Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu.

Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu. AN BUDE WANNAN SHAFI NE,SABODA TUNATAR DA KAWUKAN MU
BISA KYAWAWAN AL'ADUMMU NA HAUSA,

WADAN DA AYA Mungode

Dan Bunkasa Harshen Hausa da Al'adunsa,
Muna Maraba da shawarwarinku Domin wannan shafi naku ne.

HEADMASTER NA FARKO A AREWACIN NAJERIYA... Shin kunsan wanene Magajin Gari Muhammadu Sambo ? Marigayi Magajin Gari Sambo...
12/05/2026

HEADMASTER NA FARKO A AREWACIN NAJERIYA...

Shin kunsan wanene Magajin Gari Muhammadu Sambo ?

Marigayi Magajin Gari Sambo: Shine wanda ya kirkiri Kaduna ta Zamani, Malamin Farko ɗan Asalin Arewa, kuma Jagoran Ƙungiyar Turawan Birtaniya da ta Gudanar da Ƙirga Mutane (Ƙdaya) ta Farko a Arewacin Najeriya a 1923.

Labarin Muhammadu Aminu Sambo labari ne na jajircewa, sadaukarwa, Nagarta adalci da jagoranci. An haife shi a shekara ta 1888 a Zariya, daga babban gida mai daraja, zuriyarsa tana komawa Gidan Mal Tajo, ɗan Malam Musa Bamalli, wanda shi ne mai ɗaukar tutar Shehu Usman Ɗan Fodio, kuma wanda ya kafa gidan sarautar na Mallawa a masarautar Zazzau.

Tunaninsa ga ilimi ya bayyana tun yana ƙarami. Bayan ya kware a karatun Alƙur’ani, sai ya zama ɗaya daga cikin ‘yan Arewa na farko da s**a rungumi ilimin Turawa (ilimin boko) wani mataki mai ƙarfin da ya sauya rayuwarsa da ta al’ummarsa baki ɗaya.

Hanyarsa ta ilimi ta fara ne a shekara ta 1903 a Makarantar Kano Provincial School, inda yake ɗalibi na takwas da aka rubuta a rajista. Daga 1903 zuwa 1908, ya shimfiɗa tubalin sadaukar da rayuwarsa ga neman ilimi da wayewa.

A 1910, ya zama Malami mai kula (Headmaster) ɗan asalin ƙasa na farko a Makarantar Zariya Provincial School (wanda yanzu ake kira Alhudahuda College). Wannan nasara ta nuna irin jajircewarsa wajen ci gaban ilimi. A 1912, aka naɗa shi Headmaster na farko a Makarantar Bauchi Middle School (wacce daga baya aka sani da Sambo College of Education). A nan ne ya koyar da ilimi tare da karfafa tunani mai zurfi da neman ilimi.

A 1916, aikinsa ya ɗauki sabon salo lokacin da Sarkin Zazzau Aliyu Ɗan Sidi ya naɗa shi Wamban Zazzau kuma Hakimin Jaji. A wannan Lokacin ya fara gina wani gidan baki (guest house) wanda daga baya ya zama Command and Staff College Jaji, babbar cibiyar soja a Najeriya.

Sai dai a 1920, Sarkin Zazzau Dalhatu ya kwace masa sarauta, amma bai fid da rai ba. A 1923, a sake karramashi a lokacin da aka zaɓe shi ya jagoranci ƙungiyar Turawan Birtaniya da s**a gudanar da ƙirga mutane ta farko (Ƙidaya) a Arewacin Najeriya. Sak**akon haka, Sarkin Ingila, Sarki George, ya ba shi takardar yabo (Certificate of Honor) a 1924.

A 1925, aka dawo da shi sarautar Hakimci tare da bashi kuma ba shi Hakimi mai kula da Sabon Gari Zariya. Ya taka muhimmiyar rawa wajen gina Sabon Gari, Zariya, inda ya kafa makarantar firamare, da kuma haifar da sabbin unguwanni irin su Muchia da Dogon Bauchi daga 1927 zuwa 1930.

A 1937, tasirinsa ya bazu zuwa Kaduna, inda aka ba shi sarautar Magajin Garin Zazzau a lokacin Sarkin Zazzau Ja’afaru Ɗan Isiyaku.

A zamaninsa, Kaduna ta samu ci gaba sosai — an raya Tudun Wada, Unguwan Shanu, da wasu unguwanni. A 1943, ya fara shirin dasa itatuwa wanda ya kyautata kyawun gari, sannan ya ƙirƙiri lambar gidaje ta haruffa da lambobi (alpha-numeric house numbering), wanda ya taimaka wajen tsara gari da gyara harkokin gine-gine.

A 1956, ya kafa tarihi na zama mutumin farko daga Arewa da ya zama Administrator (Shugaba) na Gwamnatin Ƙaramar Hukumar Kaduna. A wannan shekarar kuma, Sarauniya Elizabeth II ta ba shi lambar yabo ta Member of the British Empire (O.B.E.) saboda gudunmawarsa ga al’ummarsa.

Ayyukan Muhammadu Aminu Sambo sun wuce zamaninsa. Gudunmawarsa a ilimi, ci gaban birane, da gudanarwa sun bar gagarumin tasiri a Arewacin Najeriya. Makarantun da ya kafa sun zama cibiyoyin ilimi, kuma hangen nesansa wajen tsara gari da kula da muhalli ya zama abin koyi ga shugabanni na gaba.

Ya rasu a shekara ta 1961, ya bar tarihin gaskiya, jagoranci, da ci gaba. A yau, sunansa yana nuni da ƙarfin ilimi, shugabanci mai hangen nesa, da ƙoƙarin cigaban al’umma.
Allah ya gafarta masa da dukkan magabatanmu.

Daga Dandalin Tarihin Magabata

ABUBUWA 50 DA YA KAMATA IYAYE SU LURA DA SU,DOMIN HANA YAYANSU FADAWA ZINACE-ZINACE.(3)12. HANA YAYA MATA DA S**A BALAGA...
11/05/2026

ABUBUWA 50 DA YA KAMATA IYAYE SU LURA DA SU,DOMIN HANA YAYANSU FADAWA ZINACE-ZINACE.(3)

12. HANA YAYA MATA DA S**A BALAGA WASAN KOKAWA KO RUNGUME-RUNGUME.

Akwai wata sabuwar dabi'a da ta bayyana wadda mutane suna ganinta ba komai ba,ita ce yawan mannewa juna mace da yar'uwarta mace musamman kawaye,wanda suna kaiwa su saba da juna suna iya bayyanar da kirjinsu ga junansu basu damu ba da sauran abubuwa da yawa har suna iya shiga bandaki daya su yi wanka.

Yana da kyau su sani kasancewarsu mata ba yana nufin ya halastawa kowacce kallon jikin yar'uwarta ba,ta janubinmu mu masu fadakarwa a kiyaye saboda gudun fadawa halaka,ta bangaren halasci ko haramci a nemi malamai su yi bayani.

13. NAZARIN 'YA'YA DOMIN TANTANCE KARFIN SHA'AWARSU.

Yana da kyau ya zama muna iya banbance karfun sha'awar yaranmu lokacin da su ka balaga,hakan zai sa mu lura da wurren da su ke iya shiga su kadai ba tare da Security ba..

14. ABINCI

Duk lokacin da yayanmu su ka kai marhalar balaga,dole mu lura da irin abincin da muke basu,kada a rika basu abubuwan da su ke tara sha'awa.

15. TUFAFI.
A bangaren yaya mata,dole ne mu kiyaye sosai wajen hana su sanya kaya masu bayyana tsiraici koda a cikin gida ne b***e waje,domin hakan ke kai idanuwan lalatattu zuwa kan yaya mata,haka ma samarin da su ke makota da su.

Haka suma Mazan a hana su saka kayan da ba su dace ba,suna yawo a tsakiyar kananan yan mata.
1. Gajeren wando zallah,wanda wani yana tafiya ana ganin motsin gabansa.
2. Singlet
3. Ko yawo ba riga yana bayyana cibiyarsa a tsakiyar yaran gida wasu ana iya ganin gashin cibiyarsu basu damu ba,kuma iyaye basu tsawatar ba.

Wannan duka ana maganar yayanmu da ke rayuwa waje daya ne kanne da yayye,na dangi da na makota.

16. KWANCIYA
Yana da kyau idan yayanmu suna kwance mu rika lura da irin wanciyar da su ke yi.Kwanciya tana daga cikin abubuwan da su ke da tasiri wajen tunzura sha'awa.Yana da kyau a yi kokarin hana yara kwanciyar rub da ciki,ko rungume filo da sauransu.

A muhimmantar musu da kwanciya a barin hannun dama yana da muhimmanci sosai.

17. DAUKEWA YAYANMU MATA BUKATUN YAN DA KULLUM.

A nan za mu ja hankalin iyaye maza wanda zan ce 90% daga cikinsu basa lura da matsalolin yayansu mata.

Mutum yana da 'Ya ta balaga amma bai san a ina take samun kudin sayen audugar mata ba,kai bai taba hirar da mahaifiyarta ba,bai ma san ta fara al'adaba ko aa,bai san ina take samun kudin Kyan amfaninta na yau da kullum ba,har kananun sutura irinsu Pant,underwear da brassiere,b***e a yi maganar kayan kwalliya.

Ita mace akan kanta tana so ta ji ta yi kwalliya ta fi samun nutsuwa da sukuni koda kuwa bata da aure.

Maza da yawa sun dauka ita mace tana yin kwalliya ne kawai saboda biki ko miji,lallai ba haka bane.

Mace tana jin dadi da samun farinciki ta yi wanka ta yi kwalliya ta duba mudubi ta kalli kwalliyarta koda kuwa barci zata kwanta,to wane taimako muke yiwa yayanmu da basu da mazaje ?

Akan wannan bukatar mata da yawa sun fada mummunan hannu.

Mata da yawa sun bada kansu sabi kananun bukatun wanda sun gagara fadawa iyayensu saboda kunya.

Yana da kyau a rika basu kyautar kudade masu nauyi dan biyan bukatarsu wadda ba lallai iyaye maza su kai hankulansu kanta ba.

18. KYAN KALLO.
Wajibine ga iyaye su lura da irin tashohin da yayansu ke kallo.

19. LITATTAFAI.
Duk lokacin da ka ga yaro da littafi ka tabbatar ka amsa ka ga maye a cikinsa,haka a rika yawan bincika jakunkunansu ana ganin me su ke ajiyewa ciki.

20. WAYA.
Tana daga cikin abubuwan da su ke lalalata tarbiyyar yayanmu,wajibine ku rika sanin abubuwan da ke cikin wayoyin yayanku.

Tun daga shafukan Social media zuwa fima-fimai da ake turawa.

21. KIRAN WAYA.
Idan so samu ne duk wanda ya kira yarki a waya ya zama kina kusa da ita kina jin me ake tattaunawa,kuma kada a tsawaita,idan so samu ne kada a yarda su mallaki layukansu saidai su yi amfani da wayoyinku,idan suna son waya to idan sun yi aure mazajensu su saya musu.

Za mu ci gaba Insha'Allah
08034318311
11/05/2026

ABUBUWA 50 DA YA KAMATA IYAYE SU LURA DA SU,DOMIN HANA YAYANSU FADAWA ZINACE-ZINACE.(2)3. SON JIKI.A kwai yaran da ake h...
11/05/2026

ABUBUWA 50 DA YA KAMATA IYAYE SU LURA DA SU,DOMIN HANA YAYANSU FADAWA ZINACE-ZINACE.(2)

3. SON JIKI.
A kwai yaran da ake haihuwarsu da son jiki wanda za ka ga ko da yaushe suna makalewa a jikin mutane,wasu ma sai kaga suna shafa mutum,yana da kyau a rika tsawatar musu ana takaita musu yawan bin jikin mutane da su ke.

Daga cikin matsalolin da hakan ke haifarwa:..

Za su iya fadawa hannun mutanen banza,sannan kuma za su iya tashi suna bin jikin mutane ba tare da wata damuwa ba.

Wasu shekaru masu nisa na taba ganin wata yarinya bata fi shekaru 4 ba,amma tana kwantawa a jikin mutane tana cewa dadi ta ke ji,har na tsawatar mata, tare da masu tambayarta me ta ke ji.

4. RABA WAJEN KWANCIYA.
Rabawa yaranku maza da mata wajen kwanciya,sannan da nuna musu haduwar mace da namiji waje daya ba abu ne mai kyau ba tun suna yara,har wasanni idan zai yiwu a raba musu.

Na san lokcin da muna yara idan aka ga Namiji yana wasa da Mata ana ce masa Na Mata Na Mata,idan mace ce,ana ce mata,mai wasa da maza karya,tunda na ganta na rainata....

Lallai wannan ya sa Mace da Namiji suna tashi kowannensu na kyankyamin ya kusanci dan'uwansa ko da uwa daya uba daya su ke,wanda a yanzu wannan zamanin ya rusa mana wannan tsarin,sai ya zama suna tashi tare su balaga a waje daya,shi kuma wannan canjin da ake samu na shekarun balaga ba ruwansa da sabo yan'uwantaka,nasan an sha samun matsaloli na yara uwa daya uba daya.

5. BOYE TSIRAICINSU.
A nuna musu tun tasowa suna da wasu wurare da ba a so kowa ya gani.
Hakan yana taimakawa lokacin da girma ya zo musu su kara tsananta kyamar bayyanar da wasu sassan jikinsu a tsakaninsu.

Wannan za mu iya cewa koda kuwa uwa daya ne uba daya,a tabbatar suna boye wasu sassan jikinsu tsakanin koda mace da mace haka namiji da namiji,b***e kuma mace da namiji.

A wannan wurin zan so mu yi jan hankali ga iyayen da basu damuwa da sauyawar kirjin yayansu mata,wanda ya dace tun kafin lokacin su fara nuna musu muhimmancin rayuwa da hijabi.

Shi wanda ku ke ganin dan'uwanta ne da su ke rayuwa sha'awarsa bata gaya masa haram da halas,addini ne kawai yake fadin wannan.

A shari'a har iyaye akwai wuraren da haram ne yayansu su kalla nasu b***e kuma kanne da yayye.akwai kuma wanda bai k**ata ba,..a gaban danki da ya kai shekaru sama da 10 ki rika fito da kirjinki waje a gabansa,wannan ba muna cewa haram bane idan ana son sani a je wajen malami,amma dai kada a saba masa da kallon wadannan wuraren tun a gida,domin zai zama ba sa kyankyamin kallo ha a waje..

6. Cakuduwar yara maza da mata waje daya tsirara koda kuwa lokacin wanka ne.

Akwai matsaloli da su ke yawan faruwa na yara da ake samu suna aikata munanan dabi'u duk da su basu kai lokacin balaga ba.

Na farko k**ar yadda muka fada kwakwalar dan'adam na cike da tambayiyi ne kuma tun daga yarinta,to su yara wannan banbamcin idan su ka gani so su ke sai sun tabbtar ya ya ke,to sakaya wurin yana hana tunaninsu yakai wurin.

7. CANZA TSARIN ZAMAN MAKARANTU.
An ci bahaushe da yaki wajen nuna masa mace da namiji abu daya ne musamman a makarantun zamani,tun daga yarinta ake cakudasu waje daya komai ana hada su yi harda kokawa,a nan yara ke tashi basa jin tsoron hada jiki da mata,kuma wannan lokacin shine gini na farko da ake yiwa yara na tarbiyya.

A nan yaro yake tasowa har balaga ba'a taba nuna masa banbancin mace da namiji ba,ana rayuwa babu kyankyami har su balaga a tare,suna shiga makaranta tun suna yara,idan makarantar ta zama mai hade da secondary haka zaka ga sun zama kawayen juna,gasu shekarunsu ya kai na balaga,amma komai tare ake,..kwallo guje-guje zama waje daya cin abinci tare,wannan kam ba bukatar dogon sharhi,kowa zai gane kuma zai halarto da barnar da ke faruwa.

8/9. KWADAYI DA DANGANA.
Hana yara kwadayi ta hanayar koya musu dangana dole,ya zama yaro da kansa ba komai zai gani ya sa ransa ba.
Tun suna yara ya zama ba komai su ka gani iyaye na ci sai an basu ba,wannan abu ne mai wiya amma yana da kyau.Haka kuma ba komai ne in za a basu sai an ci ba,Musali:

Iyaye su zo da abu mai dadi su cinye su hana yayansu,wani lokaci kuma a zo da abu mai dadi a mika musu ba sai iyaye sun ci ba,ko kuma,..ba su san da shi ba su ga an dauko an basu,..Mun san wannan akwai wahala sosai wani ma ba zai gane falsafar da ke ciki ba,amma akwai amfani matuka,horaswa ce sosai,duk ba za a gane ba sai an je da yaro cikin taro ya zama ba ya sa ido a kan abubuwa na ci ko sha za a gane fa'ida,sannan za a gane munin abin idan yaro ya hango wani abu na ci ko sha a wani gida ko a hannun yara ya sakawa abin ido.

Hakan yana nuna musu cewa,ba komai bane idan su ka gani sai sun ci,sannan ba komai bane idan aka basu yana nufin saida aka ci aka rage ba.

Idan yaro ya ko yi wannan,ko da ya hadu da yara masu munanan dabi'u abin hannunsu ba zai sa yakwantar da kai a wajensu ba,haka ma manya masu yaudarar yara da wasu abubuwa dan lalata su.

Sannan wannan ginin na farko na tarbiyyar yara anan ake samun matsala,yaro ya koyi wasu dabi'u da har tsufansa ba zai iya dainawa ba..

10. ROKO.
Wannan musamman yaya mata,iyaye masu yawan roko suna aika yara wurare a roko musu abu,hakan yana sanyawa yara su tashi basa kunyar rokar abu,to babbar illa tana ga 'ya mace.Lokacin da mace ya zama bata da kunyar roko to ba zata iya banbance inda ake yinsa ba,kuma wannan yana kai su ga fadawa mummunan hannu,kuma rokon zai zamar musu jiki basa ganinsa a matsala har girmansu.

11. DOLE NE KULA DA LOKUTAN BALAGA NA YARA.
A nan muna so iyaye su sani kuma su ajiye tsohon lissafin da su ke da shi na da can a kan abinda ya shafi lokacin balagar yara.

Duk wanda ya ke da 'ya mace,daga lokacin da ta kai shekaru 9 idan ya dauka cewa yarinya ce karama ya yi kuskure,masana sun gano mace na fara balaga ne daga shekaru 9 kenan daga 8 za mu fara saka ido a kansu.

Haka namiji daga shekaru 15 ya ke fara balaga,..kenan daga shekara 14 za mu saka musu ido.
Kamar muna so muce,idan yaranmu su ka kai wannan shekarun kada mu dauka basa jin dadin taba juna tsakanin mace da namiji,wanda a yanzu haka ake tafiya,yarinya zata kai shekaru 12/13 amma za ka ga samari na rike mata hannu suna wasa da ita saboda babu alamar girma da ya bayyanar mata,alhalin tana jin dadi,shi ya sa itama ta ke haye musu ko yaushe,musamman masu tallace-takkace,ko kuma rayuwar Family,kuma wasu abubuwan idan su ka faru ai ta mamaki.

A irin wannan lokacin wajibine raba musu wajen kwanciya,ma'ana kada a rika hada su daki daya maza da mata,idan maza ne kowa ya koma gefensa da ban shi kadai,idan mata ne suma kowa da gefensa shi kadai.

Ba'a so mace da mace su rika shafar junansu a lokacin haka ma Namiji,shafar da zata bayar da wata ma'ana.

Za mu ci gaba Insha'Allah

Shareef Muhsan Bachirawa
08034318311
10/05/2026

ABUBUWA 50 DA YA KAMATA IYAYE SU LURA DA SU,DOMIN HANA YAYANSU FADAWA ZINACE-ZINACE.Duk da cewa a ciki akwai abubuwan da...
11/05/2026

ABUBUWA 50 DA YA KAMATA IYAYE SU LURA DA SU,DOMIN HANA YAYANSU FADAWA ZINACE-ZINACE.

Duk da cewa a ciki akwai abubuwan da za su zama tsohon yayi,wanda iyaye su ke kallonsa a matsayin abinda ya shude kuma zai wiya su iya dawo da shi,hakan ba zai hana mu kawo su ba.

Sannan akwai abubuwa da kiyaye su akwai takurawa,amma a haka dai za mu fada wanda ya ke ganin ya shirya gina tarbiyyar gidansa sai ya yi hakuri ya kwatanta.

Sannan mu sani,
Sai an nemi taimakon Allah bayan an kiyaye.

Sannan za mu kawo komai ne bisa rayuwarmu ta yan Arewa,watakil kuma ya iya amfanar wasu da ba yan Arewa ba.

1. MAKWANCIN IYAYE:

Duk da ba lallai bane kwakwalen wasu su kai ga tsinkayo tasirin da makwancin iyaye yake da shi a wajen yayansu,saboda sabuwar wayewa da aka shigo da kuma zamani,amma wajibine mu sani cewa.
Shi yaro daga lokacin da ya fara gani da idanunsa,so ya ke ya fayyace duk abinda ganinsa ke iya kaiwa.Duk wata rayuwa da iyaye ke yinta yana kallonta kuma yana son sanin hakikarta.Insha'Allah wanda su ke bibiyar rubutun da muka fara mai taken, *HANYOYIN DA ZA KU GINA TUNANIN YAYANKU..* A ciki za mu kawo abubuwan da su ka fi yiwa yaro tasiri a marhalar rayuwarsa ta farko.

A zamanin da ya shude,babu yadda za a yi yaro ya tashi ya ga mahifinsa akan gado a kwance,b***e ya ganshi a jere shida mahaifiyarsa akan gado daya ko a kwance ko a zaune.

Gadon hausawa na lokacin ana yinsa ne mai labule kuma a saka sattara a tsakani, ba yadda za a yi a shiga da yaro wannan wurin,yaro yana tashi ne yana ganin wurin a rufe da sattara kuma har ya kai munzalin balaga bai isa yaga shimfidar nan ba.

Mai gida baya shiga wannan wuri sai ya tabbatar da yara sun yi barci,haka daga sallar asuba baya sake waiwayen wannan wuri,idan kuwa mai yin barcin safe ne,zai kiyaye ba yadda za a yi yara su ga fitowarsa daga wajen,idan kuma ya zama dole su gani,..to kuma fa ba za su taba ganin Uwarsu akan wannan gadon ba ko da rana b***e da daddare.

Yanzu kai ya waye,yaran da mu ke rainawa suna da tunani wuce na lokacin yarintarmu,kuma iyaye basa kiyaye abubuwa da yawa,wanda su ke jefawa yayansu tunani da tambayoyin yaya su ke,k**ar yadda muka kawo a wancan rubutun cewa..Shi dan'adam yan tashi da tambayoyi ne na duk abinda ya ke kewaye da shi,so ya ke sai ya sanshi ya san hakikarsa koda wuta ce kuwa.

Wasu abubuwa da iyaye ke dauka wayewa ce,suna jefa tambyoyi a kwakwalen yayansu da kuma bukatar sai sun san ya su ke kuma sai sun ta hankoron kwatawantawa,shi yasa wasan farko da yara suke fara yi a rayuwarsu wanda ba kirkirar musu shi aka yi ba shine...
Wasan Mata da Miji,ko wasan Malami da Dalibai,saboda ita ce rayuwar da su ke fara gani kuma su ke kokarin hakkake ta.

A irin wannan lokacin za mu san dabi'un da iyayensu ko malamansu ke aikatawa,za mu ga su su ke kokarin kwatantawa a tsakaninsu masu kyau da masu muni.

To yana da kyau iyaye su lura sosai tun daga kalamai da duk wani motsi da za su yi,su sani yaransu na lura da kiyayewa fiye da su iyayen.

Akwai takaici sosai yadda mu ka aro dabi'un da ba su dace da mu ba muka dulmiya kanmu a ciki,da nufin dole mu waye.Hakan ya sauya abubuwa da yawa na rayuwarmu,za mu yi bayani daga karshe.

2. YARAN DA KE WASANNIN DA YARANANKU.

Abin nufi anan shine..Bayan kun kiyaye naku bangaren,dole ku lura da yayan da su ke wasanni da yayanku a irin wannan lokacin.
."Da za ku zura ido na tsawon minti 30 idan yara na wasanni za ku sha karatu kala kala,za ku ga kowane yaro na kokarin misalta iyayensa ne ko Malaminsa na makaranta ko abinda ya fi yi masa tasiri..Ana tsakiyar wasa yaro zai ce a zo a yi wasan kaza saboda shima wannan ne bukatarsa.

Za mu ci gaba Insha'Allah

Shareef Muhsan Bachirawa
08034318311
07/05/2026

MACE MUTUM CE!(2)Ci gaba...To bari na gaya muku wata magana:..."Mace Mutum ce" kuma ta fi da yawa daga cikin maza duk ab...
02/05/2026

MACE MUTUM CE!(2)

Ci gaba...

To bari na gaya muku wata magana:...
"Mace Mutum ce" kuma ta fi da yawa daga cikin maza duk abinda ake bukata na k**ala,duk wata marhala da namiji ke iya takawa da karfin fidrarsa da Allah ya bashi,mace zata iya takawa,kai tana iya isa inda maza da yawa basa iyawa,muna da misalai sunfi dubu.

Shin ko kasan duk wannan dagawar da ka ke ji da jiji da kai, da duk wata falala da kake tak**a da ita wajen yin tunani na gano daidai da ba daidai ba,kaso 99% ka same shi ko ka gaje shi da Uwa Mace.

Ko da ya ke kana iya gane falalar haka akan iyayenmu mata,amma bama iy ganin haka a matanmu saboda ba su su ka haife mu ba.,muna jin dadi idan aka ce iyayenmu mata suna da basira kuma a wurinsu muka gado,Amma duk da haka muna mantawa sauran mata da basu haife mu ba, iyayen wasu ne kuma wannan kallon da mukewa wadanda su ka haife mu,haka suma yayan da s**a haifa su ke kallonsu,duk da cewa wannan rashin lafiyar tunnin na wasu mazan, tasirinsa ya kan kaiwa ita kanta mahaifiya idan yaro ya balaga ya ke fara sawa zuciyrsa ya fita tunani,saboda larurar ta zama ta gado.

Idan ana so a fahimci Alkiblar al'umma matan cikinsu ake kallo domin babu wasu mutne da za su haifo sai irinsu,ashe tasirin uwa yana da rinjye a al'umma,amma me ya sa mu ke kallonsu ba komai ba.

Namiji idan ya auri mace,bukatarsa kada ta gaza shi tunani,kuma so ya ke ita da iliminta da tunaninta su kom karkashin nasa ilimin da tunanin,koda kuwa bai karanta abin da ta karanta ba,baya hango abinda ta ke hangowa,kuma baya gane abinda ta ke ganewa,kawai tunda ita mace ce,shi kenan shine samanta a komai.
Ko da ya ke an koyar da mu cewa iliminsu bashi da wani amfani,harma wanda bai karatu ba zai iya kushe ilimin professor mace saboda kawai ita mace ce ba tare da wata hujja ba.

AL'MARIN KALLON MACE A BAKOMAI BA YA DADE CIKIN AL'UMMA.

Lamarin Kallon mace ba komai bace abu ne da ya dade,ba kuma daga hausawa bane kadai,.
Wannan cuta ce dadaddiya acikin al'umma wadda addinin musulunci ya zo ya taka mata birki.

Za mu ci gaba Insha'Allah

Shareef Muhsan Bachirawa
08034318311
02/05/2026

MACE MUTUM CE!(1)Ita mace tamkar gona ce da ake shuka acikinta dan samun amfani,idan na gaya muku abinda kuka sani ne......
02/05/2026

MACE MUTUM CE!(1)

Ita mace tamkar gona ce da ake shuka acikinta dan samun amfani,idan na gaya muku abinda kuka sani ne...To duk wanda ya fika kula da gonarsa sai ya fika samun amfani mai kyau da inganci.

Ba zai yiwu ka yi tsumbure a gonarka ba,kuma babu wadataccen taki,babu kyakkyawan iri sannan idan kaka ta yi ka debi buhuhuwa ka je dibar amfanin gona.

Sannan ka kwatanta ta da duk matsaloli da su ke bijirowa manomi,wanda zai ta jure su da dabaru ba gajiyawa,saboda yana da wani fata zuwa kaka.

Kaima k**ar haka za ka jure da gyara dan samun zuriyya dayyaba.

Karfi da razani da jiji da kai,ba ya iya juya ra'ayin mace,saidai zata iya yi maka shuru na wani lokaci watakil ma sai bayan kun tsufa zaka ga ashe wancan abinda ka zata ya gushe yana nan, alokcin da baka da sauran karfi,..

Yayin da kankanin lafazi cikin murya mai taushi ke iya sauya mata tunani na har abada.Mutuncinka ya karu darajarka ta karu,ta sallama maka fiye da duk yadda kake tsammani.

Matsala ta farko da namiji ya samu game da Mace ita ce:
Ya gina kwakwalwarsa ko an gina masa akan cewa ita mace ba komai bace,bata iya tunani,koda ta yi ma bashi da inganci.Yana dauka ba abinda mace zata iya a cigaban rayuwa,daga girki sai haihuwa,sai share-sharen gida,sannan ba'a bukatar yardarta ko shawararta wajen yanke kowane irin hukunci.

Wasu maza sun dauka Jarumin Namiji shine wanda ya gagari matarsa,idan ta ganshi ta rika tsuma,idan ya tashi magana ya yi tsawa,kuma mai iya keta mutuncinta a majalisa.

To ina baku shawara mai k**a da umarni...??

-Shareef Muhsan Bachirawa
08034318311
29/04/2026

Shehu Danfodiyo Musulunci Ya Yi Ba Fulatanci BaSarakunan ƙasar Hausa, da na Barno da na Nupe da yankunan Jukun da Shehu ...
21/04/2026

Shehu Danfodiyo Musulunci Ya Yi Ba Fulatanci Ba

Sarakunan ƙasar Hausa, da na Barno da na Nupe da yankunan Jukun da Shehu Usmanu ya kawar, tabbas da yawansu Musulmi ne. Kamar yadda yau su Tinubu, Buhari da Abacha da IBB da Shagari su ke Musulmi. Musulunci bai hana su cin amanar al'umma ba, Musulunci bai hana su shimfida zalunci da danniya ba, bai hana su sace dukiyar al'umma ba, bai hana su aikata miyagun ayyuka iri-iri ba. Ka na jin yau da Annabi (S) zai dawo cikinmu zai kyale su ne don su Musulmi ne?

Sarakunan da Shehu Usmanu ya samu sun fi waɗannan lallacewa sosai nesa ba kusa ba, wani zai yi mamaki ko? Waɗancan Sarakuna ba kawai sun lallace ba ne, sun daukar wa kansu matsayin Iyayengiji, wato su na ganin k**ar ma su ne su ka halicci al'ummarsu, ga shirka kala-kala da sunan sarauta, ga nau'ikan zalunci da ko kare ba zai ci ba. A wannan halin Shehu ya fara musu wa'azi ya na kiransu zuwa ga hanyar Allah, su watsar da dagutanci, su riƙe hanyar Allah, sai su ka fara yaƙar Shehu da sunan zai kwace musu mulki.

A lura Shehu fa ba zuwa ya yi daga duniyar wata ba, haifaffen ƙasar Gobir ne, in ma akwai wanda su ka zo toh ba Shehu ba ne, shi a nan Allah ya samar da shi, don haka Shehu ɗan ƙasar Hausa ne. Zuwan kakannin Shehu ƙasar Hausa ya fi shekara 400 kafin a haifi Shehu, don haka ba bako bane da ya taho daga wani waje don kwace mulkin ƙasar Hausa. Yadda waɗannan sarakunan su ke jin ƙasa tasu ce, haka Shehu ma ya ke da wannan haƙƙin na ƙasa, musamman ma mun san ƙasa ta Allah ce.

Ba Shehu ba ne ya fara yaƙar su, k**ar yadda na faɗa ayyukansu ya ke yaƙa, bayan su na da nasu mallaman da su ke tsarkake musu duk irin tsiyar da suke da sunan mulki. Sun sanya yaƙi da Shehu, Allah ya ɗaura Shehu a kansu, har ya yi nasara a kansu. Kamar yadda ba Annabi (S) ba ne ya fara yaƙar Kuraishawa, su ne su ka fara yaƙarsa daga ya na yaƙi da shirka da zaluncin da su ke yi. Allah ya ɗaura Annabi (S) kansu; bayan Annabi (S) sai mu ka samu makiya su na cewa da takobi Annabi (S) ya isar da Musulunci, bayan ba haka ba ne. Irinsa ake yi wa Shehu yanzu, Shehu da jama'arsa su na iya kuskure, amma ƙarya ne, ba irin wanda maƙiya ke faɗa ba ne.

Sannan Shehu ba sarauta ya yi ba sam, abin da aka kafa a bayan Shehu na sarauta, amma kuskuren magada ne, ba na Shehu ba, Shehu Mallami ne mai shiryar zuwa ga Allah, Shehu Sufi ne masanin Allah mai horo a bi Allah, sarakunan da ake ce musu na Fulani wanda su ka zo bayan Shehun su ne su ka maida al'amarin Sarauta, Shehu ba Sarki ba ne, babu wani waje da Shehu ya taɓa sarauta. Sarakunan nan za su iya zama jinin Shehu, amma a aikace ba magadan Shehu ba ne. Kamar yadda Banil Abbas da Banu Umayyah su ka kafa sarauta a da'irar Musulunci bayan Annabi (S) haka aka kafa ta bayan Shehu.

Bari na tsaya a nan, reactions ɗin ƴan addinin Hausa zai sa na ci gaba ko na dakata a haka.

“Baban Sayyida Asma'u wanda ta zam a cikin nuqaba'u, zuwa na yi na ƙurbi ma'u, na tafi a cikin Manzon Allah. Baba wajen Muhammadu Bello, Attijjaniyu Muhammadu Bello...” wakar Auwalu Gawuna.

–Haj Baqeer, al-Barnawy a asali.

TATSUNIYAR FIFIDALOFIFI-DALLOGa ta nan ga ta nan ku.Wata Bafulatana ce dai tana da dańta anakiransa Maigari. Mijinta kum...
11/04/2026

TATSUNIYAR FIFIDALO
FIFI-DALLO

Ga ta nan ga ta nan ku.
Wata Bafulatana ce dai tana da dańta ana
kiransa Maigari. Mijinta kuma ana kiransa Fifi-Dallo.

Kullum sai ta tatsi nonon saniyarsu ta dora wa ɗanta ya tafi talla.

Ana nan ana nan. Ran nan da ta kare tatsar nonon sal ta ce da shi, "To Maigari, sai ka tafi talla. Ka yi ƙoƙari ko ka sayar ka dawo da sauri."

Sai ya ce, ""ya ba ni da lafiya."
Sai ta cê dole ya tafi tallan nan. Shi kuma ya ce ba zai lya ba. Ta dai tilasta masa ya đauki nonon ya tafi yâna kuka.

Yana cikin tafiya a dokar daji kafin ya shiga
gari sai ajalinsa ya sauka. Sai ya fadi da kwaryar nonon nan ya mutu.
Shi ke nan sai wata tsuntsuWa ta zo za ta wuce ta gan shi a kwance. Da ta gan shi sai ta ce, Wannan lafiya kuwa?"
Sai ta sauka ƙasa.

Da ta sauka sai ta dudduba ta gani ba shi da rai. Sai ta ce a ranta, Lalle wannan kome aka yi đan gidan Fifi-Dallo ne.'

Sai ta tashi fir, ta je ta sauka a kan soron gidan su wannan yaron. Da saukarta sai ta ce:

Uwargidan Fifi-Dallo.
Uwargidan Fifi-Dallo.
Fifi-Dallo Maigari ya fadi.
Fifi-Dallo can a dokar daji
Fifi-Dallo har da rigar saƙi.
Fifi-Dallo har da wandon saƙi.
Fifi-Dallo har da hular saƙi.

Fifi-Dallo har da zobbansa bakwai.
Fifi-Dallo har da ƙwaryar nono.
Fifi-Dallo sai a je đauko shi.

Ashe ita Uwargidan Fifi-Dallo tana niƙa, ba ta san cewa tsuntsuwar nan da ita ta ke ba.

Sai ta bar niƙan ta kasa kunnenta.
Sai tsuntsuwar nan ta kuma cewa:

Uwargidan Fifi-Dallo.
Uwargidan Fifi-Dallo.
Fifi-Dallo Maigari ya fadi.
FIfi-Dallo can a dokar daji.
Fifi-Dallo har da rigar saki.
Fif-Dallo har da wandon sakl.
FIf-Dallo har da hular saƙi.
Fif-Dallo har da zobbansa bakwai,
Fif-Dallo har da ƙwaryar nono.
Fifi-Dallo sai a je dauko shi.
Da ta ji haka sai ta yi salati ta saka kuka.

Sai ta tafi da gudu ta nemo mijinta. Da
ta ga mijin nata sai ta ce da shi, Zo ka li
abin da tsuntsuwar nan ta ke fadi.
Sai shi ma mijin nata ya saurara ya ji abin da tsuntsuwar ta ke fada, ya fashe da kuka.
Tsuntsuwar ta ce, "Sai ku yi hakuri ku daina kuka,.".

Shi ke nan. Sai ya yi wa tsuntsuwar godiya. Ita ma matar ta yi godiya. Da s**a yi wa tsuntsuwar godiya, sai ita kuma tsuntsuwar ta yi musu gaisuwar ta'aziya sannan ta tashi abinta fir.

Shi ke nan. Sai Fifi-Dallo ya gayyaci mutane aka je aka dauko gawar Maigari a makara, aka kawo shi gida, aka yi masa wanka.

Bayan an gama yi masa wanka, kafin a kai shi a bunne, sai mutane s**a ce, "Da ma ba shi da lafiya ne ?"
So matar ta ce, "Ni dai na tatsar masa nono na ce ya je ya sayar.

Sai ya ce da ni ba shi da lafiya, Ni kuwa na ce dole sai ya tashi ya tafi. Na dai tilasta shi ya tafi tallan nar ba da son ransa ba. Yana kuka ma ya tafi. Yana cikin tafiya sai ya
gamu da ajalinsa a daji. Allah ne ya kai wata yar tsuntsuwa dajin ta gano gawar tasa."

Sai mijnta ya-ce, "Yo ke ashe da ma ya ce ba za shi ba kika tllasta masa don kin gani ba na nan?To yanzu ai ga shi nan kin rasa shi, ni ma na rasa shi.'"

Shi ke nan. Sai aka hada shi aka kai shi aka
bunne.

Sai ita ma ta dawo tana cewa, "Da na sani ai da. ban tilasta masa ya tafi tallan ba,"
Shi ke nan.
Kurunkus.

Bayani:
Me wannan labarin ya tuna muku na yarinta?

KARIN MAGANA GUDA DARI 1.A daga sama! An yi wa wada kwace.2.A dauki kare ran farauta?3.A dauri kashi ko a bata igiya?4.A...
11/02/2026

KARIN MAGANA GUDA DARI
1.
A daga sama! An yi wa wada kwace.
2.
A dauki kare ran farauta?
3.
A dauri kashi ko a bata igiya?
4.
A aiki kare ya aiki wutsiya?
5.
A amshi kadai ne, ba a ga mutuwa ba.
6.
A bakin tsoho ne, goro kan tsufa.
7.
A bakin wawa, akan ji magana.
8.
A bar dariyar mai noma, ko bai sayar ba, ya ci abinsa.
9.
A bar ganin allura kankanuwa,karfe ce.
10.
A bar kaza, cikin gashinta.
11.
A bari ya huce, shi kan kawo rabon wani.
12.
A ci a sha, a rage don gobe.
13.
A ci ba a sayar ba, kwai ya fi doki.
14.
A ci yau a ci gobe, shi ne ci.
15.
A cikin ido, ake tsawurya.
16.
A haifi da da samu, ya fi a mutu a bar masa gado.
17.
A ja mu a kai! An ba uwar makaho kashi.
18.
A kashe wuta, tun tana kankanuwa.
19.
A lallaba a kai ta, in ta fito muna so.
20.
A lokacin da mage na nan, bera ba ya wasa.
21.
A mari matacce, don mai rai ya ji tsoro.
22.
A nema a samu, arziki ne.
23.
A nuna wa na rigingine farin wata?
24.
A raba arne da makami.
25.
A rabe da alwalar kifi a ruwa?
26.
A rabe magirbin yakuwa, da na rama?
27.
A rabu a gana, arziki ne.
28.
A rama wa kura aniyarta.
29.
A rashin kira, karen bebe ya bata.
30.
A rashin kula, akan kade kudi.
31.
A rashin sani, bako ya sha ruwan wanka.
32.
A rika sara, ana duban bakin gatari.
33.
A sa a baka, ya fi a rataya.
34.
A san mutum, a san cinikinsa.
35.
A sayar a fadi, karin wayo.
36.
A shekara saran ruwa, sai tambatse.
37.
A so kare, har jelarsa.
38.
A so uwa, a so 'ya'yanta.
39.
A tauna tsakuwa, don aya ta ji tsoro.
40.
A taya Allah kiwo, ya fi Allah na nan.
41.
A yi a gama, ya fi gobe a karasa.
42.
A yi abin da za a yi! Mahaukaci ya dauki rigar kurma.
43.
A yi maza, a fidda jaki daga duma.
44.
A yi wadda za a yi! Bera ya zubda garin kyanwa.
45.
A zaba a gasa, ta hana yaro suna.
46.
A zuba wa ungulu kwan zabuwa?
47.
Abin kwarai ya saba bacewa an dangana, ba takalmi ba.
48.
Abin al'ajabi! Ango ya kwanada kunzugu.
49.
Abin aljihu, na mai riga ne.
50.
Abin Allah! Budurwa da ciki; gwauro da yaye.
51.
Abin Allah! Budurwa da jika.
52.
Abin Allah, na Annabi ne.
53.
Abin aro, ba ya ado.
54.
Abin aro, bai rufe katara.
55.
Abin ba zai yiyu ba, auren mage da bera.
56.
Abin ba'a ne? An ce da kare mai sunan maza.
57.
Abin banza, hanci ba kafa.
58.
Abin biki, na biki ne.
59.
Abin cikin kwai, ya fi kwai dadi.
60.
Abin da aka gasa, shi ya ga wuta.
61.
Abin da aka shuka, shi yake tsira.
62.
Abin da Allah ya yi, Annabi sai ceto.
63.
Abin da babba ya gani daga zaune, yaro ko ya hau rimi ba zai linkaye shi ba.
64.
Abin da baki ya daura, hannubai iya kwancewa.
65.
Abin da dama ta jure, hagun ba ta jure ba.
66.
Abin da k**ar wuya! Gurguwa da aure nesa.
67.
Abin da ke ga amarya, shi takan ba ango.
68.
Abin da ke gidan Sarki, akwai shi a kasuwa.68.
Abin da ke gidan Sarki, akwai shi a kasuwa.
69.
Abin da kunya, uwar 'ya ta cinye suruki ran aure.
70.
Abin da mutum ya shuka, shizai girba.
71.
Abin da ruwan zafi ya dafa, in aka hakura ruwan sanyi ma ya dafa.
72.
Abin da wancan ya ce shi na ce! Kirarin mai tsoro.
73.
Abin da ya ba ka tsoro, wataran shi zai ba ka tausayi.
74.
Abin da ya ci Doma, ba ya barin Awai.
75.
Abin da ya ci ungulu, ba ya barin shaho.
76.
Abin da ya dami mutum, da shi yake mafarki.
77.
Abin da ya kewaye gida, gidan zai shiga.
78.
Abin da ya kora bera wuta, ya fi wutar zafi.
79.
Abin da ya taba hanci, ido saiya yi ruwa.
80.
Abin da ya zo, shi ake yayi.
81.
Abin daga Allah yake! Matar takaba ta yi ciki.
82.
Abin dariya! Yara sun tsinci hakori.
83.
Abin duniya mene ne? Kaza ta jawo muzuru kwanan gida.
84.
Abin duniya mene ne? Sarkinfawa da kyautar kaho.
85.
Abin fada, na mai baki ne.
86.
Abin majinyaci, na mai magani ne.
87.
Abin mamaki! Ciyawa da cin doki.
88.
Abin mamaki! Kare da tallan tsire.
89.
Abin mamaki! Kurege da fada wa zomo dadin kanzo.
90.
Abin mutum, abin wasansa.
91.
Abin na yi ne! An biya wa zawara hajji.
92.
Abin nema ya samu! Matar falke ta haifi jaki.
93.
Abin sai ido! Bebiya ta auri makadi.
94.
Abin shanya, ba a hana rana.
95.
Abin su na 'yan dangi, bare ina ruwanka?
96.
Abin tsana! Amarya a kan kare.
97.
Abin tsoro! Kura a rumbu.
98.
Abin wani da wuya, ne

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu. posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Practice

Send a message to Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu.:

Share