulmi Nayi Kukan farin ciki sosai game Da Samun nasarar hada kudin Gudun muwar aikin ceton rai na wannan Yaron Allah ya Saka ma kowa da Gidan Aljanna yasa Albarka a cikin Rayuwar Wanda s**a taimaka tundaga Naira Dari biyar har masu har zuwa Masu Naira Dubu Dari biyar a dunkule. Allah Yasa hanyar shigarmu aljanna ce Gaba Daya. 🙏🙏🙏

Tsakanin CONVENTIONAL DOCTOR da TRADITIONAL DOCTOR, duk wanda ya ƙi yarda da ilimin ɗaya, to ko dai rashin ilimi ne, ko ...
21/12/2025

Tsakanin CONVENTIONAL DOCTOR da TRADITIONAL DOCTOR, duk wanda ya ƙi yarda da ilimin ɗaya, to ko dai rashin ilimi ne, ko kuma son zuciya irin ta ɗan Adam ne.

Domin kuwa Allah Maɗaukakin Sarki Ya ce:

Kuma a bisa kowanne mai ilimi akwai wanda yafi shi sani.
(Suratul Yusuf: 76)

Wannan aya tana nuna mana cewa ilimi ba na mutum ɗaya ba ne, kuma Allah ne Yake rarraba shi gwargwadon hikimar Sa.

Haka kuma Annabi Muhammad (s.a.w) ya ce:

Allah bai saukar da wata cuta ba face Ya saukar da maganinta.
(Bukhari da Muslim)

Wannan hadisi yana tabbatar da cewa magani yana wanzuwa ta hanyoyi daban-daban, ko ta likitan zamani (Conventional) ko ta likitan gargajiya (Traditional), muddin an bi gaskiya, ilimi da tsoron Allah.

Abin takaici, a ƙasar Nijeriya ne aka fi fuskantar wannan kalubale, inda wasu ke raina ilimin juna maimakon haɗa kai domin ceton rayukan bayin Allah Koda yake Mafi yawan Masu irin wannan yara ne a fagen Ilmin lafiya. Masu Ilmin Cikin su sun San amfanin maganin Gargajiya domin suna da Ilmin yanda Magabata s**a rayu da magungunan itatuwa da tsirrai kafin samuwar likitancin Zamani dama bayan samuwar shi.

Addinin Musulunci ya koya mana tawali’u, adalci, da girmama juna, k**ar yadda Allah Ya ce: “Kada ku raina juna.”(Suratul Hujurat: 11)

Don haka, wajibi ne mu fahimci cewa duk ilimi daga Allah yake, kuma haɗin kai tsakanin masu ilimi daban-daban shi ne hanya mafi kyau ta kawo ci gaban lafiya da jin daɗin al’umma.

Address

NO, 30 KUDANSA BY MASANAWA Road, KAWO, KADUNA
Kaduna
0062

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Taskar Murtala Kawo posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Practice

Send a message to Taskar Murtala Kawo:

Share

Share on Facebook Share on Twitter Share on LinkedIn
Share on Pinterest Share on Reddit Share via Email
Share on WhatsApp Share on Instagram Share on Telegram