Kerau Quarters Katsina

Kerau Quarters Katsina peaceful place and welcome to all

26/06/2025

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Aleey Heydeer, Sulaiman Hassan, Moh Isa, Isah Nafiu

تقبل الله منا ومنكم
05/06/2025

تقبل الله منا ومنكم

05/06/2025

Idan Ka Tashi Aure Abokina....

Ka Auri Matar Aure, Karka Kuskura Ka Auri Matar Gida.
Kayi Aure, KarKa Bari A Aureka.
Ka Auri Wadda Take Sonka, Ba Wadda Kake So Ba.

Ka Auri Mace Ba Ƴar Gwagwarmaya Ba.
Ka Auri Mai Son Addini, Ba Mai Ilimin Addini Ba.
Karka Damu Da Auren Ƴar Alhaji Wane, Domin A Mafiya Yawan Lokuta Auren Ƴar Malam Wane Yafi Alheri A Gareka.

Ka Auri Nagarta, Kaso Nagarta, Ka Nemi Nagarta, Tabbas Aurenka Zai Kasance Mai Nagarta!

04/06/2025

❝ Wata ba mijin aure ta rasa ba, kalar mijin da take so ne bata samu ba, dan haka take jiran lokaci. Saboda ita bata yadda ta sha wahala ba. kawai abinda take so ta auri wanda ya sha Gwagwarmaya, ya sha Wahala ya tara kuɗinsa, Rana daya ya dauko ta tazo taji daɗi da dukiyarsa. Ita bata yadda ta auri talakka ba, koda yana da manufa da tsarin rayuwa mai kyau. Kawai burinta ta ji daɗi tun daga farkon aurenta har ta tsufa Kuma wannan ba zai yiwu ba har abadah ❞

•Wa ya fada miki Auren Me kudine yake bada Jin dadin zaman aure⁉️😨 idan kina wasa da rayuwarki to ki farka, domin samun kudi ba shi ne yake kawo kwanciyar hankalin zaman gidan Aureba, face samun Namijinda ya dace mai Addini da Nagarta•

Duk irin wannan bayanan wasu Matan basa ganesu har sai sunje sun fada hannu marar kyau da suke tsammanin samun jin dadin, idan s**a ga Bacin rai da bakinciki a aikace, sannan suke yin Nadama marar amfani🧏🏻🤷🏻‍♂️

Ya ke Yar Uwa mai Daraja kada ki gwada idan kuma zaki gwada ga Duniyar nan🤷🏻‍♂️

Allah yasa mu dace

14/04/2025

ƘISSAR AS'HABUL UKHDUD (MA'ABOTA RAMIN WUTA)

Daga shafin Bashir Halilu.

Allah Maɗaukakin Sarki Ya faɗi ƙissar waɗannan mutane a Alkur'ani mai girma, cikin suratul Buruwj, ayah ta huɗu, Allah Ya ce:

قُتِلَ أَصْحَابُ الْأُخْدُودِ • النَّارِ ذَاتِ الْوَقُودِ • إِذْ هُمْ عَلَيْهَا قُعُودٌ • وَهُمْ عَلَى مَا يَفْعَلُونَ بِالْمُؤْمِنِينَ شُهُودٌ • وَمَا نَقَمُوا مِنْهُمْ إِلَّا أَن يُؤْمِنُوا بِاللَّهِ الْعَزِيزِ الْحَمِيدِ • الَّذِي لَهُ مُلْكُ السَّمَوَاتِ وَالْأَرْضِ وَاللَّهُ عَلَى كُلِّ شَيْءٍ شَهِيدٌ •

Ma'ana

4. An la'anci ma'abota rami (na azabtar da muminai).

5. Na wuta mai ruruwa.

6. Yayin da suke zaune a gefenta.

7. Alhali su suna kallon abin da suke aikata wa muminai.

8. Babu kuwa abin da suke tuhumar su da shi sai don kawai sun yi imani da Allah Mabuwayi, Sha-yabo.

9. Wanda Yake da mulkin sammai da kasa. Allah kuma Mai ganin komai ne.

Acikin wannan Ƙissa, Allah (Mai tsarki da daukaka) ya bayyana cewa, ya la'anci ma'abota wani wawakeken rami, wanda s**a haƙa s**a hura wuta a cikinsa ganga-ganga, s**a riƙa jefa muminai a cikinsa da ransu, yayin da suke zaune a gefen ramin suna kallon yadda suke azabtar da muminai. Ba don wani laifi da suke tuhumar su da aikatawa ba, sai don kawai sun yi imani da Allah Mabuwayi, Sha-yabo, wanda shi ne kadai mai mulkin sammai da kasa, kuma mai ganin komai.

Annabi (SAW) ya ba da labarin waɗannan muminai da aka yi wa wannan azaba ta jefa su cikin ramin wuta, kamar yadda ya zo a hadisin da Muslim [ #3005] ya ruwaito daga Suhaibu dan Sinan (Allah ya kara masa yarda).

A taƙaice, hadisin ya bayyana cewa: "A da can an yi wani sarki kafiri, yana da mai yi masa aikin sihiri. To lokacin da mai sihirin ya tsufa sai ya bukaci Sarki ya zabo wani matashi daga jama'arsa don ya koya masa sihiri, domin ya ci gaba da wannan aiki nasa ko bayan mutuwarsa. Sarki ya amsa masa, ya tura masa wani saurayi wanda zai rika koyon sihiri a wurinsa.
A hanyar saurayin ta zuwa wurin malaminsa mai sihiri, sai yake gamuwa da

11/04/2025

DAGA CIKIN HANYOYIN SAMUN KUSANCI ZUWA GA ALLAH.

Yi qoqari duk lokacin da ka samu dama, a gida, shago ko office ka saba da yin sallar walha. Raka'a biyu ko hudu, ko shida ko takwas.

Lokacin ta yana farawa ne daga bayan hudowar rana da 'yan mintoci zuwa kafin sallar azahar da kamar minti 15. Amma darajar ta tana qaruwa idan rana ta fara zafi kad'an. (10am +).

Sallar walha tana daga cikin ibadoji ma su saurin kusantar da zuciyar bawa zuwa ga Allah. Tana kawo natsuwar zuci da yayewar damuwa Wallahi. Sadaka ce daga dukkan gabbai, ajiya ce a asusun ayyukan alherinka, kuma wasiyya ce ta musamman daga manzo S.A.W zuwa ga masoyanshi.

Dan'uwa yi sauri ka shiga cikin ayari, kar ka bari a bar ka a baya.

11/04/2025

Alhamdulillah for another blessed Friday. May Allah accept your prayers, forgive your sins, & shower you with His mercy. "Indeed, the best day on which the sun has risen is Friday." (Sahih Muslim) May this Jumu ah bring peace, blessings, success to you & your loved ones. Jumu'ah Mubarak

28/03/2025

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Sulaiman Nababa, Mustapha Mannir Kofar Bai, Ibrahim Aminu Maigari, Engr Suleiman Modibbo Umar, Abubakar Abdullahi, Yusuf Mannir, Auwal Sambo, Umar Halilu, Rabilu Musa Gumau, Danniger Bindawa, Adamu Abba

15/03/2025

Big shout out to my new rising fans! Sulaiman Muhammad

22/03/2024

وعن عبدالله بن مسعود رضىالله عنه قال؛ قال رسول الله صلى الله عليه و سلم يعنى عن ربه عز وجل : (النظرة سهم مسموم من سهام إبليس من تركها مخا فتى أبدلته ايمانا يجد حلاوته فى قلبه) رواه الطبرانى والحاكم مم حديث حذيفة.

19/03/2024

قال رسول الله صلى الله عليه وسلم -: (قل سبحان الله ، والحمد لله ، ولاإله إلا الله ، والله أكبر ، يغرس لك بكل واحدة شجرة فى الجنة) صحيح ابن ماجة. (٣٠٨٤ والشجر الذي فى الجنة من ذهب وفضة ولؤلؤ وفا كهة الجنة ألين من الزبدة وأحلى من العسل ...

24/02/2024

Nau'in Mata 7 da baikamata namiji ya aura bah.
1) Al’anaanah: Mace mai jinini da tsirtiya
a kodayaushe, wadda kullum a shirye
take ta kai karar miji ko saurayi, sannan
ba ta da sirri ko na sisin kwabo.
2) Al-manaanah: Mai yawan shimfida
hannuwanta wajen bayar da kyauta ko
alheri, amma idan abu ya faru a gaba,
sai ta yi wa mijinta gorin cewa ta yi kaza
da kaza domin shi.
3) Al-hannanah: Mace mai tuna baya
kan tsohon mijinta ko saurayinta, har ta
rika cewa ai da wane ne, da ba zai yi
mata haka ba. Ko kuma ta rika sambatu
da sunan wani alhali tana tare da kai
4) Al-Kannaanaa: Mace mai yawan
surutu tare da alfahari da dukiyar
iyayenta ko ‘yan’uwanta, musamman
sarautar mahaifinta da sauransu.
5) Al-hadaakah: Mai zuba idanu kan
abin duniya. Komai ta gani sai ta nuna
maita da kwadayinta a fili, ba ta iya
boye abin take so, sannan za ta iya
takurawa ta matsa lamba, ba za ta
kwantar da hankalinta ba, har sai an
saya mata, ta kowane hali.
6) Al-barrakah: Mai yawan bata
lokacinta wajen gyaran fuska domin
birge maza, kuma ba ta damu da zubar
da kimarta gaban ko waye ba. Za ta yi
kwalliya ba don mijinta kawai ba, sai
domin a ce ta yi kyau, ko kuma kawaye,
‘yan’uwa da abokan arziki su ce tana jin
dadi a dakin mijinta.
7) Al-sadakah: Mai zubar gadon
kalamai, wadda ba ta da linzami ko
miskala zarratin ga harshenta. Allah ka bamu mata na gari ma su tsoron ka

Address

Katsina

Telephone

08069612009

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kerau Quarters Katsina posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Practice

Send a message to Kerau Quarters Katsina:

Share