23/11/2016
CIGABA DA TSARE SHAIKH ZAKZAKY YA SABAWA DOKAR KASA- Kungiyar CEDRA
* Gwamnati ta Sake Shi
*โYan Jaridu s**a rika yiwa โYan Shiโa adalci
Daga Mahdi Garba
Wata kungiya mai rajin kare hakkin bil adama mai suna โcentrum initiative for development and fundamental rights advocacy (CEDRA) a turance, tayi kira da a saki jagoran harkar Musulunci a Nijeriya, Shaikh Ibrahim Zakzaky. Tayi wannan kiran ne ranar laraba 23 ga watan Nuwamba, 2016 a babban dakin taron Julius Berger dake Jamiโar Lagos, a birnin Lagos din Nijeriya. Kiran ya fito ne daga bakin shugaban kungiyar Dakta John Danfulani, Malami kuma mai rajin kare hakkin โdan Adam.
A gabatar da makasudin zuwanshi birnin Ikko don karanta kasidar tasa yace โna fito ne yau don tattauna yadda Gwamnati ke take hakkin โYan Shiโa a wasu jihohin Arewacin Kasar. Kuma don neman goyon bayan masu fito-na-fito da zalunci a kudancin Kasar da ma duniya baki daya don irin yadda Gwamnatin Nijeriya da โyan amshin shatanta ke gasa musu dankali a hannu.โ
Ya cigaba da cewa โa lokacin da Sojoji s**a je gidan Shugaban โyan Shiโa Shaikh Zakzaky a watan Disamban shekarar da ta gabata, fitowarsu kai kace fagen daga zasu je fafatawa da wani babban makiyi. Daga bisani s**a daukeshi zuwa wani wajen da babu wanda ya sani, kafin s**a mika shi ga jamiโan tsaron farin kaya (DSS). Tun daga nan basu saken barinshi ya more โyancinshi da dokar Kasa ta 1999 ta tanadar ba don ko Kotu basu kaishi ba.โ
Duk da fitowar da almajiransa suke don gabatar da muzaharar lumanan neman sakin Malaminsu a Abuja, Gwamnati tayi kunnen uwar shegu da bukatarsu. Malamin ya shigar da kara akan take mishi hakki da Gwamnatin tarayya take, wanda muna fatan zasu sakeshi da gaggawa don zuwa ganin likita da kuma more โyancinsa a matsayin โdan Adamโ inji Dakta John Danfulani.
Da yake magana kan soke harkar da wasu Gwamnoni suke a fadin Kasar, yace โ wani abin da yake ci min tuwo a kwarya shine, a daidai lokacin da โyan harkar suke muzaharorin lumana don neman sakin jagoransu kamar yadda dokar kasa ta tanadar, kwatsam sai ga Gwamnonin wasu jihohin Nijeriya sun fara soke Harkar a jhohinsu, wanda haka katsalanda ne ga dokar Kasa. Saboda dokar Kasa ta baiwa kowanne โdan Kasa hurumin bautawa duk abinda ya yarda da shi.โ
Ya kara da cewa โsoke harkar a jihohin ne ya budewa wasu โyan jagaliya daman aukawa โya โyan harkar a garuruwa daban-daban. Amma abin takaici babu wanda Gwamnati ta gurfanar a Kotu ya zuwa yanzu.โ
Da yake korafi da nuna alhini akan rahotannin da โyan jarida suke kawowa duk lokacin da wani abu ya faru tsakanin โyan harkar da mahukuntan Kasar, ya yace โ a duk lokacin da aka yiwa โyan shiโa katsalanda akan โyancinsu, sai manema labarai su kawo wasu labarai masu ban dariya akan wai anyi fito-na-fito da Jamiโan Soji ko โYan Sanda. Wanda hakan ya tallafawa tatsuniyoyin da Gwamnati take yi ne akan โyan harkar na tafiya da muggan makamai a lokutan tarukansu. Wannan kawai labarin kanzon kurege ne.
Dakta Danfulani ya cigaba da koke akan dabiโar wasu โyan jaridu da kuma gidajen Jaridun Kasar. Ya nuna takaici akan yadda ake shirya labaran karya akan โYan IMN din, kuma idan s**a rubuta martini sai a jingine. Mafi munin lamari shine manyan gidajen jaridun Kasar basa son karban tallace-tallacensu.โ Inji Shi.
Dakta Danfulani ya cigaba da cewa โyan jaridu suna daga cikin kashin bayan Dimokradiyya. Don haka idan ana son Dimokradiyya ya daure a kowacce Kasa dole a yiwa kowanne โdan Kasa adalci wajen kowa labarinsa.โ
Da yake tofa albarkacin bakinsa kan dabiโun Jakadun wasu manya kasashe da wasu kungiyoyi masu zaman kansu dake Nijeriya, yace โJakadun wasu kasashe da wasu kungiyoyi masu zaman kansu su ma sun fada tarkon irin labaran da jaridun Nijeriya suke kawo kan lamarinโ. Yace abin takaici shine yadda su ma suke ganin hare-haren a matsayin arangama. Yace โda Kafata naje tattakin arbaโeen na Kano don naga wainar da ake toyawa a wajen. Babu wani mai makami acikinsu, amma idan aka kawo musu hari sai ace arangama akayiโ.
Idan ni daba โdan Shia ba, zan iya zuwa Kano mai zai hana Jakadun Amurka da sauran Kasashe zuwa wajen don cire kwarkwatar idanunsu?โ ya karkare.