12/05/2026
HEADMASTER NA FARKO A AREWACIN NAJERIYA...
Shin kunsan wanene Magajin Gari Muhammadu Sambo ?
Marigayi Magajin Gari Sambo: Shine wanda ya kirkiri Kaduna ta Zamani, Malamin Farko ɗan Asalin Arewa, kuma Jagoran Ƙungiyar Turawan Birtaniya da ta Gudanar da Ƙirga Mutane (Ƙdaya) ta Farko a Arewacin Najeriya a 1923.
Labarin Muhammadu Aminu Sambo labari ne na jajircewa, sadaukarwa, Nagarta adalci da jagoranci. An haife shi a shekara ta 1888 a Zariya, daga babban gida mai daraja, zuriyarsa tana komawa Gidan Mal Tajo, ɗan Malam Musa Bamalli, wanda shi ne mai ɗaukar tutar Shehu Usman Ɗan Fodio, kuma wanda ya kafa gidan sarautar na Mallawa a masarautar Zazzau.
Tunaninsa ga ilimi ya bayyana tun yana ƙarami. Bayan ya kware a karatun Alƙur’ani, sai ya zama ɗaya daga cikin ‘yan Arewa na farko da s**a rungumi ilimin Turawa (ilimin boko) wani mataki mai ƙarfin da ya sauya rayuwarsa da ta al’ummarsa baki ɗaya.
Hanyarsa ta ilimi ta fara ne a shekara ta 1903 a Makarantar Kano Provincial School, inda yake ɗalibi na takwas da aka rubuta a rajista. Daga 1903 zuwa 1908, ya shimfiɗa tubalin sadaukar da rayuwarsa ga neman ilimi da wayewa.
A 1910, ya zama Malami mai kula (Headmaster) ɗan asalin ƙasa na farko a Makarantar Zariya Provincial School (wanda yanzu ake kira Alhudahuda College). Wannan nasara ta nuna irin jajircewarsa wajen ci gaban ilimi. A 1912, aka naɗa shi Headmaster na farko a Makarantar Bauchi Middle School (wacce daga baya aka sani da Sambo College of Education). A nan ne ya koyar da ilimi tare da karfafa tunani mai zurfi da neman ilimi.
A 1916, aikinsa ya ɗauki sabon salo lokacin da Sarkin Zazzau Aliyu Ɗan Sidi ya naɗa shi Wamban Zazzau kuma Hakimin Jaji. A wannan Lokacin ya fara gina wani gidan baki (guest house) wanda daga baya ya zama Command and Staff College Jaji, babbar cibiyar soja a Najeriya.
Sai dai a 1920, Sarkin Zazzau Dalhatu ya kwace masa sarauta, amma bai fid da rai ba. A 1923, a sake karramashi a lokacin da aka zaɓe shi ya jagoranci ƙungiyar Turawan Birtaniya da s**a gudanar da ƙirga mutane ta farko (Ƙidaya) a Arewacin Najeriya. Sak**akon haka, Sarkin Ingila, Sarki George, ya ba shi takardar yabo (Certificate of Honor) a 1924.
A 1925, aka dawo da shi sarautar Hakimci tare da bashi kuma ba shi Hakimi mai kula da Sabon Gari Zariya. Ya taka muhimmiyar rawa wajen gina Sabon Gari, Zariya, inda ya kafa makarantar firamare, da kuma haifar da sabbin unguwanni irin su Muchia da Dogon Bauchi daga 1927 zuwa 1930.
A 1937, tasirinsa ya bazu zuwa Kaduna, inda aka ba shi sarautar Magajin Garin Zazzau a lokacin Sarkin Zazzau Ja’afaru Ɗan Isiyaku.
A zamaninsa, Kaduna ta samu ci gaba sosai — an raya Tudun Wada, Unguwan Shanu, da wasu unguwanni. A 1943, ya fara shirin dasa itatuwa wanda ya kyautata kyawun gari, sannan ya ƙirƙiri lambar gidaje ta haruffa da lambobi (alpha-numeric house numbering), wanda ya taimaka wajen tsara gari da gyara harkokin gine-gine.
A 1956, ya kafa tarihi na zama mutumin farko daga Arewa da ya zama Administrator (Shugaba) na Gwamnatin Ƙaramar Hukumar Kaduna. A wannan shekarar kuma, Sarauniya Elizabeth II ta ba shi lambar yabo ta Member of the British Empire (O.B.E.) saboda gudunmawarsa ga al’ummarsa.
Ayyukan Muhammadu Aminu Sambo sun wuce zamaninsa. Gudunmawarsa a ilimi, ci gaban birane, da gudanarwa sun bar gagarumin tasiri a Arewacin Najeriya. Makarantun da ya kafa sun zama cibiyoyin ilimi, kuma hangen nesansa wajen tsara gari da kula da muhalli ya zama abin koyi ga shugabanni na gaba.
Ya rasu a shekara ta 1961, ya bar tarihin gaskiya, jagoranci, da ci gaba. A yau, sunansa yana nuni da ƙarfin ilimi, shugabanci mai hangen nesa, da ƙoƙarin cigaban al’umma.
Allah ya gafarta masa da dukkan magabatanmu.
Daga Dandalin Tarihin Magabata