Sheikh Alqasim Umar Jibrin Hotoro

Sheikh Alqasim Umar Jibrin Hotoro Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Sheikh Alqasim Umar Jibrin Hotoro, Hotoro kano, Kano.

This is an Official Facebook Fans Page of Sheikh AlQasim Umar Jibrin Hotoro

Guide people to Islam through the authentic sources of the Quran and Sunnah in a contemporary way with the understanding of the righteous predecessors

*ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH*Muna farin cikin sanar da ษ—aukacin Al'ummar Musulmi cewa insha Allahu daga yau litinin 3...
31/01/2022

*ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH*

Muna farin cikin sanar da ษ—aukacin Al'ummar Musulmi cewa insha Allahu daga yau litinin 31/01/2022 za'a fara saka karatun Littafin Muwadda Malik na Dr Ahmad BUK (Rahimahullah) a Rahma Radio Dake Kano Insha Allahu.

Ranakun da za'a ke sakawa sune:

๐Ÿ‘‰. Ranar Litinin-Jumaยดa Karfe 9:00 na dare

๐Ÿ‘‰ Asabar da Lahadi 9:00 na safe bayan shirin Fatawoyin Rahma

Allah yasa mu amfana da abun da zamu Saurara.

Allah ya gafartawa malam yasa jannatul firdaus itace makomarsa Ameen.

05/03/2021

Wannan Tasha Ta Alheri Hausa Tv Zata Rika Kawo Muku Shirye Shirye Masu kayatarwa Da Nishadantarwa Da kuma ilmantarwa ...

Assalamu alaikum Warahmatullah.Daga Gobe Asabar 2 Ramadan 1441 = 25 April 2020 Malamin mu Dr. Muhammad Sani Umar R/Lemo ...
24/04/2020

Assalamu alaikum Warahmatullah.

Daga Gobe Asabar 2 Ramadan 1441 = 25 April 2020 Malamin mu Dr. Muhammad Sani Umar R/Lemo zai fara gabatar da Tafsirin Ramadan na wannan Shekara amma ta kafar sadarwa ta Fcbk, a Shafin sa Mai suna: Dr. Muhd Sani Umar R/Lemo.

Kullum da Misalin Qarfe 5:00pm na Kwanakin Azumi insha'Allah.

Sannan zaku iya sauraro ta Kafafen sadarwa kamar haka.
1. SUNNAH TV 10:00pm

2. NTA KANO 10:00pm Daukar nauyi SHENZEN GOLBAL SERVICES.

3. AMINCHI FM 103.9 Kano 6:00am Daukar nauyi Alh. Kabiru Hassan Sugungu tare da Hadin Gwuiwar Sautul Haq.

4. RAHMA FM 97.3 Kano 9:00am Daukar nauyi Sautul Haq.

5. PYRAMID FM 103.5 Kano 11:00am Daukar nauyi Sautul Haq.

6. EXPRESS FM 90.3 Kano 4:30pm Daukar nauyi Alh. Muhammad Adamu Alqali.

7. GUARANTEE FM Kano 94.7 10:00pm SHENZHEN GLOBAL SERVICES.

8. GLOBE FM Bauchi 98.5 11:00am

9. BRC FM TORO 89.1 BAUCHI 2:00pm Daukar nauyi Iyalan Marigayi Alh. Adamu Garkuwa Toro.

10. NAGARTA RADIO KADUNA 10:00pm, Daukar nauyi SHENZEN GOLBAL SERVICES.

11. BRTV 95.3 MAIDUGURI 2:00pm, Daukar nauyi DAGIRA ALTERNATIVE HEALTH CARE.

12. DANDAL KURA FM 98.9 MAIDUGURI 4:00pm, Daukar nauyi DAGIRA ALTERNATIVE HEALTH CARE.

13. COMPANION FM 104.5 KATSINA 10:00pm, Daukar nauyi SHENZEN GOLBAL SERVICES.

14. GARKUWA FM SOKOTO 10:00pm, Daukar nauyi SHENZEN GOLBAL SERVICES.

15. NAGARTA FM MARADI.

16. ALHERI FM MARADI.

17. ZAMZAM FM TASAWA 8:00am, Daukar nauyi Alh. Rabu Isa Sheda.

18. RADION JIHAR ZAMFARA 7:30pm, Daukar nauyi Alh. Abubakar Aliyu Dan Madamin Maradun.

Zuwa wannan Lokaci abinda muka kammala tattarawa kenan, insha'Allah zaku ji ragowar da zarar komai ya Kammala.

Allah yasa muyi Ibada Kar6a66iya, Allah ya yaye mana wannan Annoba, Allah ya qarawa Malam lfy da Nisan kwana.

Sanarwa daga PRO Sautul Haq

11/11/2019

Macijiya ce ta shiga shagon kafinta, tana kutsawa sannu a hankali, cikin rashin lura sai ta yi tuntube da zarto, wanda hakan ya ja sanadiyyar da wannan zarton ya dan karceta,

cikin bacin rai Macijiya ta juyo, ta kaiwa wannan zarto sara, wanda hakan ya yi sanadiyyar fitan jini a bakin Macijiya, kokarin neman daukar fansa, ya sa wannan Macijiya ta nannaษ—e wannan zarton da nufin ta yi mika don ta karairaya shi, sai dai kuma kash! hakan ya yi sanadiyyar rasa rayuwarta ba tare da wannan zarto ya ji koda kwarzane ba.

๐ŸŒบ Jan hankali: so da yawa mukan yi saurin fushi da kokarin hanzarin daukar fansa, hatta akan wanda ya saba mana cikin kuskure, kuma mu dage akan sai mun dau fansa, wanda da yawa hakan kan sanya ฦ™aiฦ™ayi ya koma kan mashekiya.

# Ba a kan komai ake daukar fansa ba, kamar yadda saurin fishi kan sanya muguwar madama.

Ya kamata hukumar BBC Hausa ta binciki ma'aikatanta!Imma dai akwai 'yan shi'a a BBC kuma suna anfani da BBC don yada shi...
06/08/2019

Ya kamata hukumar BBC Hausa ta binciki ma'aikatanta!

Imma dai akwai 'yan shi'a a BBC kuma suna anfani da BBC don yada shi'ancinsu ko suna gefe suna kitsa hakan, ko kuma rashin sanin makamar aiki ya fara yawa a BBC. Ko ma ya ne, hakan zai watsa suna da nagartar da BBCn ta gina tsawon shekara-da-shekaru.

A kwanaki can BBC ta yi labarin gidan yi wa hadisan Manzo SAW hidima na Saudiya a gurbatance, ta kwaso labarin da 'yan shi'a suke yadawa a kan Saudiyyan na qarya, ta tattauna da wani malami maqiyin Saudiyya kan Saudiyyar ta na yaye 'yan ta'adda ba tare da sun yi balancing ba.

A makon da ya gabata, s**a je Wikipedia su ka kwaso labarin da 'yan shi'a su ka qaga a na qarya wai Muhammad Yusuf ya yi karatu a Jami'ar Madina, alhalin qarya ne, ko a Wikipedia din ma ba source.

Yanzu kuma Kotu ta ba wa jagoran 'yan shi'a izinin zuwa Indiya don a duba tunbinsa da sauran sassan jikinsa da na matarsa, sai ga BBC sun buga labarin qarya wai mutanen Indiya sun fara maraba da Zakzakiy (https://www.bbc.com/hausa/labarai-49240955?ocid=wshausa.chat-apps.in-app-msg.whatsapp.trial.link1_.auin).

Abin takaici shi ne, wai fa madogarar BBC ita ce wani mutum daya jal dan shi'a, wai shi Hashmi, ya yi twitting cewa Indiya na maraba da Zakzakiy. Mutumin nan ba wani sananne bane, duka-duka fa a watan March din nan da ya wuce ne ya yi joining Twitter, followers dinsa 11 ne kacal, haka ma yawan "like" da aka yi wa labarin nasa, retwit 2 qwal, amma wai a kan haka ne har BBC za su buga dogon labarin cewa wai 'yan Indiya sun fara maraba da Zakzakiy.

Sannan a labarin sai s**a ce:

"Daya daga cikin sharuddan shi ne dole ne jami'an gwamnati su yi wa Zakzaky da matarsa rakiya zuwa Indiya."

Abin da za a fahimta anan shi ne kotun ta martaba Zakzakiy da matarsa don ta bada umarnin dole jami'an gwamnati su yi musu rakiya. Wannan ba gaskiya bane, domin kotun cewa ta yi:

"...under the strict supervision of the respondent and to return to Nigeria (for continuation of trial)"

Wato ta bada izini Zakzakiy ya je Indiya amma qarqashin sa idon qud-da-qud na Gwamnati kuma da ya gama dole ne ya dawo a dora daga inda aka tsaya. Gwargwadon umarnin na kotu fa in ma Zakzakiy ya dawo to za a garqame shi, ba wai ta bada belinsa bane.

Sannan sai BBC su ka shiga sharhin nuna kamar akwai wata alaqar qauna tsakanin Zakzakiy da Indiyawa amma duk sai su ka qare a labarin da Wikipedia ta wallafa, shi ma marar tushe. BBC ta ce:

"...kasar India na daya daga cikin kasashen da ba na Musulmi ba, amma masu yawan mabiya mazhabar Shi'a a duniya, inda bayanai s**a ce akwai 'yan Shi'a da dama a Musulman kasar."

Ga kuma rubutun Wikipedia:

"India, the only non-Muslim nation in the world with Shiite population of 2โ€“3 percent of its entire population"

Don Allah wannan ba wanki bane kai tsaye? To shi kuma rubutun na Wikipedia ba shi da tushe, ga shi: https://en.m.wikipedia.org/wiki/Shia_Islam_in_India

To a hakan ma, ai Wikipedia cewa su ka yi 'yan shi'ar na Indiya 2-3% ne, kuma a hakan ba wai iya irin 'yan shi'ar Zakzakiy bane 2% din, a'a suna da yawa brijik ciki har da jama'ar su Shaikh Hamza Lawal da Saleh Zaria.

An yi qididdigar yawan jama'ar Indiya a karo na 15 a 2011, mutanen indiya 1,210,854,977 ne (http://www.census2011.co.in). Musulmi ne na biyu a yawa bayan addinin Hindu da kashi 14.2% (http://www.census2011.co.in/religion.php)

Ida ka ja lissafi, mutum 1,210,854,977 รท 100 x 14.2 zai baka kusan Musulmi 169,761,868 a Indiya. Su kuma 'yan shi'ar, idan ma an yarda da lissafin na Wikipedia, shin 2% na jama'ar qasar har ya kai adadin da zuwan Zakzakiy zai zama wani batun tattaunawa?

Gaskiya ban ga abin da BBC za su fada na gamsu ba shi'anci su ke tallatawa ba. Sun dora BBC a tafarkin watsa ta. Muna kira, kuma za mu bi matakan hurawa hukumar BBC wuta don ta gaggauta bincika lamarin nan ta dauki matakan da su ka kamata.

Allah ya kyauta.

*BBC HAUSA: GANGANCI KO RASHIN KWAREWA?*โœ’ Mansur Sokoto30 ga July, 2019Akwai mamaki matuka irin yadda tashar BBC Hausa R...
30/07/2019

*BBC HAUSA: GANGANCI KO RASHIN KWAREWA?*
โœ’ Mansur Sokoto
30 ga July, 2019

Akwai mamaki matuka irin yadda tashar BBC Hausa Radio ta wallafa tarihin jagoran Boko Haram Muhammad Yusuf jiya a shafinta, bayan ya cika shekaru 10 da mutuwa tare da alakanta shi da Jami'ar Musulunci ta Madina.
Wannan ba zai yiwu ya zama kuskure ba. Musamman in muka yi la'akari da yadda a cikin rahoton s**a yi biris da kasancewarsa jagoran Zakzakiyya na jihar Yobe kafin ya rungumi kungiyar Tajdid, sannan ya sauya sheka daga baya zuwa abinda aka kira Salafiyya, da kuma yadda BBCn s**a fito da sunan Ibnu Taimiyyah baro baro a matsayin wanda Muhammad Yusuf yake da'awar koyi da shi. Amma abin tambaya shi ne: Don wace manufa s**a yi haka?
To, ko don mine ne dai muna sanar da su cewa, al'ummar kasar Hausa ta ga alheran wadanda wannan Jami'a mai albarka ta yaye a tsawon kusan shekaru 60 da ta yi tana hidimar karantar da yayan Musulmin duniya sahihin karatun addinin Musulunci kyauta. Kuma _alhamdu lillahi_ ba a san dan ta'adda ko daya wanda ita wannan Jami'ar ce ta kyankyashe shi ba. Muhammad Yusuf kuma ko bangon Jami'ar bai taba gani ba.
*Makaryaci ba shi zama gwani kowane ne.*

Abubuwa 15 Gameda Shugaba Muhammad Mursi..1- An haifi Mursi a jihar Sharqiyya a Masar a shekarar 1951 ya rasu 2019 (shek...
18/06/2019

Abubuwa 15 Gameda Shugaba Muhammad Mursi..

1- An haifi Mursi a jihar Sharqiyya a Masar a shekarar 1951 ya rasu 2019 (shekaru 68). Ya na da mata daya da 'ya'ya biyar, maza hudu mace daya.

2- yayi digiri na farko a fannin Engineering a shekarar (1975), da na biyu a shekarar (1978) a kan Metals Engineering duk a Jami'ar Alkahira (Cairo University).

3- Ya tafi Amurka inda ya yi digirinsa na uku a Jami'ar (Southern California University) a shekarar 1982, inda ya karantar a Jami'ar har zuwa shekarar 1985

4- Bayan dawowarsa ya karantar a Jami'ar Zaqaziq a Masar daga shekarar 1985 zuwa 2010. , inda ya rike bangaren (Materials Engineering) a Jami'ar.

5- Ya shiga cikin kungiyar 'Yan'uwa Musulmi a shekarar 1977 inda ya rike makamai da dama a cikin kungiyar.

6- Mursi ya cigaba da gwagwarmayar siyasa, inda ya yi takara lokuta da dama a matakin majalisa ta kasa. ya zama dan majalisa a shekarar 2000.

7- Kungiyarsa ta 'Yan'uwa Musulmi ta tsaida shi a matsayin dan takarar matakin shugaban kasa, inda aka kara tsakanin manyan yan takara guda biyar a kasar bayan boren da ya yi awon gaba da shugaba Muhammad Husni Mubarak a shekarar 2011

8- Mursi ya ci nasarar zama shugaban kasa na farko bayan lashe zaben da ya yi da kashi 52% a kan babban abokin hamayyarsa Ahmad Shafiq a shekarar 2012 , a zaben da ya zamto mafi tsafta a tarihin Masar.

9- Ministan tsaron da ya nada Abdulfattah al-Sisi ya yi awon gaba da shi bayan zanga-zangar da 'yan adawa da shi musamman (secularists) su ka yi akan dole ya sauka ya shirya wani zaben cikin gaugawa su na masu zarginsa da kokarin cusa musulunci a tsarin gwamnatinsa da karawa Kansa karfin iko.

10- Sisi wanda ya samu cikakken goyon baya daga wadansu daga cikin gwamnatocin kasashen waje na larabawa da da Isra'ila ya yi amfani da damar wajen shirya juyin mulki ga shugaba Mursi a shekarar 2013

11- Magoya bayan Mursi sun cigaba da gudanar da zanga-zangar lumana ta nuna rashin amincewarsu da juyin mulkin da Sisi ya yi wa zababben shugabansu, kuma ya ke cigaba da tsare shi, tareda wadansu dubban magoya bayansa, da kashe wasu, da tilastawa da dama daga cikinsu yin gudun hijira zuwa kasashen ketare. Sisi ya aiwatar da kisan kiyashi ga magoya bayan Mursi, wanda mafi muni shine kisan da sojoji su ka yi wa magoya bayan Mursi mutum 2000+ da su ka taru su ka yi zaman dirshen a dandalin Rabia da ke Nasr city a cikin birnin Alkahira.

12- A shekara daya da yayi yana mulki, Mursi ya samu kauna ta ban mamaki daga al'ummar larabawa da sauran musulman duniya, wanda su ke ma kallon jagoran da zai dawo musu da kimarsu a duniya, musamman yanda ya ke nuna damuwarshi da al'ummar musulmi da yadda ya ke nuna goyon bayan shi ga mutanen Palastinu da Zirin Gaza.

13- A daya daga cikin zqman da aka yi bayan gabatar da shi a kotu, Mursi ya bayyanawa kotu cewa rayuwarshi na cikin hatsari, amma ba a dau wani mataki ba.

14- Gidan talabijin din Masar ya sanar a ranar litinin 17/6/2019 cewa Mursi ya rasu a kotu yayin da ake masa shari'a , amma wasu na ganin wannan shiri ne kawai na boye hakikanin dalilin rasuwarshi, musamman da ya ke an hanashi magani a kurkuku.

15- Dr. Muhammad Mursi cikakken mahaddaci Alkur'ani ne mai kishin addininsa da al'ummarsa, wanda ke kokarin baiwa al'ummarsa da addinin sa kariya duk inda ya samu kansa kuma ya Samu dama.

Muhammad Mursi daya ne daga cikin miliyoyin musulmai a duniya da ke gwagwarmayar dawowa al'umma da karfinta da izzarta ta kowane bangare, kuma su ke bada jinanensu a matsayin farashin wannan aiki, kuma ba za su taba juya baya ba har sai hasken Allah ya cika.

Allahu Akbar Allah ya yi gaskiya:

"ู…ู† ุงู„ู…ุคู…ู†ูŠู† ุฑุฌุงู„ ุตุฏู‚ูˆุง ู…ุง ุนุงู‡ุฏูˆุง ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ ูู…ู†ู‡ู… ู…ู† ู‚ุถู‰ ู†ุญุจู‡ ูˆู…ู†ู‡ู… ู…ู† ูŠู†ุชุธุฑ ูˆู…ุง ุจุฏู„ูˆุง ุชุจุฏูŠู„ุง"

Mu na yi wa al'ummar musulmin duniya ta'aziyya na rasuwar wannan babban gwarzo wanda ya bada rayuwarsa domin hidimtawa al'ummarsa da addininsa. Ya Allah ka jikansa ka gafarta masa ka karbi shahadarsa ka sanya jininsa ya zamto la'ana ga makasansa.

Umar Mansur
umarmansur47@gmail.com
17/6/2019

30/08/2018

DALILIN DA YA SA ANNABI (SAW) YA YI HU'DUBA A GHADEER KHUM!!!

LALLAI YA TABBATA ANNABI (SAW) YA TSAYA A WANI WURI DA AKE KIRANSA "GHADEER KHUM" A KAN HANYARSA TA KOMAWA GIDA MADINA DAGA MAKKA, BAYAN GAMA HAJJINSA NA BAN-KWANA, ANNABI (SAW) TARE DA SAHABBANSA, YA YI ZANGO NE A WANNAN WURI SABODA DOGUWAR TAFIYA IRIN TA WANCAN LOKACI TA GAJI YA DA ZANGO, SABODA TAFIYA CE DA AKE YINTA A CIKIN KWANAKI KO MAKONNI.

LALLAI MALAMAN HADISI SUN RUWAITO RIWAYOYI MASU YAWA GAME DA ABIN DA YA FARU A "GADEER KHUM", AMMA MAFI YAWA BA SU INGANTA BA, MUSAMMAN SABODA MAK'ARYATA DA 'YAN BIDI'A DA SON RAI SUN YI WASA DA WA'DANNAN RIWAYOYI DON CUSA MUNANAN AQIDUNSU DA BIDI'O'INSU, AMMA โ€“ ALHAMDU LILLAHI -, CIKIN IKON ALLAH, ALLAH YA TANADI MALAMAN HADISI MASU TANKA'DE DA RERAYA, INDA S**A TANKA'DE ABIN DA YA INGANTA, DAGA RIWAYOYIN MAK'ARYATA DA GUR'BATATTUN MARUWAITA.

INGANTACCEN NASSIN HADISIN GADEER KHUM:

(1) IMAMU MUSLIM YA RUWAITO A CIKIN SAHIHINSA YA CE :
6378 - ุญุฏุซู†ู‰ ุฒู‡ูŠุฑ ุจู† ุญุฑุจ ูˆุดุฌุงุน ุจู† ู…ุฎู„ุฏ ุฌู…ูŠุนุง ุนู† ุงุจู† ุนู„ูŠุฉ ู‚ุงู„ ุฒู‡ูŠุฑ ุญุฏุซู†ุง ุฅุณู…ุงุนูŠู„ ุจู† ุฅุจุฑุงู‡ูŠู… ุญุฏุซู†ู‰ ุฃุจูˆ ุญูŠุงู† ุญุฏุซู†ู‰ ูŠุฒูŠุฏ ุจู† ุญูŠุงู† ู‚ุงู„ ุงู†ุทู„ู‚ุช ุฃู†ุง ูˆุญุตูŠู† ุจู† ุณุจุฑุฉ ูˆุนู…ุฑ ุจู† ู…ุณู„ู… ุฅู„ู‰ ุฒูŠุฏ ุจู† ุฃุฑู‚ู… ูู„ู…ุง ุฌู„ุณู†ุง ุฅู„ูŠู‡ ู‚ุงู„ ู„ู‡ ุญุตูŠู† ู„ู‚ุฏ ู„ู‚ูŠุช ูŠุง ุฒูŠุฏ ุฎูŠุฑุง ูƒุซูŠุฑุง ุฑุฃูŠุช ุฑุณูˆู„ ุงู„ู„ู‡ -ุตู„ู‰ ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ ูˆุณู„ู…- ูˆุณู…ุนุช ุญุฏูŠุซู‡ ูˆุบุฒูˆุช ู…ุนู‡ ูˆุตู„ูŠุช ุฎู„ูู‡ ู„ู‚ุฏ ู„ู‚ูŠุช ูŠุง ุฒูŠุฏ ุฎูŠุฑุง ูƒุซูŠุฑุง ุญุฏุซู†ุง ูŠุง ุฒูŠุฏ ู…ุง ุณู…ุนุช ู…ู† ุฑุณูˆู„ ุงู„ู„ู‡ -ุตู„ู‰ ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ ูˆุณู„ู…- - ู‚ุงู„ - ูŠุง ุงุจู† ุฃุฎู‰ ูˆุงู„ู„ู‡ ู„ู‚ุฏ ูƒุจุฑุช ุณู†ู‰ ูˆู‚ุฏู… ุนู‡ุฏู‰ ูˆู†ุณูŠุช ุจุนุถ ุงู„ุฐู‰ ูƒู†ุช ุฃุนู‰ ู…ู† ุฑุณูˆู„ ุงู„ู„ู‡ -ุตู„ู‰ ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ ูˆุณู„ู…- ูู…ุง ุญุฏุซุชูƒู… ูุงู‚ุจู„ูˆุง ูˆู…ุง ู„ุง ูู„ุง ุชูƒู„ููˆู†ูŠู‡.
ุซู… ู‚ุงู„ ู‚ุงู… ุฑุณูˆู„ ุงู„ู„ู‡ -ุตู„ู‰ ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ ูˆุณู„ู…- ูŠูˆู…ุง ููŠู†ุง ุฎุทูŠุจุง ุจู…ุงุก ูŠุฏุนู‰ ุฎู…ุง ุจูŠู† ู…ูƒุฉ ูˆุงู„ู…ุฏูŠู†ุฉ ูุญู…ุฏ ุงู„ู„ู‡ ูˆุฃุซู†ู‰ ุนู„ูŠู‡ ูˆูˆุนุธ ูˆุฐูƒุฑ ุซู… ู‚ุงู„ ยซ ุฃู…ุง ุจุนุฏ ุฃู„ุง ุฃูŠู‡ุง ุงู„ู†ุงุณ ูุฅู†ู…ุง ุฃู†ุง ุจุดุฑ ูŠูˆุดูƒ ุฃู† ูŠุฃุชู‰ ุฑุณูˆู„ ุฑุจู‰ ูุฃุฌูŠุจ ูˆุฃู†ุง ุชุงุฑูƒ ููŠูƒู… ุซู‚ู„ูŠู† ุฃูˆู„ู‡ู…ุง ูƒุชุงุจ ุงู„ู„ู‡ ููŠู‡ ุงู„ู‡ุฏู‰ ูˆุงู„ู†ูˆุฑ ูุฎุฐูˆุง ุจูƒุชุงุจ ุงู„ู„ู‡ ูˆุงุณุชู…ุณูƒูˆุง ุจู‡ ยป. ูุญุซ ุนู„ู‰ ูƒุชุงุจ ุงู„ู„ู‡ ูˆุฑุบุจ ููŠู‡ ุซู… ู‚ุงู„ ยซ ูˆุฃู‡ู„ ุจูŠุชู‰ ุฃุฐูƒุฑูƒู… ุงู„ู„ู‡ ูู‰ ุฃู‡ู„ ุจูŠุชู‰ ุฃุฐูƒุฑูƒู… ุงู„ู„ู‡ ูู‰ ุฃู‡ู„ ุจูŠุชู‰ ุฃุฐูƒุฑูƒู… ุงู„ู„ู‡ ูู‰ ุฃู‡ู„ ุจูŠุชู‰ ยป. ูู‚ุงู„ ู„ู‡ ุญุตูŠู† ูˆู…ู† ุฃู‡ู„ ุจูŠุชู‡ ูŠุง ุฒูŠุฏ ุฃู„ูŠุณ ู†ุณุงุคู‡ ู…ู† ุฃู‡ู„ ุจูŠุชู‡ ู‚ุงู„ ู†ุณุงุคู‡ ู…ู† ุฃู‡ู„ ุจูŠุชู‡ ูˆู„ูƒู† ุฃู‡ู„ ุจูŠุชู‡ ู…ู† ุญุฑู… ุงู„ุตุฏู‚ุฉ ุจุนุฏู‡. ู‚ุงู„ ูˆู…ู† ู‡ู… ู‚ุงู„ ู‡ู… ุขู„ ุนู„ู‰ ูˆุขู„ ุนู‚ูŠู„ ูˆุขู„ ุฌุนูุฑ ูˆุขู„ ุนุจุงุณ . ู‚ุงู„ ูƒู„ ู‡ุคู„ุงุก ุญุฑู… ุงู„ุตุฏู‚ุฉ ู‚ุงู„ ู†ุนู…

MUSLIM YA RUWAITO DAGA ZAIDU BN ARQAM (RA) YA CE:
"WATA RANA ANNABI (SAW) YA TSAYA A CIKINMU YANA MAI HU'DUBA A WANI RUWA (KWARIN RUWA), ANA KIRANSA "KHUMMUN", WANDA YAKE TSAKANIN MAKKA DA MADINA, SAI YA YI GODIYA MA ALLAH, YA YI MASA YABO, SAI YA YI WA'AZI YA TUNATAR DA MUTANE, SA'ANNAN SAI YA CE:
"BAYAN HAKA: KU SAURARA YA KU MUTANE, LALLAI NI MUTUM NE, KUMA 'DAN AIKEN UBANGIJINKU YA YI KUSA YA ZO GARE NI, NI KUMA IN AMSA MASA, LALLAI ZAN BAR WASU ABUBUWA MASU NAUYI GUDA BIYU A CIKINKU, NA FARKONSU SHI NE LITTAFIN ALLAH, LALLAI AKWAI SHIRIYA DA HASKE A CIKINSA, DON HAKA KU K**A LITTAFIN ALLAH, KUMA KU YI RIK'O DA SHI".
SAI YA ZABURAR A KAN LITTAFIN ALLAH, KUMA KWA'DAITAR A KANSA, SAI YA CE:
"SAI KUMA IYALAN GIDANA, INA TUNA MUKU ALLAH A KAN IYALAN GIDANA, INA TUNA MUKU ALLAH A KAN IYALAN GIDANA, INA TUNA MUKU ALLAH A KAN IYALAN GIDANA".

SAI HUSWAIN YA CE: SU WANENE IYALAN GIDAN NASA YA ZAID, SHIN MATANSA BA IYALAN GIDANSA BA NE?
SAI YA CE: MATANSA SUNA CIKIN IYALAN GIDANSA, AMMA IYALAN GIDANSA (DA AKE NUFI A NAN) SU NE WA'DANDA AKA HARAMTA MASU CIN SADAKA A BAYANSA.
SAI YA CE: SU WANENE SU?
SAI YA CE: SU NE; IYALAN ALIYU, DA IYALAN AQILU, DA IYALAN JA'AFAR, DA IYALAN ABBAS.
SAI YA CE: DUKA WA'DANNAN AN HARAMTA MUSU CIN SADAKA?
SAI YA CE: EH".

(2) AL- IMAMU AHMAD YA RUWAITO A CIKIN AL- MUSNAD:
641 - ุญุฏุซู†ุง ุงุจู† ู†ู…ูŠุฑุŒ ุญุฏุซู†ุง ุนุจุฏ ุงู„ู…ู„ูƒุŒ ุนู† ุฃุจูŠ ุนุจุฏ ุงู„ุฑุญูŠู… ุงู„ูƒู†ุฏูŠุŒ ุนู† ุฒุงุฐุงู† ุฃุจูŠ ุนู…ุฑุŒ ู‚ุงู„: ุณู…ุนุช ุนู„ูŠุงุŒ ููŠ ุงู„ุฑุญุจุฉ ูˆู‡ูˆ ูŠู†ุดุฏ ุงู„ู†ุงุณ: ู…ู† ุดู‡ุฏ ุฑุณูˆู„ ุงู„ู„ู‡ ุตู„ู‰ ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ ูˆุณู„ู… ูŠูˆู… ุบุฏูŠุฑ ุฎู…ุŒ ูˆู‡ูˆ ูŠู‚ูˆู„ ู…ุง ู‚ุงู„ ุŸ ูู‚ุงู… ุซู„ุงุซุฉ ุนุดุฑ ุฑุฌู„ุงุŒ ูุดู‡ุฏูˆุง ุฃู†ู‡ู… ุณู…ุนูˆุง ุฑุณูˆู„ ุงู„ู„ู‡ ุตู„ู‰ ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ ูˆุณู„ู… ูˆู‡ูˆ ูŠู‚ูˆู„: " ู…ู† ูƒู†ุช ู…ูˆู„ุงู‡ ูุนู„ูŠ ู…ูˆู„ุงู‡ "

IMAMU AHMAD YA RUWAITO TA HANYAR ZAZAN YA CE: NA JI ALIYU (RA) A RAHABA (WANI WURI NE A GARIN KUFA), YANA MAGIYA WA MUTANE:
"WANENE YA HALARCI LOKACIN DA MANZON ALLAH YAKE FA'DIN ABIN DA YA FA'DA A RANAR GADEER KHUM?
SAI MUTANE GOMA SHA UKU (13) S**A TASHI, SAI S**A BA DA SHAIDAN CEWA; SUN JI MANZON ALLAH (SAW) YANA CEWA:
"DUK WANDA NA KASANCE MASOYINSA NE, TO ALIYU MA MASOYINSA NE".
WANNAN HADISIN HASAN NE.

(3) AL- IMAMU AL - TIRMIZIY YA RUWAITO A CIKIN SUNAN NASA, DA 'DABARANIY A CIKIN AL- KABEER:
3713- ุญุฏุซู†ุง ู…ุญู…ุฏ ุจู† ุจุดุงุฑ ุŒ ู‚ุงู„ : ุญุฏุซู†ุง ู…ุญู…ุฏ ุจู† ุฌุนูุฑ ุŒ ู‚ุงู„ : ุญุฏุซู†ุง ุดุนุจุฉ ุŒ ุนู† ุณู„ู…ุฉ ุจู† ูƒู‡ูŠู„ ุŒ ู‚ุงู„ : ุณู…ุนุช ุฃุจุง ุงู„ุทููŠู„ ูŠุญุฏุซ ุŒ ุนู† ุฃุจูŠ ุณุฑูŠุญุฉ ุŒ ุฃูˆ ุฒูŠุฏ ุจู† ุฃุฑู‚ู… ุŒ ุดูƒ ุดุนุจุฉ ุŒ ุนู† ุงู„ู†ุจูŠ ุตู„ู‰ ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ ูˆุณู„ู… ู‚ุงู„ : ู…ู† ูƒู†ุช ู…ูˆู„ุงู‡ ูุนู„ูŠ ู…ูˆู„ุงู‡.
ู‡ุฐุง ุญุฏูŠุซ ุญุณู† ุบุฑูŠุจ.
ูˆู‚ุฏ ุฑูˆู‰ ุดุนุจุฉ ุŒ ู‡ุฐุง ุงู„ุญุฏูŠุซ ุŒ ุนู† ู…ูŠู…ูˆู† ุฃุจูŠ ุนุจุฏ ุงู„ู„ู‡ ุŒ ุนู† ุฒูŠุฏ ุจู† ุฃุฑู‚ู… ุŒ ุนู† ุงู„ู†ุจูŠ ุตู„ู‰ ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ ูˆุณู„ู… ู†ุญูˆู‡.
ูˆุฃุจูˆ ุณุฑูŠุญุฉ ู‡ูˆ : ุญุฐูŠูุฉ ุจู† ุฃุณูŠุฏ ุตุงุญุจ ุงู„ู†ุจูŠ ุตู„ู‰ ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ ูˆุณู„ู….

DAGA ZAIDU BN ARQAM (RA), DAGA ANNABI (SAW) YA CE:
"DUK WANDA NA KASANCE MASOYINSA NE, TO ALIYU MA MASOYINSA NE".
WANNAN HADISIN INGANTACCE NE.

* WANNAN KAWAI SHI NE ABIN DA YA INGANTA NA HADISIN GADEER. ANNABI (SAW) YA YI HU'DUBA A WANI KWARIN RUWA, WANDA AKE KIRA DA "KHUMMUN", WANDA YAKE TSAKANIN MAKKA DA MADINA. SAI YA YI YABO DA GODIYA WA ALLAH, YA YI WA'AZI YA TUNATAR, SA'ANNAN YA YI ISHARA ZUWA GA KUSANTOWAN LOKACIN RASUWARSA, SAI YA YI WASIYYA DA RIK'O DA LITTAFIN ALLAH, DA KIYAYE HAKKOKIN IYALAN GIDANSA.

* SA'ANNAN A CIKIN WANNAR KHU'DUBA DA YA YI, YA YI BAYANIN MATSAYIN ALIYU (RA) A WAJENSA, SABODA K'IYAYYA DA WASU SUKE NUNA MASA, SAI YA CE:
" ู…ู† ูƒู†ุช ู…ูˆู„ุงู‡ ูุนู„ูŠ ู…ูˆู„ุงู‡ "
"DUK WANDA NA ZAMA MASOYINSA TO ALIYU MASOYINSA NE".

K**AR YADDA IMAMU AHMAD YA RUWAITO DA ISNADI MAI KYAU DAGA ALIYU (RA), HAKAN NAN TIRMIZIY DA 'DABARANIY S**A RUWAITO DAGA ZAIDU BIN ARK'AM (RA) CEWA; ANNABI (SAW) YA FA'DI HAKAN. SHI KUMA ZAIDU BIN ARQAM (RA) SHI NE WANDA YA RUWAITO WANCAN HADISIN DA MUSLIM YA FITAR DA SHI, WANDA YA YI BAYANIN HU'DUBAR ANNABI (SAW) A GADEER KHUM.

TO ABIN TAMBAYA A NAN SHI NE; MENENE DALILIN DA YA SA ANNABI (SAW) FA'DI WANNAR MAGANA, DA TAKE WAJABTA SON ALIYU (RA), DA NISANTAR K'INSA DA ADAWA DA SHI??

LALLAI DALILIN DA YA SA ANNABI (SAW) YA YI WANNAR HU'DUBA, HAR YA FA'DI WANNAR MAGANA A GAME DA ALIYU (RA) A GADEER KHUM, SHI NE; KASANCEWAR TUN KAFIN ANNABI (SAW) YA FITO AIKIN HAJJI DAGA MADINA, YA AIKA ALIYU (RA) A CIKIN WATA TAWAGA A MATSAYIN SHUGABANTA ZUWA YAMAN, TARE DA WASU SAHABBAI, HAR ANNABI (SAW) YA TAFI HAJJI BA SU DAWO MADINA BA, A KAN ZA SU WUCE MAKKA SU HA'DU DA ANNABI (SAW) A CAN WAJEN AIKIN HAJJI.
SAI ALIYU (RA) DA WA'DANDA SUKE TARE DA SHI, S**A RISKI ANNABI (SAW) DA SAHABBANSA A WAJEN AIKIN HAJJI, SAI BURAIDA BIN HUSAIB (RA) YA JE WAJEN ANNABI (SAW) YANA GAYA MASA ABIN DA YA GANI A WAJEN ALIYU (RA) NA TSANANI DA KUMA 'DAUKAR BAIWA DA ALIYU (RA) YA YI DAGA CIKIN KHUMUSI, A LOKACIN SUNA TARE A YAMAN, SAI YA NAK'ASA ALIYU (RA), SAI ANNABI (SAW) YA YI FUSHI, SAI YA CE MA BURAIDA (RA):
ู…ู† ูƒู†ุช ู…ูˆู„ุงู‡ ูุนู„ูŠ ู…ูˆู„ุงู‡
"DUK WANDA NA ZAMA MASOYINSA, TO ALIYU (RA) MA MASOYINSA NE".

TO, BAYAN AN GAMA AIKIN HAJJI ANA DAWOWA SAI AKA ISO "GADEER KHUM", SAI AKA YA DA ZANGO DON A SAUKA A HUTA, SAI ANNABI (SAW) YA TASHI YA YI HU'DUBA WA MUTANE DA SUKE TARE DA SHI, A CIKI SAI YA FA'DI WANNAN HADISI:
ู…ู† ูƒู†ุช ู…ูˆู„ุงู‡ ูุนู„ูŠ ู…ูˆู„ุงู‡
"DUK WANDA NA ZAMA MASOYINSA, TO ALIYU (RA) MA MASOYINSA NE".

(1) IMAMU AHMAD YA RUWAITO YA CE:
ุญุฏุซู†ุง ุงู„ูุถู„ ุจู† ุฏูƒูŠู†ุŒ ุญุฏุซู†ุง ุงุจู† ุฃุจูŠ ุบู†ูŠุฉุŒ ุนู† ุงู„ุญูƒู…ุŒ ุนู† ุณุนูŠุฏ ุจู† ุฌุจูŠุฑุŒ ุนู† ุงุจู† ุนุจุงุณุŒ ุนู† ุจุฑูŠุฏุฉ ู‚ุงู„: ุบุฒูˆุช ู…ุน ุนู„ูŠ ุงู„ูŠู…ู† ูุฑุฃูŠุช ู…ู†ู‡ ุฌููˆุฉุŒ ูู„ู…ุง ู‚ุฏู…ุช ุนู„ู‰ ุฑุณูˆู„ ุงู„ู„ู‡ ุตู„ู‰ ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ ูˆุณู„ู… ุฐูƒุฑุช ุนู„ูŠุง ูุชู†ู‚ุตุชู‡ุŒ ูุฑุฃูŠุช ูˆุฌู‡ ุฑุณูˆู„ ุงู„ู„ู‡ ุตู„ู‰ ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ ูˆุณู„ู… ูŠุชุบูŠุฑ ูู‚ุงู„: " ูŠุง ุจุฑูŠุฏุฉ ุฃู„ุณุช ุฃูˆู„ู‰ ุจุงู„ู…ุคู…ู†ูŠู† ู…ู† ุฃู†ูุณู‡ู… ุŸ " ู‚ู„ุช: ุจู„ู‰ ูŠุง ุฑุณูˆู„ ุงู„ู„ู‡ . ู‚ุงู„: " ู…ู† ูƒู†ุช ู…ูˆู„ุงู‡ ูุนู„ูŠ ู…ูˆู„ุงู‡ "

DAGA BURAIDA (RA) YA CE:
"NA JE YAK'I TARE DA ALIYU (RA) A YAMAN, SAI NA GA KAUSHIN HALI A TARE DA SHI, TO A LOKACIN DA MUKA ISA WAJEN ANNABI (SAW) NA AMBACI ABIN DA ALIYU (RA) YA YI, SAI NA K'ASK'ANTA SHI (AIBANTAWA), SAI NA GA FISKAR ANNABI (SAW) TANA CANZAWA, SAI YA CE:
"YA BURAIDA, SHIN BA NI NE NA FI CANCANTA GA MUMINAI FIYE DA KAWUKANSU BA?".
SAI NA CE: EH, HAKA NE YA MANZON ALLAH.
SAI YA CE:
"DUK WANDA NA ZAMA MASOYINSA, TO ALIYU (RA) MA MASOYINSA NE".
WANNAN HADISIN INGANTACCE NE.

(2) KUMA IMAMU AHMAD DA HAKIM SUN RUWAITO:
ุญุฏุซู†ุง ูˆูƒูŠุนุŒ ุญุฏุซู†ุง ุงู„ุฃุนู…ุดุŒ ุนู† ุณุนุฏ ุจู† ุนุจูŠุฏุฉุŒ ุนู† ุงุจู† ุจุฑูŠุฏุฉุŒ ุนู† ุฃุจูŠู‡ ุฃู†ู‡: ู…ุฑ ุนู„ู‰ ู…ุฌู„ุณุŒ ูˆู‡ู… ูŠุชู†ุงูˆู„ูˆู† ู…ู† ุนู„ูŠ ููˆู‚ู ุนู„ูŠู‡ู… ูู‚ุงู„: ุฅู†ู‡ ู‚ุฏ ูƒุงู† ููŠ ู†ูุณูŠ ุนู„ู‰ ุนู„ูŠ ุดูŠุกุŒ ูˆูƒุงู† ุฎุงู„ุฏ ุจู† ุงู„ูˆู„ูŠุฏ ูƒุฐู„ูƒ ูุจุนุซู†ูŠ ุฑุณูˆู„ ุงู„ู„ู‡ ุตู„ู‰ ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ ูˆุณู„ู… ููŠ ุณุฑูŠุฉ ุนู„ูŠู‡ุง ุนู„ูŠุŒ ูˆุฃุตุจู†ุง ุณุจูŠุง ู‚ุงู„: ูุฃุฎุฐ ุนู„ูŠ ุฌุงุฑูŠุฉ ู…ู† ุงู„ุฎู…ุณ ู„ู†ูุณู‡ . ูู‚ุงู„ ุฎุงู„ุฏ ุจู† ุงู„ูˆู„ูŠุฏ: ุฏูˆู†ูƒ . ู‚ุงู„: ูู„ู…ุง ู‚ุฏู…ู†ุง ุนู„ู‰ ุงู„ู†ุจูŠ ุตู„ู‰ ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ ูˆุณู„ู… ุฌุนู„ุช ุฃุญุฏุซู‡ ุจู…ุง ูƒุงู†ุŒ ุซู… ู‚ู„ุช: ุฅู† ุนู„ูŠุง ุฃุฎุฐ ุฌุงุฑูŠุฉ ู…ู† ุงู„ุฎู…ุณ . ู‚ุงู„: ูˆูƒู†ุช ุฑุฌู„ุง ู…ูƒุจุงุจุง ู‚ุงู„: ูุฑูุนุช ุฑุฃุณูŠุŒ ูุฅุฐุง ูˆุฌู‡ ุฑุณูˆู„ ุงู„ู„ู‡ ุตู„ู‰ ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ ูˆุณู„ู… ู‚ุฏ ุชุบูŠุฑ ูู‚ุงู„: " ู…ู† ูƒู†ุช ูˆู„ูŠู‡ุŒ ูุนู„ูŠ ูˆู„ูŠู‡ "

DAGA BURAIDA YA CE:
"YA KASANCE AKWAI WANI ABU A ZUCIYATA A GAME DA ALIYU (RA), KHALID MA YA KASANCE HAKA, SAI MANZON ALLAH (SAW) YA AIKANI A CIKIN TAWAGA WACCE SHUGABANTA SHI NE ALIYU (RA), SAI MUKA SAMU BAYI, SAI ALIYU (RA) YA 'DAUKI WATA BAIWA DAGA CIKIN KHUMUSI MA KANSA, SAI KHALID YA CE: TO KA K**A SHI DA WANNAN LAIFIN.
SAI YA CE: A LOKACIN DA MUKA ZO WAJEN ANNABI (SAW) SAI NA FARA GAYA MASA ABIN DA YA FARU, SAI NA CE: ALIYU (RA) YA 'DAUKI BAIWA DAGA KHUMUSI.
TO NA KASANCE NI MUTUM NE MAI SUNKUYAR DA KAI, TO SAI NA 'DAGA KAINA, SAI NA GA FISKAR MANZON ALLAH (SAW) TA CANZA, SAI YA CE:
"DUK WANDA NA ZAMA MASOYINSA, TO ALIYU (RA) MA MASOYINSA NE".
WANNAN HADISIN INGANTACCE NE.

(3) WANNAN HADISIN KUWA, BUKHARI MA YA RUWAITO SHI K**AR HAKA:
ุญุฏุซู†ูŠ ู…ุญู…ุฏ ุจู† ุจุดุงุฑ ุญุฏุซู†ุง ุฑูˆุญ ุจู† ุนุจุงุฏุฉ ุญุฏุซู†ุง ุนู„ูŠ ุจู† ุณูˆูŠุฏ ุจู† ู…ู†ุฌูˆู ุนู† ุนุจุฏ ุงู„ู„ู‡ ุจู† ุจุฑูŠุฏุฉ ุนู† ุฃุจูŠู‡ ุฑุถูŠ ุงู„ู„ู‡ ุนู†ู‡ ู‚ุงู„ ุจุนุซ ุงู„ู†ุจูŠ ุตู„ู‰ ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ ูˆุณู„ู… ุนู„ูŠุง ุฅู„ู‰ ุฎุงู„ุฏ ู„ูŠู‚ุจุถ ุงู„ุฎู…ุณ ูˆูƒู†ุช ุฃุจุบุถ ุนู„ูŠุง ูˆู‚ุฏ ุงุบุชุณู„ ูู‚ู„ุช ู„ุฎุงู„ุฏ ุฃู„ุง ุชุฑู‰ ุฅู„ู‰ ู‡ุฐุง ูู„ู…ุง ู‚ุฏู…ู†ุง ุนู„ู‰ ุงู„ู†ุจูŠ ุตู„ู‰ ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ ูˆุณู„ู… ุฐูƒุฑุช ุฐู„ูƒ ู„ู‡ ูู‚ุงู„ ูŠุง ุจุฑูŠุฏุฉ ุฃุชุจุบุถ ุนู„ูŠุง ูู‚ู„ุช ู†ุนู… ู‚ุงู„ ู„ุง ุชุจุบุถู‡ ูุฅู† ู„ู‡ ููŠ ุงู„ุฎู…ุณ ุฃูƒุซุฑ ู…ู† ุฐู„ูƒ

DAGA BURAIDA YA CE:
ANNABI (SAW) YA AIKA ALIYU (RA) ZUWA WAJEN KHALID (RA) DON YA KAR'BI KHUMUSI, NI KUMA NA KASANCE INA K'IN ALIYU (RA), KAWAI SAI GA SHI YA YI WANKA (NA JANABA), SAI NA CE MA KHALID: SHIN BA KA GA ABIN DA WANNAN MUTUMI YA YI BA?!
TO LOKACIN DA MUKA ZO WAJEN ANNABI (SAW) SAI NA GAYA MASA ABIN DA YA FARU, SAI YA CE:
"YA BURAIDA, SHIN KANA K'IN ALIYU (RA) NE?
SAI NA CE: EH.
SAI YA CE:
"TO KADA KA K'I SHI, SABODA YANA DA RABO A CIKIN KHUMUSI FIYE DA DA BAIWAR DA YA 'DAUKA".

TO, WANNAN K'IYAYYA DA WASU DAGA CIKIN SAHABBAI SUKE YI WA ALIYU (RA) ITA CE DALILIN DA YA SA DA ANNABI (SAW) YA ZO GADEER KHUM A KAN HANYARSA TA KOMAWA MADINA, SAI YA YI HU'DUBA A CIKIN MUTANE, DON SAURAN SAHABBAI MASU ADAWA DA ALIYU (RA) SU NISANCI HAKAN, BAYAN TUN A FARKO YA KWA'BI SHI BURAIDA (RA).

SABODA HAKA WANNAN A FILI YAKE, BA WANI DALILI NE YA SA ANNABI (SAW) YA YI HU'DUBA A GADEER KHUM BA, FACE DON YA KAWAR DA K'IYAYYAR ALIYU (RA) DA WASU SAHABBAI SUKE YI MASA, DON HAKA KWATA โ€“ KWATA BABU MAGANAR SHUGABANCI, KO KHALIFANCI, KO IMAMANCI A CIKIN HU'DUBAR DA ANNABI (SAW) YA YI A GHADEER KHUM.
WANNAN YA SA YA YI AMFANI DA KALMAR "MAULA", WACCE TAKE DADAI DA KALMAR "WALIYYI" WACCE TAKE 'DAUKE DA MA'ANAR MASOYI MAI TAIMAKO, BAI YI AMFANI DA KALMAR "WAALIY" BA, WACCE TAKE 'DAUKE DA MA'ANAR SHUGABA.
SHI YA SA YA CE:
ู…ู† ูƒู†ุช ู…ูˆู„ุงู‡ ูุนู„ูŠ ู…ูˆู„ุงู‡ "
"DUK WANDA NA ZAMA MASOYINSA, TO ALIYU (RA) MA MASOYINSA NE."
BAI CE:
ู…ู† ูƒู†ุช ูˆุงู„ูŠู‡ ูุนู„ูŠ ูˆุงู„ูŠู‡
"DUK WANDA NA KASANCE SHUGABANSA, TO ALIYU MA SHUGABANSA NE" BA.
BAI FA'DI HAKA BA.

SABODA HAKA KWATA - KWATA HADISIN BA YANA MAGANA A KAN SHUGABANCI BA NE, ANNABI (SAW) YANA MAI DA MARTANI NE, SABODA K'ARAN ALIYU (RA) DA AKA KAWO MASA, WANDA YA K'UNSHI AIBANTA SHI DA NUNA MASA ADAWA DA K'IYAYYA.

** DON HAKA A TAK'AICE, DUK ABIN DA BA WANNAN BA, BA INGANTACCE BA NE A HADISIN GADEER, IMMA YA ZAMA K'ARIN 'YAN SHI'A NE, KO KUMA K'ARIN DA'IFAN MARUWAITA MARASA KIYAYE HADISI K**AR YADDA YAKE.

27/10/2017

WAJIBI NE JAMI'AN TSARO SU HANA TA'ADDANCI A KAN GAWAR DAN MAJALISA DAME:
Wajibi ne Gwamnan Jihar Taraba a matsayin shi na chief security na Jihar, da kuma Police commissioner na Jihar su hana Kiristoci a karkashin kulawar Kungiyar CAN cin mutuncin gawar Dan Majasiar Jihar Taraba Abdul Malik Emma Dame da Allah Ya yi masa rasuwa Alhamis din nan.
Shi dai Abdul Malik Emma Dame mutum ne da ya musulunta a lokacin da yake dan majalisar Jihar Taraba yau fiye da shekaru bakwai ke nan da s**a wuce, kuma tun da ya musulunta din dan majalisa ne shi har zuwa Alhamis din nan 26/10/2017 da Allah Ya dauki ran shi.
Dan Majalisa Dame da girmansa ne, kuma ilminsa, cikin kuma hayyacinsa, da lafiyarsa ya yi watsi da addini, da kuma imani irin na kiristanci, ya koma a cikin zabinsa, da ganin damansa ya rungumi addini, da kuma imani na Musulunci; don Allah in banda tsokanar al'ummar Musulmi da fada, da kuma ra'ayi irin na yin ta'addanci a kan matacce ta kaka ne za a ce: kiristocin Jihar Taraba za su nemi maida gawar wannan Dan Majalisa kirista a yanzu; kiristancin da ita gawar ta guje wa, ta kuma yi watsi da shi a lokacin da take raye??
Muna kira ga Inspector General na Police da ya ja hankalin Police Commissioner na Jiha Taraba da ya yi aiki da dokar Kasa ya nesantar da Kiristocin Taraba daga gawar wannan Dan Majalisa Dame.
Allah Ka raba mu da dukkan wata fitina. Amee.

Daga Dr Ibrahim Jalo Jalingo

05/09/2017

HAQIQANIN ABINDA YA JANYO RIKICIN BURMA

A iya bincikenda nayi gameda Rikicin
Shine Sude yan'uwa musulmai da ake kashewa ba yan Asalin Burma bane

Su Suna gefen Qasar Burma ne sunan yankin dasuke sunanshi (Arakaan) daulace me cin gashin kanta

Yawan musulman dake ciki garin adadinsu ya kai miliyan 3

Ayayinda sukuma yan Burma sun kai miliyan 50

Sude musulman Arakan Allah ya Azurtasu da malamai Na Addini dasuke shuguwa suna musu da'awa

Harma ya kaiga suna basu auren yaransu domin musulunci ya qara samun yaduwa

Ana cikin Haka se yan Burma s**a qullaci Musulman Arakan da malaman dake musu da'awa

Daga nan s**a shirya propaganda s**a afka ma wadannan malamai masu da'awa da duka suna feto dasu daga gidajensu suna duka

Haka Za'a kamo mutun akama harshensa a yanka

Zasu kashe mutun susa Wuqa suna wasa da gawansa

Daga nan se musulman s**aga cin mutuncin da ake ma yan da'awan nan yayi yawa se s**a tashi domin basu kariya

Shikenan sukuma yan Burma ses**a farma yan Arakan din gaba daya

S**a fara qona gidaje tare da kashe yara qanana

Adadin gidajen da s**a qona awannan shekara na 1784 ya kai 2600

Mutane da dama sun nutse aruwa sun mutu garin guduwa domin su tsira da rayukansu

Bayan haka ta faru se s**a hada garin Arakan da burma seya zama yana qarqashin ikonsu

Wannan fa shine musabbabin rikicin

Badon komai akamusu haka ba wai sedon sunce sun yarda Allah shine ubangijinsu

Wai meyasa Qasa yafi jinin dan adan wahalan zubarwa ne ???

Meyasa dan Adam din da aka karramashi sama da dukkannin halittu ake cin zarafinsa hakane ???

Saboda dan Adam din nanfa aka saukar da Littafi badon komai ba se don a sanya rayuwansa cikin tsari

Saboda dan Adam din nan ne fa aka aiko da manzanni saboda a ban bantashi da dabba

Wannan Dan Adam din ne fa akasa mala'iku s**a masa sujuda

Saboda Dan Adam din nan ne fa aka saukar da shari'a badon komai saboda abashi haqqinsa

Meyasa yau muka wayi gari Dan Adam yazama kamar dabba ne

Ina Human Rights ne ???

Menene anfaninku ???

Allah kadai yasan meze biyo baya matuqar aka cigaba da kashe muslmai a Burma

Allah be Azzalumin KOwa bane

Allah ka Kawo musu mafita

Daga BinAl-Qasim Asadul Islam

05/04/2017

โ€‹INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJIUN!!!โ€‹

โ€‹Allah ya yiwa daya daga cikin manyan malaman kasar nan Sheikh Dr. Alhassan Sa'id Adam Jos rasuwa a wani asibiti dake kano.โ€‹

โ€‹Za'ayi jana'izarsa a Gobe Alhamis, misalin karfe 11:00am na safe.

KUMA ZA'AYI JANAIZAR NE A MASALLACIN ALFURQAN, DAKE ALU AVENUE, NASSARAWA, A JIHAR KANO.

Muna rokon Allah ya gafarta masa kuma yayiwa zuriyarsa albarka.

28/01/2017

Allah yajikan Sheikh Rabiu Daura ya gafartamasa kurakuransa ya Mai Rahama yasa Aljanna ce makomarsa Ameen.

26/01/2017

SOUTHERN KADUNA: WHO ARE THE REAL VICTIMS?

Muhammad Auwal Abu Suhaib Jamaโ€™a town was founded by the Muslims in 1804 under the Ruler ship of Malam Usman Yabo and similarly Zango town by the Hausa Muslims traders. Therefore, the crises in the region is a grand design to completely wipe-out the Muslims and Muslim Communities in the area by the Christians Militias taking advantage of their numerical strength. It is important to note that, the Districts of Zangon Kataf, Kachia, Kagarko and Chawai referred to as at then as Southern Zaria were under Zazzau Emirate until the creation of Chiefdom by the administration of Colonel Lawal Jaโ€™afaru Isa in 1995 and the additional by Ahmed Mohammed Makarfi in 2001.

The Catalogue of Crises in Southern Kaduna include:-

๏ƒผ The kasuwan Magani Episodic Massacre of Muslims 1979/80, 19 people were killed all of them Muslims.

๏ƒผ The Kaduna Strife 1982

๏ƒผ The Jere incidence of 1983

๏ƒผ The Gure/kahugu and Yarkasuwa Crisis 1984

๏ƒผ The Kafanchan Crisis of 1987, which spread to Kaduna, Zaria, Ikara, Funtua, Katsina etc

ยค1992 Zango Kataf Genocide.

๏ƒผ The kafanchan attack of 1999 against installation of the New Emir of Jama'a: 54 Muslims were Massacred.

๏ƒผ The February and May 2000 Kaduna Carnage and the massive killing of Muslims in February 23, 2000 in Kachia.

๏ƒผ The 2005 Merciless attack on the Muslims in Mariri, town-lere Local Government. Eleven Muslims killed and over 155 houses destroyed.

๏ƒผ The Post2011 Presidential Election Violence in some parts of the state which resulted in the cleansing of
Muslims in Zonkuwa town, which is still fresh in our memories.

๏ƒผ The 2013 Crises resulting in the killing of 11 Muslims in Kafanchan, Sanga and Kachia.

๏ƒผ The 2016 crises resulting in the killing of 84 Muslims in Samarun Kataf and another 4 in Dangoma.

๏ƒผ The Muslims towns of Zango, Zonkwa, Matsirga, Sabon Gora, Television, Sabon Tasha, Marrabar Rido were completely wiped out and the next target is Kafanchan another strong hold of the Muslims in Southern Kaduna.

๏ƒผ The Persistent communal clashes between the Pastoral and Farmers in the Southern Senatorial District of the state.

All these crises had their genesis from Southern Kaduna State and aggressive against the Muslims.

However, those of 1987,1992, 2000 and 2011 were unprecedented which touches not only on the Social, Political and Economy of the State but the country as a whole. It was senseless and merciless attack on the Muslims.

Details of some these crises were given below:

(1) 1987 Kafanchan Violence, 19 Muslims killed,Many wounded and property worth N78,537,768.94 destroyed. Instigators are
(i) Rev Abubakar Bko
(ii) Capt Manya
(iii) Fellowship of Christian students
(iv) Mrs Ladi Lekwot and others,

(2) 1992 Zangon Kataf Genocide against Muslims,1,533 Muslims massacred, thousandth wounded and property worth N207,658,560.00 destroyed.
The planners and executors were: Gen Zamani Lekwot,
Mal B.A.D Gora,.
Mr J.B.Ayok and many Christians and political leaders.

Gen Lekwot and 5 others were found guilty and sentenced to death but was not carried out.

(3) 2000 Religious disturbances: Over 5000 Muslims perished thousands wounded and unquantifiable property loss.
The following Christians leaders were found to be involved
Elder Saidu Dogo,
Archb P. Y. Jatau,
Archb B.A. Achigili and many others.

See White Paper on the Report of Judicial Commission of Inquiry into Kaduna State Religious Disturbances of February 2000, Page 17.

(4) 2011 Presidential election, 943 persons were killed, thousands wounded and property worth
N23,330,737,540.00 destroyed.

Brig Gen. Adamu Dyeris and many others were indicted.

NOTES:
i.- it should be noted that in the statistical figures of 943 deaths recorded all over the country in the 2011 post presidential election disturbances over 80 % of persons killed were from southern Kaduna senatorial district and in this crises, there was no arrest in connections with the killings. See chapter two page 17 of The White Paper on the Report of the Federal Government Investigation Panel on the Election Violence.

ii- it should also be noted the convoy of Emir Of Jamaโ€™a was ambushed at Samarun Kataf on his way back to Kafanchan from Kaduna after a security meeting and similarly the
convoy of the Execute Governor of Kaduna State and members of security council were also attacked about a month ago. All these are indication that the people of Southern Kaduna don't want peace.

THE WAY FORWARD

1. Failure of Government to punish perpetrators of these crises has allowed the continuation of similar crises in the state for close to 40 years.

2. We call on the Government to arrest and punish the perpetrators of the current crises.

3. We call on the Government to find lasting solutions to all these crises.

4. The Government should as a matter of urgency revive the Muslim-Christian consultative committee which is headed by the Governor of the State.

5. The Government should always take proactive measures upon receipt of intelligent report.
Nuhu Ali Ayo Ojeniyi Cyril Oseghale Ladesope Ladelokun Segun Fagbemi

Address

Hotoro Kano
Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sheikh Alqasim Umar Jibrin Hotoro posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Share on Facebook Share on Twitter Share on LinkedIn
Share on Pinterest Share on Reddit Share via Email
Share on WhatsApp Share on Instagram Share on Telegram