Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu.

Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu. AN BUDE WANNAN SHAFI NE,SABODA TUNATAR DA KAWUKAN MU
BISA KYAWAWAN AL'ADUMMU NA HAUSA,

WADAN DA AYA Mungode

Dan Bunkasa Harshen Hausa da Al'adunsa,
Muna Maraba da shawarwarinku Domin wannan shafi naku ne.

ABIN MAMAKI: Yadda Aka K**a Fasto da Zargin Kai wa 'Yan Bindiga Mak**ai a Jihar Filato.Najeriya ta shiga wani sabon babi...
16/11/2025

ABIN MAMAKI: Yadda Aka K**a Fasto da Zargin Kai wa 'Yan Bindiga Mak**ai a Jihar Filato.

Najeriya ta shiga wani sabon babi mai ban al’ajabi — Inda aka k**a wani malamin addinin kirista (Reverend Father) da ake zargi da kai wa ‘yan bindiga muggan mak**ai a Jihar Filato da kewaye.

Eh, ka karanta daidai.
Wani limamin coci — wanda aka yarda da shi a matsayin mai addu’a, zaman lafiya da kare rayuka — yanzu ana zarginsa da taimakawa waɗanda ke hallaka al’umma marasa laifi.

Rahotanni sun ce jami’an tsaro sun gano yana *tsara safarar mak**ai iri-iri*, wanda ake zargi da taimakawa 'yan ta'adda wajen sace mutane, kai hari da kashe-kashe.

Yanzu sai na sake tambaya...

Lokacin da wasu daga cikinmu s**a ce *matsalar tsaro a Najeriya ba ta addini bace*, mutane s**a ci mutunci, suna cewa muna goyon bayan mugunta.

Amma yanzu, me za su ce?

Shin waɗanda s**a yi gaggawar garzayawa Amurka suna kiran abun “kisan kiyashi ga Kiristoci” za su kai wannan labari wajen Donald Trump domin daidaita labarin?

Domin gaskiya ita ce:

Tsaro a Najeriya ba ya da addini.
(1) Ba ya sanye da zobon saliba ko tesbihu.
(2) Ba ya rike Alƙur’ani ko Littafi Mai Tsarki.
(3) Yana buya a daji, yana sayen mak**ai, yana halaka rayuka — Musulmi, Kirista, kowa.

Amma duk lokacin da aka fadi gaskiya, mutane kan mayar da martani da ji ba da hankali ba.

Wannan k**a ta bayyana gaskiya mai zurfi:

(1) Matsala laifi ce, ba addini ba.
(2) Mugaye suna ko’ina — a coci, a masallaci.
(3) Kuma yaƙi yana da su ne, ba da addininsu gabaɗaya ba.

Idan har Reverend Father za a k**a da kai wa 'yan bindiga mak**ai, to watakila... matsalar Najeriya ta fi “kisan kiyashi a ɓangare guda” girma da rikitarwa.

Mu kira gara gari.
Mu gyara matsalar tsaro — ba mu juya ta ta zama siyasa ko neman tausayi daga ƙasashen waje ba.

Daga: Abdul Mdk

CIGABAN MANTA SALLAH — MAI RUBUTU A TSAYEBayan da aka zauna gaban kwamiti domin binciken zargin da Mista Barry Burgess y...
10/11/2025

CIGABAN MANTA SALLAH — MAI RUBUTU A TSAYE

Bayan da aka zauna gaban kwamiti domin binciken zargin da Mista Barry Burgess yake yi a kan Getso, sai shi Barry ya ce yana son shirin Manta Sallah na mako na 5, 7, 10, da kuma ragowar ukun ƙarshe a fassarasu zuwa Turanci.

Hakan kuwa aka yi, domin ma, mai gaba ɗaya aka yi. Duka guda goma sha uku sai da aka fassarasu zuwa Turanci. Daga nan ne aka ba Halilu Getso damar kare kansa a kan zargin Barry.

Ya ce, da farko dai, wannan shiri ya ta’allaka ne a kan yadda rayuwar Turawa take, wato abubuwan da suke yi na al’adunsu da tsare-tsarensu waɗanda ba a sani ba. Sai kuma abubuwan da ba sa yi amma ake jita-jita cewa suna yi, da kuma waɗanda suna yi ɗin amma an juya labarin sama ta koma ƙasa.

Ya ƙara da cewa, misali: mu a Najeriya, akwai Hausawa da suke tunanin cewa Bature zai fito waje ya je majalisa ko wata maciya a ƙarƙashin bishiya ko rumfa ya zauna, a kawo masa abinci yaci, ko kuma ya fita wajen mai shayi a haɗa masa shayi da biredi da ƙwai 🥚 k**ar yadda tamu al’adar take.

To a can, sam, ba haka bane. Ya ce, mu bamu da juriyar bibiyar abu, ko da kuwa haƙƙinmu ne, bama iya kai-kawo wajen ganin an biya ko an bayar. Amma a can, idan akwai wani haƙƙi na mutum ko na gwamnati, to dole sai an bibiya.

Ya ce, maganar ta’addanci da Mista Barry yake cewa na ce Turawa suna yi, to bai fahimta bane. Wato farkon zuwana nan (London), na kunna talabijin a gidan da nake, sai naga wata mata da aka nuna cewa Allah ya bata haihuwa, kuma mace mai lalura ce. Ita kuma bata son ƴa mace, ballantana mai lalura.

Kullum sai ta fito da ita waje ta ajiye a kan keken masu lalura, ta barta a nan babu kayan kirki a jikinta, ga kuma dusar ƙanƙara 🌨️. Ita a dabararta, bata so a tuhume ta da laifin kisan kai, shiyasa take yi mata wannan azabar domin ta mutu ta huta.

To kuma da yake Allah shi ne mai kashewa da rayawa, sai gashi ta ƙi mutuwa, amma tana matuƙar shan wahala. Ko ni daga inda gidana yake a London zuwa ofishinmu na BBC, train 🚉 nake hawa. Kuma daga inda yake ajiyeni zuwa harabar BBC, yawanci rigata da hulata suna cike da ƙanƙarar snow.

Wannan labarin ba ƙirƙira bane, a labarai na gani kuma ana hira da ita wannan matar. Ku bincika, zaku tabbatar da cewa haka abin yake. A Afrika kuwa, abin mamaki ne a ce uwa ta yiwa ɗiyarta haka.
Sai na tambayi Mista Barry,

“Yanzu ka gamsu da abin da nake faɗa, ko har yanzu kana kan batunka na cewa ina ɓata muku suna?”

🧾 Batun bin haƙƙi

Getso ya ce, akwai abokin aikina da ya hau jirgin ƙasa daga wata unguwa a London zuwa wata unguwa, sai aka samu matsala, wato a inda zai sauka jirgin bai tsaya ba sai a tasha ta gaba.
Mai karɓar tikiti (ticket collector) ya rubuta masa adireshin inda zai biya ragowar kuɗin da ake binshi, sannan ya bashi da nashi adireshin.

Amma abokin aikin ya ƙi zuwa ya biya. Bayan wa’adin da s**a bashi ya cika, sai s**a sake rubuta masa wasika ta tunatarwa cewa har yanzu bai biya ba. Wani abin mamaki, wasikar haɗe take da kan sarki (official letter), kuma kuɗin kan sarkin sun fi waɗanda ake binshi yawa.

Sai dai duk da haka, s**a rubuta masa sau uku ba tare da gajiyawa ba, har sai da ya gaji da kanshi, yana mita da surutu, ya je ya biya haƙƙinsu sannan ya huta.

“Wannan abin cigaba ne,” in ji Getso.
“Zai nuna wa shugabannin Afrika da ‘yan Afrika yadda ake riƙe aiki da gaskiya da rikon amana.
Kuma zai haskawa al’ummarmu yadda ake bautawa ƙasa da gudummawar da kowane ɗan ƙasa zai iya bayarwa domin cigaban ƙasarsa.”

A taƙaice dai, kwamiti ya gano cewa Getso yana kan daidai, kuma ya bayar da umarni cewa ya ci gaba daga inda ya tsaya — saboda abin birgewa ne.

Saboda haka, bashi da wata matsala. An ba da damar ci gaba da shirin daga inda aka tsaya.

Wannan shi ne cikakken abin da ya faru tsakanin Bature Mista Barry Burgess da kuma Bahaushe Halilu Ahmad Getso a Rediyo BBC Hausa London.

© Jiya Ba Yau Ba.

MANTA SALLAH, MAI RUBUTU A TSAYE. Wannan shi ne sunan wani shiri da Alhaji Halilu Ahmad Getso ya gabatar lokacin da yake...
10/11/2025

MANTA SALLAH, MAI RUBUTU A TSAYE.

Wannan shi ne sunan wani shiri da Alhaji Halilu Ahmad Getso ya gabatar lokacin da yake aiki da BBC Hausa, Landan. Shiri ne da ya jawo masa s**a daga wasu Turawan ƙasar Birtaniya, wadanda s**a yi zargin cewa yana cin zarafinsu ne ta hanyar abin da ke ƙunshe a cikin shirin.

Tabbas, labarin da nake son bayarwa zai ɗan iya ɗaukar lokaci, amma kuwa zai amfanar da ma’abota son aikin jarida, musamman ɗaliban ilimi, da duk wanda ke da son tarihi. Don haka, ku biyo mu a hankali.

Karin magana ta “Manta Sallah Mai Rubutu a Tsaye” ta samo asali ne tun lokacin da Turawan mulkin mallaka s**a shigo Najeriya, musamman yankin Arewa. Karin maganar tana da tsawo, amma yawancin ɗaliban ilimi basa sanin ƙarshenta. Ga cikakkiyar karin maganar k**ar yadda take:

“Manta Sallah Mai Rubutu a Tsaye, Huntu Ubangijin Mai Riga, Mai Shawara Ɗari Ɗaya Babu, Ta Ɗarin Ya Fasa, Ku Ci Gari Ku Kwana a Daji.”

Yanzu bari mu ajiye wannan bangaren, mu koma ga labarin shirin “Manta Sallah Mai Rubutu a Tsaye”, wanda aka gabatar a shekarar 1975 a BBC Hausa. Wannan ya faru ne bisa tsarin da gidan rediyon ke amfani da shi a lokacin, cewa duk wanda ya yi aiki a BBC, ana ba shi damar ƙirƙirar shiri na musamman na tsawon kwata ɗaya ko biyu kafin ya kammala aikinsa ya koma gida.

Haka abin ya kasance ga Halilu Getso, wanda FRCN Kaduna s**a ba da aron sa zuwa BBC na tsawon shekaru biyu. Kafin cikar wannan wa’adin, sai ya ƙirƙiri shirin Manta Sallah Mai Rubutu a Tsaye, wanda ya ƙunshi season ɗaya mai episodes goma sha uku.

Sai dai daga baya aka kai ƙarar Getso wajen shugabansu na lokacin, David Warren, sannan aka mika ƙarar zuwa ma’aikatar cikin gida ta Ingila da kuma ofishin jakadancin ƙasar a Landan. Wanda ya kai ƙarar kuwa shi ne wani Bature mai suna Barry Burgess.

A cikin ƙarar da ya gabatar, Barry Burgess ya zargi Halilu Getso da cin zarafin Turawa a cikin shirin, yana cewa kalamansa sun ƙunshi ƙazafi, ɓatanci, da nuna bambancin launin fata.

David Warren, babban daraktan BBC Hausa a lokacin, bai ɗauki zancen da wasa ba. Sai dai kafin ya yanke hukunci, ya tabbatar da cewa an kafa kwamitin bincike domin gano gaskiyar lamarin, k**ar yadda umarni ya zo daga sama.

A cikin rahoton ƙarar, an zargi Getso da cewa:

Yana nuna cewa Turawa basa da imani,

Yana cewa suna ƙin wanda ba nasu ba,

Kuma yana zarginsu da rashin yafiya da girman kai.

Waɗannan sune manyan tuhume-tuhumen da aka gabatar a kansa a wancan lokaci. Ba tare da bata lokaci ba, aka kira shi domin ya kare kansa idan yana da abin karewa.

Zamu ci gaba da wannan labarin a gaba.

© Jiya Ba Yau Ba.

10/11/2025

❤️يَأَيُّهَا الَّذِينَ امَنُوا صَلُّوا عَلَيْهِ وَسَلِّمُوا تَسْلِيمًا❤️

- _Lugude_ MAKAMAN KANO BA KA YI KIWON BANZA BA. Ran 2 ga watan Fabrairu na shekarar 1942, Mak**an Kano ya ta da baraden...
07/11/2025

- _Lugude_

MAKAMAN KANO BA KA YI KIWON BANZA BA.

Ran 2 ga watan Fabrairu na shekarar 1942, Mak**an Kano ya ta da baradensa, ya ce su tafi duk inda Amareta ya ke, a bugo shi da jama’a tasa, a kawo su a ɗaure. Aka yi shiri aka tafi. Da zuwan baraden nan, sai s**a iske Amareta bisa kujera mutane sun kewaye shi, sai molo da warin giya ke tashi. Ana masa kirari: ‘‘Umaru dan Kurtullu Sarkin Ɓarayi! Sata a wurinku ba dashe ba ce, gado ce. Ubanka ya yi, kakanka ya yi, kuma ɗanka zai yi, jikanka zai yi!’

Da s**a yi arba da baraden nan, sai ya yi wa sojansa umurni, nan da nan sai ga su kowa da kibiya ɗane a bakansa. Da ganin haka sai Kutiki ya murza hular layu, ya sauko daga doki, ya tara ƙasa a gabansa misalin tukubar tsire. Sai ya koma kan doki ya ce, ‘Bismilla!’ ‘Ɓarayin nan s**a yi ta aikowa da kibiyoyi k**ar zubar ruwan sama. To, kowace kibiya ta zo, ba ta sauka ko ina, sai kan ’yar tarin ƙasar nan, har kibiyoyi s**a ƙare duk.
Kutiki da Afilu s**a matsa dawaki, sai ga su a tsakiyar askarawan. Sai takuba da gatura da wuƙaƙe a ke ta amfani da su. Duk mak**an ɓarayin s**a lalace, aka shiryo su a ankwa aka kawo su gun mak**a. Mak**a ya yi murna ƙwarai da gaske da wannan.
—M. Talle Daura diresan Wudil.

📌DAYA DAGA CIKIN KAYAN AZABTARWA MAFI BAN TSORO😨Sun kira shi Kujerar Yahuda. Wani nau'in azabtarwa ne da ake fara wa mut...
28/10/2025

📌DAYA DAGA CIKIN KAYAN AZABTARWA MAFI BAN TSORO😨

Sun kira shi Kujerar Yahuda.
Wani nau'in azabtarwa ne da ake fara wa mutum tsirara, a zaunar da mutum kan tsinin samansa.
Sai a fara gangaro da mutum a hankali, cike da radadi.

An ce akan soka mutane ne ta wuraren da s**a Fi rauni a jiki, ko ta dub*ra(Namiji kenan) ko ta far*i (mace kenan).
Azabtarwan kan iya ɗaukan sa’o’i, wani lokacin har kwanaki.
Masu azabtarwan har ma suna rataye abubuwa masu nauyi daga idon sawun wa'anda ake azabtarwan. s**an tilasta musu gangarowa ta inci da inci.
An fara ambaton Kujerar a cikin Turai, ƙarni na 19.

An nufi Kujerar Yahuda ne an don azabtar da mutane a bainar jama’a. An ce an yi amfani da ita don tilasta ikirari, hukunta ’yan bidi’a, ko tsoratar da duk wanda ya ƙalubalanci iko.
Wahalar ba ta ɓoye ba, akan nuna ta ga bainar jama'a, dan a wulakanta mutum.

A yau, ana iya gani kwafin(copy) Kujerar Yahuda a gidajen tarihi na azabtarwa a duk faɗin duniya.

Darasi: Wato duk Wanda ya kirkiri wannan abun, ba karamin mugu bane. Tabdi jam😱



ENGLISH TRANSLATION IN THE COMMENT SECTION 👇

I GEMBU: Garin Da Ya Tara Tsala-tsalan 'Yan Mata Mafi Kyawu A NijeriyaDaga Saliadeen SiceyGembu birni ne, da ke a yankin...
27/10/2025

I GEMBU: Garin Da Ya Tara Tsala-tsalan 'Yan Mata Mafi Kyawu A Nijeriya

Daga Saliadeen Sicey

Gembu birni ne, da ke a yankin Duwatsun Mambilla, a Jihar Taraba, a Nijeriya. Ita ce hedikwatar karamar hukumar Sardauna (tsohuwar "Mambilla") a jihar Taraba.

Mutanen Mambilla ko Mambila na Najeriya suna zaune a tudun Mambilla. Kadan daga cikin 'yan ci-rani na Mambilla sun tashi daga duwatsun Mambilla zuwa filin Ndom da ke gefen K**aru na kan iyakar kasa da kasa da kuma wasu kananan kauyuka, k**ar sabuwar Namba, da ke kan arewa zuwa garuruwan Gashaka da Banyo.

Mambila na Zaune a matsakaita tsayin kusan mita 1,348 (4,423 ft) sama da matakin teku, yana daga cikin manyan biranen Najeriya.

Tarihi

An yi imani tun da dadewa cewa mutanen farko na mazaunan Duwatsun Mambilla su ne zuriyar kakannin Bantu. mutanen Bantu waɗanda s**a zauna a Gembu ta zamani bayan faɗaɗar Bantu a faɗin Afirka daga 4000 zuwa 3500 Kafin Haihuwar Annabi Isa AS

Dalilin Da zai sanyaku zuwa mambila

1, Garin yafi ko'ina matan fulani kyawawa

2, Dutsen Mambila yana Jahar Taraba kuma shine wuri mafi sanyi a Najeriya baki daya. Akasarin yara da ke tasowa a yankin ba su taɓa ganin na'urorin da ke bayar da sanyi a zahiri ba sai dai a talabijin ko kuma litattafai.

Gembu a ranar hudu ga watan Satumban shekarar 2021, yanayin sanyi ya kai maki 17 digiri selshiyos.

Shi ma shafin da ke wallafa bayanai na intanet Wikipedia ya tabbatar cewa ƙauyen Dorofi da ke kan tsaunin na Mambila shi ne yanki mafi sanyi a Najeriya.

Da zarar ka fara haurawa kan tsaunin daga wani ƙauye da ake kira Mayo Selbe da ke karamar hukumar Gashaka za ka hangi tsauni mai tudun gaske lulluɓe da koren ciyayi da bishiyoyi da hazon ƙanƙara iya hangenka.

Daga wannan ƙauyen ne yanayi ke sauyawa daga zafi zuwa sanyi ko kuma sanyi zuwa ɗan karen sanyi.

Kana isa kan tsaunin daga garin Maisamari har zuwa sauran ƙauyuka da s**a yi iyaka da jamhuriyar K**aru za ka iske kusan kowa ya yi shigar maganin sanyi.

Za ka ga mutane da manyan rigunan sanyi da ake kira "Kuntu" da hulunan sanyi da takalma sau ciki domin maganin sanyi.

3, Saboda sanyi yasa mutanen wurin basa amfani da Firji, AC, ko fanka, domin duk wani nau'in kayan sha ko yaushe da sanyin sa.

4, kusan Kowa a garin ya iya fillanci duk dacewa manyan yaruka da kabilu 4 ne a yankin wanda s**a hada da Mambilawa, Fulani, Panso da Kakah.

5, Hotel yanada araha a yankin domin akuwai dakin ₦1500

6, Garin yana da arzikin duwatsun daimond da blue sapaya, kana sunada arziƙin shanu shi yasa nama yake da araha a yankin.

7, Sunada nau'in kayan itace da nau'in abinci daban-daban har da wanda baka taba ganiba b***e ci, wanda s**a hada da piya, ayaba, chanis apple, mangoro, bulumji, deppi, dankalin turawa, samaije da sauransu, gwaiba kam tun a hanya zaka tsaya ka tsinka a hanya.

8, kauyukan da suke da kyawawan mata a dutsen mambila su hada da, Kakara, Leme, Yarimaru, Mayo-ndaga, Dorofi, Nguroje, da Galadima.

9, Dutsen yafi ko ina yawan itacen zaiti a Najeriya

10, Babu sauro a garin.

11, Manyan garuruwa da suke kan dutsin mambila sun hada da, Gembu, Nguroje, Mayo-ndaga (d**o cede) da Mai samari.

TARIHIN SHEIKH MODIBBO JELANI AL-TIJJANI, YOLAAn haifi Sheikh Modibbo Abdul-Qadir Jelani Ibn Modibbo Altine wanda aka fi...
25/10/2025

TARIHIN SHEIKH MODIBBO JELANI AL-TIJJANI, YOLA

An haifi Sheikh Modibbo Abdul-Qadir Jelani Ibn Modibbo Altine wanda aka fi sani da "Sheikh Modibbob Jelani Yola" a shekara ta 1903 a wani kauye mai suna "Badara" dake cikin jihar Bauchi. An ba shi sunan Abdul-Qadir Jelani saboda mahaifinsa wato (Modibbo Altine) ya kasance mai riko da Darikar Sufate ta Kadiriyya.

Modibbo Jelani ya fara koyo a wurin mahaifinsa tun yana dan shekara 14. Mahaifinsa ya rasu, ya bar Modibbo Jelani, kaninsa Muhammad Tukur da kuma wata kanwa mai suna Sutrah.

Don ci gaba da karatu, Modibb Jelani ya zagaya wurare da dama, ya kuma koyi darasi daga manyan malamai na wancan lokacin. Daga cikin wuraren da ya ziyarta da kuma malaman da ya koyo da su sun hada da Kano da Zariya; wato Mallam Sani Harazimi da Shariff Sani Tudun Wada Zaria. Daga nan ya koma Kano zagaye na biyu domin karin neman ilimin addinin Musulunci bayan ya karbi Darikar Sufaye ta Tijjaniyya. Yayi "Tarbiyyah" a hannun Babban Shehi, "Shaikh Tijjani Usman Yan Mota" , Kano (wanda Sheikhul Islam Alhaji Ibrahim Inyass RTA ya sabunta masa shi).

Bayan shekaru, Modibbo Jelani ya koma garinsu (Badara) ya yanke shawarar ci gaba da tafiya Makka k**ar yadda mahaifinsa marigayi ya fara. Ya zauna a wurare daban-daban a cikin garin Gombe kuma yana da mabiya da yawa wadanda dalibansa ne da sahabbansa. Ya shiga Adamawa ya sauka a “Gudumiya” (wani kauye a karkashin Hong L.G.A, Adamawa). Lamido Muhammadu Mustafa (1928-1946) ya gayyace shi kan cewa ya dawo Yola da zama, amma shi kuma ya zabi zama a Gudumiya sabida ya fi jin dadin zama a garin.
Duk da haka, bayan wasu shekaru Modibbo Jelani ya gamsu da bukatar Lamido Ahmadu (1946-1953) daga bisani ya koma Yola da zama.

Ya sadaukar da rayuwarsa wajen koyo da koyarwa da yada addinin Musulunci da Daular Sufanci ta Jijjaniya ta hanyar manyan dalibansa, mabiyansa da kuma yayansa. Modibb Jelani ya rasu, aka binne shi a gidansa da ke Yola yana da shekaru 83 a duniya a shekara ta 1986.
Allah ya jaddada Rahma

Kotun ta ce nan da kwanaki 60 a daura wa Ashiru da sahibarsa aure. Kotun ta kuma umurci hukumar tace fina-finai ta jihar...
20/10/2025

Kotun ta ce nan da kwanaki 60 a daura wa Ashiru da sahibarsa aure. Kotun ta kuma umurci hukumar tace fina-finai ta jihar kano da ta sa ido don ganin an daura wannan auren.

Mene ne fatanku gare su?

Hoto: Ashiru FB

10/10/2025

*TALLA TALLA TALLA*

*GURU NA FAMILY PLANING.*

Amincin Allah Su Tabbata Agareku Dafatan kuna Lafiya Cikin Amincin ALLAH.

Albishirinku Yan Uwa Masu Girman Daraja Da Albarka,A Yau Munzo Muku Da Guru Na Tazarar Haihuwa.

Wannan Guru Ne Na Tazarar Haihuwa,Idan Mace Ta Ɗaura Wannan Guru A ƙugunta Yayi Kwana Ɗaya A Jikinta Sai Tayi Shekara Ɗaya Bata Haihu Ba, Haka Nan Idan Yayi Kwana Biyu a Jikinta Shekara Biyu Zatayi Bata Haihu Ba.

Ma'ana Duk Adadin kwanakin Da Wannan Guru Yayi A Jikinta Shine Shekarun Da Zatayi Bata Haihu Ba.

-ABINDA ZA'A KIYAYE SHINE:-

Matar Da Zata Ɗaura Wannan Gurun Ta Tabbata Be tsinke Ba a Lokacin Da take Ɗaura Shi,Sannan Ta kiyaye Karya Kunce Har Sai Tayi Adadin kwanakin Da take Buƙata.

Sannan Ta Nisanci Kusanta(Saduwa) a Lokacin Da Take Ɗaure Dashi a ƙugunta.

Ga Wanda Suke Da Buƙata Sai Su Tuntuɓemu a Wannan Number:-

-07066778330

Dan Asalin Jihar Katsina Injiniya Ibrahim Lawal Dankaba Ya Kera Motar Sulke Domin Kare Al'umma Rubutun Katsina TimesWani...
06/10/2025

Dan Asalin Jihar Katsina Injiniya Ibrahim Lawal Dankaba Ya Kera Motar Sulke Domin Kare Al'umma

Rubutun Katsina Times

Wani ɗan asalin Katsina, Injiniya Ibrahim Lawal Dankaba, ya ƙera wata mota ta zamani mai sulke wadde aka sanya mata suna “Begua” kalmar Hausa da ke nufin dabba wadda take da ƙashin kariya a jikin ta.

A cikin tattaunawar da Majiyar Accuracy News Hausa "Katsina Times" ta yi da matashin Injiniya Dankaba ya bayyana cewa, aikin wata hanya ce ta tsaron al’umma domin ƙara ƙarfin rundunonin tsaro na Gwamnati da kuma dawo da kwarin gwuiwar jama’a a yankunan da matsalar tsaro ta addaba.

“Mun zaɓi wannan suna ne saboda ma’anarsa. Begua ba ta fara farmaki sai an cuce ta. Idan aka kawo mata hari ne kawai take kare kanta. Haka nan wannan mota ba don tada rikici aka yi ta ba, sai don kariya idan aka kawo wa al’umma hari,” in ji shi.

Motar Begua ta bambanta da sauran motocin sulke da ake gani a kasuwa saboda tana amfani da taya-trak (tracked APC) maimakon taya na al’ada. A cewar Injiniya Dankaba, hakan ya fi dacewa da yanayin ƙasar nan da kuma buƙatun tsaro na karkara.

Za ta iya shiga gonaki, dazuzzuka da ƙasa mai laka.

Ba ta cika makalewa a cikin caɓo ko hanya mara kyau ba.

Tana bayar da kariya mai ƙarfi ga mutanen da ke cikinta.

Dankaba ya ce aikin ya wuce matakin zane a takarda, yanzu haka ana kan gwajin samfurin farko. Ya ƙara da cewa an fara tunanin aikin tun kusan shekaru biyu da s**a wuce a lokacin da hare-haren ’yan ta’adda da ’yan bindiga s**a ƙaru a arewacin Najeriya.

“A cikin ’yan makonni masu zuwa, za mu gayyaci jama’a da manema labarai domin kallo da shaida yadda Begua za ta yi aiki,” in ji shi.

Ya jaddada cewa aikin ba zai maye gurbin jami’an tsaro ba, sai dai ƙarfafa musu guiwa.

“Wannan aikin haɗin kan al’umma ne domin tallafawa gwamnati da hukumomin tsaro. Muna son haɗin kai tsakanin jama’a, gwamnati da masu ruwa da tsaki domin kare rayukan mutane,” ya bayyana.

Ga mazauna yankunan da ke fuskantar matsalolin tsaro, Injiniya Dankaba ya ce:

“Mun san irin fargaba da damuwar da jama’a ke ciki. Saƙonmu shi ne muna ɗaukar matakai na zahiri don taimaka musu. Duk da cewa gwamnati da jami’an tsaro su ne ginshikin tsaro, al’umma da kirkire-kirkiren cikin gida ma suna da rawar da za su taka. Begua wani ɓangare ne na wannan gudummawa,” in ji shi.

Katsina Times za ta kawo muku cikakkiyar tattaunawa da aikin Begua ta kafafenmu na Katsina Times TV (YouTube), Katsina City News (Facebook), da sauran shafukanmu na sada zumunta.

Hoto: Katsina City News

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu. posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Practice

Send a message to Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu.:

Share

Share on Facebook Share on Twitter Share on LinkedIn
Share on Pinterest Share on Reddit Share via Email
Share on WhatsApp Share on Instagram Share on Telegram