Jibwis Yola West

Jibwis Yola West Wannan shafi namaganane akan Kitabu was Sunna, aikinsa shine nemo labarai na alkhairi kamar yadda kowane shafi na JIBWIS keyi. Allah yataimakemu, Ameen.

AN SAMU 'YAN GYARA DANGANE DA SANARWA DA MUKA FITAR DA SAFE.1- Wa'azin Dare a Ranar Asabar Tsakanin Magrib zuwa Isha ne ...
07/07/2021

AN SAMU 'YAN GYARA DANGANE DA SANARWA DA MUKA FITAR DA SAFE.

1- Wa'azin Dare a Ranar Asabar Tsakanin Magrib zuwa Isha ne kuma a Masallacin Juma'a na Doubeli za'a yi ba a Capital ba Kamar yadda muka sanar.

2- Aikin Hijama da kuma Medical outreach za'a soma sune tun daga karfe 8:00am na safe har zuwa karfe 4:00pm na yamma, inda za'a fara tun daga Ranar Juma'a har zuwa Asabar.

-Medical Outreach a Hannatu Ngilari Clinic Demsawo

-Hijama a Bakari Bole Clinic Shagari Phase 1 ne ba Phase 2 ba Kamar yadda muka sanar a baya.

3- Wa'azin Mata na Jam'iyyatu Nisa'us Sunnah za'a gabatar dashi ne a FOMWAN da Misalin karfe 10am na safe zuwa 12:00pm Insha Allah.

AN KADDAMAR DA GIDAUNIYAR TAIMAKAWA   A JIHAR ADAMAWA.Daga Khalifa Bello DahiruA jiya Jumma’ah 09/09/1439AH – 26/05/2018...
26/05/2018

AN KADDAMAR DA GIDAUNIYAR TAIMAKAWA A JIHAR ADAMAWA.

Daga Khalifa Bello Dahiru

A jiya Jumma’ah 09/09/1439AH – 26/05/2018 Kungiyar ta Jama’atul Izalatil Bid’ah Wa’ikamatus Sunnah Ta Kasa (JIBWIS), reshen jihar Adamawa ta gabatar da asusun tallafawa marayu na jihar, kamar yadda kungiyan ta JIBWIS karkashin jagorancin Asheik Abdullahi Bala Lau ta saba ko wacce shekara cikin watan domin tallafawa marayu da ke fadin kasan nan. Rehen Kungiyan ta JIBWIS ADAMAWA jiya a wurin Tafsirin Al-qur’ani mai girma, wanda Dr Abdulkadir Kazaure tare Alaramma Idris Gashuwa su gudanarwa a Babban Massallacin Jumma’a dake Demsawo. Kungiyar ta kaddamar da bayanin rahoton aiyukan da ta gabatar na tallafin marayu, na shekaran da ta gabata. Daga bakin Shugaban Kwamitin Marayun na Jiha, Alhaji Usman Ibrahim.

Daga bisani shugaban kwamitin Marayun na jiha ya bukaci shugaban Kungiya na Kasa, Asheik Imam Abdullahi Balau domin yazo ya fara kaddamar da tasa gudumawa ga marayun na jiha. Inda Shugaba Asheik Abdullahi Balau ya jaa Hankalin yen Uwa musulmai da su taimamawa Marayu a duk inda suke, hakazalika ya kara da jaa hankalin matasa akan gujewa shiga harkan chacha na Naijabet wanda kusan yanzu ta zamto ruwan dare waa .

Shugaban Kungiyar na Kasa Asheik Abdullahi Balau ya kaddamar da asusun na bana da
Shinkafa forin Buhu Hamsin (50Bags) Sannan da kudi naira Dubu dari biyu da Hamsin
N250,000.00
Bayan shugaban kungiya na kasa Asheik Abdullahi Bala Lau ya kamala kaddamar da tasa gudumawa sai saura al-ummah s**a shiga kaddamar da tasu gudumawa domin ganin anyiwa marayu kayan Sallah da kuma tallafa musu da abinci yayin bukin Sallah.
A cigaba da tallafawa marayun ne Senata Abdul’aziz Nyako shima ya bada nasa gudumar na
Shinkafa 25kg 50bags
Masara 25kg 50bags da
1million cash (Naira Miliyon daya)
Malam Nuhu Ribada shima ya bada tasa gudumawar ta naira dubu dari biyar (N 500,000.00)
Al-ahli Security Guard suma s**a bada tasu tallafin na naira dubu dari (N100,000.00)
Hakazalika yen Agaji s**a rika zagayawa gurin yen uwa mahalarta tafsirin domin karban taimako wanda insha Allahu bana ma da ita za’a kuma tallafawa marayu domin suma suji tamkar iyayen su suna raye. Daga karshe Shugaban Kungiyan JIBWIS na kasa yayiwa yen uwa s**a taimaka fatan alkhairi, hakazalika masu niyan taimakawa daman wanda basu da halin taimakawa, ya kara da jan hankali bisa gujewa sharrin shedan. Daga nan ne Shugaban ya rufe wurin tafsirin adduah.
Allah ya saka da alkhairi kuma kofa abude yake domin taimawa a kowani lokaci.
Ameeeen
JIBWIS SOCIAL MEDIA ADAMAWA STATE.
KHALIFA BELLO DAHIRU
Agt. Secretary General JSM ADA Chapter

17/11/2017

FALALA.
INJI BAKIN DA BAYA QARYA " KU YAWAITA YIMIN SALATI ARANAR JUMA'AH" TO YAN UWA MUYI AZAMA DOMIN NEMAN FALALAR WANNAN RANA.

17/11/2017

ASSALAMU ALAIKUM.
HAPPY JUMU'AH TO ALL MUSLIMS.

31/10/2017

Ga wani sirri:
Idan akwai wanda kake jin haushi haka kawai to duk lokachin da kuka hadu ka mishi sallama wallahi zaku zama masoya.

ALLAH YAYIWA MAHAIFIN ADAMU JIBRIL RASUWA ASST. DIV. DISCPLINE OFFICER, NA MAJALISAR AGAJIN YOLA~WEST. ALLAH YA GAFARTA ...
16/09/2017

ALLAH YAYIWA MAHAIFIN ADAMU JIBRIL RASUWA ASST. DIV. DISCPLINE OFFICER, NA MAJALISAR AGAJIN YOLA~WEST. ALLAH YA GAFARTA MASA, AMEEN.

12/09/2017

Innaa lillahi wa'innaa ilaihi raji'uun. A shekaran jiyane
Allah yayiwa Mallam Hassan tela (Kawu) rasuwa, mahaifin dan uwah Abdurra'uf na anguwar wauru jabbe. Muna fatan Allah ya gafarta masa ameen.

04/09/2017

Bismillahir rahmanir raheem.
Qalallahu Ta'ala: La'in shakartum La'azidan nakum, wala'in kafartum inna azabee lashadeed.

02/09/2017

Assalamu alaikum, munaiwa al'ummah islamiyya barka da sallah, da fatan Allah ya karbi ibadun mu.

DAURIN AURE! DAURIN AURE!! DAURIN AURE!!!Iyalan Marigayi Malam Dahiru  Ahmadda naMarigayi Mallam Abdullahisuna farin cik...
26/04/2017

DAURIN AURE! DAURIN AURE!! DAURIN AURE!!!

Iyalan
Marigayi Malam Dahiru Ahmad
da na
Marigayi Mallam Abdullahi
suna farin cikin Gayyatan Yen uwa da Abokan Arziki
zuwa wurin Daurin Auren 'ya 'yansu
MALLAM YA'U D. AHMAD (El-Hajj)
da Amaryar sa
MALAMA HASSANA ABDULLAHI
wanda za'ayi kamar haka
Rana: 28 April, 2017
Lokaci: 07:30am prompt
Wuri: Walawol kusa da Massallacin Mallam Idris, wauru Jabbe, Yola South LGA, Adamawa State.

Allah ya bada ikon Halarta Ameeeeeen

Sanarwa: Jibwis Social Media Adamawa State

27/03/2017

ALFIRDAUS TAHIR ALIYU DA UMMU MUSADDAD ISLAMIC QIESTIONS N ANSWERS AL- ASHMAAWIY Bismillah wassalatu wassalamu ala rasulillah. (24) CIGABA DA KARATU CIKIN BABIN AZUMI Malam yace: Kuma Mustahabbi ne azumtar ranar arfa ga wanda baya aikin hajji, da azumtar goma ga Zulhijja da Almuharram da Rajab da Sha'aban, da kwanaki uku ako wani wata, Amman Malik ya karhanta su zama cikin ayyamul beed saboda gudun kar a iyakance kwanakin. Haka ya karhanta azumumtar sittu shawwal saboda tsoron kar jahili ya hadeshi da ramadan. Haka an karhanta dandanon gishiri ga mai azumi, in kuma yayi to ya tofar dashi kuma in babu wani abu nashi daya kai maqoshinsa to babu komai akanshi. Haka somi somin jima'i makaruhi ne ga mai azumi, kamar su sumbata, da shafa, da kallo wanda zaa dade (adade ana kallon har shaawa ya motsa), da wasanni in ansan bazaa sami matsala a yin hakan ba. (in ansan ko anyin mutum zai iya mallakan kanshi kar ya fadama abinda aka hana to shine yake matsayin makaruhi) amman in ba haka bama to haraamun ne yin hakan akanshi, amman in ya fitar da maziyyi saboda hakan da yayi to akwai ramuwa akanshi, in kuma ya fitar da maniyyi toh zaiyi ramuwa tare da kaffara. Qiyamu ramadan mustahabbi ne (tsayuwan dare) kuma an kwadaitar akan yinshi, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agareshi ya ce: Duk Wanda ya tsaya awatan ramadan yana mai imaani da neman lada to an gafarta masa abinda ya gabata na zunubansa. Kuma anso ( yin tarawihi agida) daya, daya ( agida ba a jam'in masallaci ba) in har ansan bazaa bar masallaci ba kowa ba. Allah shine mafi sani. Nan muka kawo qarshen wannan littafi mai albarka: العشماوية في العبادات على مذهب السادة المالكية للشيخ عبد الباري العشماوي الرفاعي. Allah ya sakama Malam da alkhairi ya gafarta masa kurakuransa tare da sauran Malamanmu. Mu kuma albarkaci rayuwanmu, ya bamu ilimi mai albarka ya bamu ikon aiki da ilimin. Littafinmu na gaba shine Iziyya in Shaa Allah agaba kadan. Abinda muka fada daidai Allah yabamu ladansa, wanda mukayi kuskure ya gafarta mana, ya fahimtar damu kuma yabamu ikon gyarawa. سبحانك اللهم وبحمدك نشهد أن لا إله إلا أنت نستغفرك ونتوب إليك. ALFIRDAUS TAHIR ALIYU DA UMMU MUSADDAD ISLAMIC QIESTIONS N ANSWERS

27/03/2017

ALFIRDAUS TAHIR ALIYU DA UMMU MUSADDAD ISLAMIC QIESTIONS N ANSWERS AL- ASHMAAWIY Bismillah wassalatu wassalamu ala rasulillah. (23) CIGABA DA KARATU CIKIN BABIN AZUMI Malam yace: Duk abinda ya qaraso zuwa maqogoro amman ba ta baki ya bi ba da kunne, da hanci da makamantansu koda bakhuur ne toh ramuwa kawai zaiyi, ko misali irin kaki (majina) da zaka iya zubarwa. Sannan abinda yake galibi na kurkuran baki da yin asuwaki, dama dukkan abinda yake iya zuwa ciki koda alluran ruwa ne, haka wanda ya ci abinci bayan koken rashin lafiya da alfijir duka wannan babu komai akansu sai ramuwa. Amman ramuwa bata lizimtarshi in quda ya shige mishi ko quran kan hanya ko gari ko auna farar qasa ga me sanarshi, ko kuma allura ta dubura, ko ciwo da yake bude ana sa mai magani. kuma ya halatta ga me azumi yin asuwaki aduka yininshi, haka ya halatta ya kurkura baki don qishi, da wayan gari da janaba (ya wayi gari da janaban da ya sameta tun kafin fitowan alfijir, in yaso bayan fitowan alfijir ya yi wanka). Mai ciki idan taji tsoro ma abinda ke cikinta sai tasha azumin amman bazata ciyar ba, wasu kuma s**ace zata ciyar. Mai shayarwa idan taji tsoro ma yaronta kuma bata samu wanda zata shayar mata dashi ba (ta dauki wata haya don shayar da yaron) ko kuma yaron bazai karbi na wata ba sai ita, toh zata iya shan azumi sai ta ciyar, haka tsoho tukuf zai ciyar idan ya shaa azumi, haka wanda yayi sakaci gurin rama azumin ramadan har wata ramadan din ta shigo, duka ciyarwan dake cikin wannan shine mudu daya akan kowace ranan da zai ranka. Kuma anso (Mustahabbi) Me azumi ya kame harshensa, da gaggauta rama abinda ke wuyanshi na azumi da jerashi. Nan zamu dakata in shaa Allah, mako mai zuwa zamu cigaba daga inda muka tsaya. Abinda muka fada daidai Allah yabamu ladansa, wanda mukayi kuskure ya gafarta mana, ya fahimtar damu kuma yabamu ikon gyarawa. سبحانك اللهم وبحمدك نشهد أن لا إله إلا أنت نستغفرك ونتوب إليك.

27/03/2017

ALFIRDAUS TAHIR ALIYU DA UMMU MUSADDAD ISLAMIC QIESTIONS N ANSWERS AL- ASHMAAWIY Bismillah wassalatu wassalamu ala rasulillah. (22) CIGABA DA KARATU CIKIN BABIN AZUMI Malam yace: Yana daga cikin sharuddan ingancin azumi yin niyya kafin alfijir na farilla ne ko nafila. Sannan niyya daya ta wadatar ma sauran azumin da suke bibiyan juna, kaman azumin ramadan da azumin kaffarar zihari, da na kisa, da alwashin da mutum ya kallafama kansa, Amman azumin jerawa ko wani ayyanannen rana (wanda a asali ba wajibi bane ya jeranta saidai misali ace shi al'adarshi duk alhamis sai yayi azumi da makamancin haka) to wannan babu makawa duk in zeyi ya ringa kwana da niyya. Cikin sharuddun ingancin azumi akwai tsarkakuwa daga jinin haila da nifaasi, idan jinin hailan ko nifaasi (jinin haihuwa) ya dauke kafin alfijir koda da second ne toh azumin wannan rana ya wajaba akanta kuma ko da bata yi wanka ba har sai bayan alfijir. Sannan ana sake niyya idan jerantawan azumin ya tsinke da ciwo ko haila ko nifasi da makamancinsu (maana in wani abu ya dakatar dakai daga jeranta azumin to randa zaka cigaba to fa sai ka sake daura niyya). Haka cikin sharuddan ingancin azumi akwai hankali, wanda bashi da hankali kaman mahaukaci da wanda ya suma azuminsu basa inganta awannan yanayin, amman yana wajaba akan mahaukacin idan hankalinshi ya dawo ko da bayan shekaru ne masu yawa daya rama abinda ya kubuce mishi na azumi alokacin haukanshi. Haka ma wanda ya suma idan ya farfado. Yana cikin Sharuddan ingancin azumi barin jimaa'i, da ci da sha. Duk wanda ya aikata haka acikin yinin ramadan da gangan batare da wata mafaka ta kusa ba kuma ba jahilci ba toh lallai zai rama wannan azumin tare da kaffara. Kaffaran kuwa shine ciyar da miskinai guda sittin 60, zai ciyar da kowani miskini daya mudu da mudunNabiy, wannan shi yafi, (in bai da halin hakan) to sai yayi kaffaran da 'yanta baiwa mumina ko yayi azumin wata biyu ajere. Nan zamu dakata in shaa Allah, mako mai zuwa zamu cigaba daga inda muka tsaya. Abinda muka fada daidai Allah yabamu ladansa, wanda mukayi kuskure ya gafarta mana, ya fahimtar damu kuma yabamu ikon gyarawa. سبحانك اللهم وبحمدك نشهد أن لا إله إلا أنت نستغفرك ونتوب إليك.

27/03/2017

ALFIRDAUS TAHIR ALIYU DA UMMU MUSADDAD ISLAMIC QIESTIONS N ANSWERS AL- ASHMAAWIY Bismillah wassalatu wassalamu ala rasulillah. (21) BABIN AZUMI Azumin ramadan farilla ne, kuma ana tabbatar dashi ne da cikan watan sha'aban ko da ganin watan Adilai, ko jamaa masu yawa, haka ma lokacin shanruwa (ganin watan sallah wanda dashi zaayi amfani a aje azumi), kuma ana kwana da niyyan azumi tun daga farkonshi, amman basai ka cigaba da kwana da niyya ba asauran kwanakin ramadan, sa'annan ana cike azumin zuwa dare (faduwan rana), yana daga cikin sunna gaggauta bude baki da jinkirta sahur, kuma duk aka tabbatar da ganin wata kafin fitowan alfijir to azumi ya wajaba, in kuma baka tabbatar da ganin watan ba har sai bayan alfijir to kame baki ya wajaba, kuma dole arama azumin wannan ranan.(saboda baka jira atabbatar da aganin wata ba don ka kwana da niyyanka kenan baka da niyya.) Kuma yin niyya kafin atabbatar da ganin wata bataccene ko da kuwa kayi niyya kafin aga wata sa'annan ka tashi da safe baka ci ba baka shaa ba sai ya bayyana ganeka ai wannan ranan cikin ramadan ne (wato ai anga wata an fara azumi) toh wannan bai wadatar maka ba, zaka kame daga ci da shaa acikin wannan yinin saboda falalan watan (dukda kai baka da azumin wannan yinin) kuma zaka ramashi. Sa'annan bazaka azumci ranan shakka ba saboda ka hadeshi da ramadan (ranan shakka, shine misali baka tabbatar da cewa anga watan ba, sai ka dau niyya cewa in ya tabbata dai anga watan to ina azumin ramadan, in kuma baa gani ba to ina azumin nafila, to baa yin haka kana shakkan niyya atsakanin abubuwa biyu) amman ya halatta ka azumci ranan shakkan don yin azumin nafila in yadace da ranan (misali ka saba duk alhamis ko litinin kana azumi to yau sai gashi anasa rai da ramadan din toh in bai tabbata ba babu laifi ka cigaba da azumin da ka saba) ko na alwashi. Kuma Mustahabbi ne kame baki afarkonshi saboda mutane su tabbatar da ganin watan, idan har rana ta d**o amman babu labarin anga wata to sai mutane su ci abinci. Wanda amai ya kwace mishi bazai ci abinci ba azuminsa na nan sai in shine ya qaqaro aman toh zai rama azumin wannan ranan, wanda yayi mafarki azuminsa bai karye ba, haka wanda akayima qaho, amman an karhanta yin qaho ga mara lafiya saboda tsoron kar ya tagayyara. Nan zamu dakata in shaa Allah. Abinda muka fada daidai Allah yabamu ladansa, wanda mukayi kuskure ya gafarta mana, ya fahimtar damu kuma yabamu ikon gyarawa. سبحانك اللهم وبحمدك نشهد أن لا إله إلا أنت نستغفرك ونتوب إليك.

27/03/2017

ALFIRDAUS TAHIR ALIYU DA UMMU MUSADDAD ISLAMIC QIESTIONS N ANSWERS AL- ASHMAAWIY Bismillah wassalatu wassalamu ala rasulillah. (20) Cikin karatunmu na wannan littafi in bamu manta ba awancen makon mun tsaya cikin babin jana'iz, wanda muka tsaya a cikin adduan da akeyi in yaro ne mai rasuwan. Toh yau zamu cigaba daga inda muka tsaya. Malam ya cigaba da cewa: اللهم ألحقه بصالح سلف الصالح المؤمنين في كفالة إبراهيم وأبدله دارا خيرا من داره، وأهلا خيرا من أهله، وعافيه من فتنة القبر، ومن عذاب جهنم. Yaa Allah ka sada shi da Magabata na kirki Muminai cikin kulawar Annabi Ibarahim, Kuma ka masanya masa da gida wanda yafi gidansa alkhairi, da ahalin da s**a fi ahalinshi alkhairi, Kuma ka tsareshi daga fitinar qabari, da kuma azaban jahannama. Zaka fadi hakan ne ayayin kowace kabbara, sa'annan bayan kabbara ta hudu sai kace: اللهم اغفر لأسلافنا وأفراطنا ولمن سبقنا بالإيمان. اللهم من أحييه منا فأحيه على الإيمان، ومن توفيته منا فتوفه على الإسلام، واغفر للمسلمين والمسلمات والمؤمنين والمؤمنات الأحياء منهم والأموات. Yaa Allah ka gafartama Magabatanmu, da wanda s**a rigayemu da alkhairi, da kuma wanda s**a rigayemu da imaani. Yaa Allah wanda Ka rayar dashi cikinmu to ka rayar dashi akan imaani, wanda kuma ka karbi ransa toh ka karbi ransa yana Musulmi, Ka gafarta ma Musulmai maza da Musulmai mata, da Muminai maza da Muminai mata, rayayyu cikinsu da matattu. Sai kayi Sallama, Wallahu aalam. Nan muka zo qarshen wannan babin kuma nan zamu dakata, in shaa Allah mako mai zuwa zamu shiga BABIN AZUMI. Allah ya datar damu alkhairan duniya da lahira Ya kyautata qarshenmu Ya sanya Aljannatul firdaus ce makomarmu baki daya. Abinda muka fada daidai Allah yabamu ladansa, wanda mukayi kuskure ya gafarta mana, ya fahimtar damu kuma yabamu ikon gyarawa. سبحانك اللهم وبحمدك نشهد أن لا إله إلا أنت نستغفرك ونتوب إليك

27/03/2017

UMMU MUSADDAD DA ALFIRDAUS TAHIR ALIYU AL- ASHMAAWIY Bismillah wassalatu wassalamu ala rasulillah. (19) Cikin karatunmu na wannan littafi mai albarka in yan uwa basu manta ba muna cikin babin jana'iza. Inda mun gama magana akan addua ma namiji in ya rasu. Yau in shaa Allah zamuji in mace ce yaya nata adduan zai kasance. Malam yace: Idan kuma Sallar na mace ne sai kace: اللهم إنها أمتك. Allahumma innaha amatuk. Yaa Allah lallai ita baiwarka ce, sai ka cigaba da karanto addu'oin da lamirin mata (wadan can adduoin da mukayi abaya 17,18 wanda akeyi ma namiji), saidai ita bazaka ce amasanya mata miji mafi alkhairin mijinta ba, saboda ita ba mamaki ta zama mata ga mijinta na duniya a aljanna. Su ko matan aljannah an tsaresu ne ga mazajensu basu buqatan amasanya masu su. Idan kuma ka riski jana'iza baka san ko mace bane ko namiji sai kace: اللهم إنها نسمتك. Allahumma innaha nasamatuk. Yaa Allah lallai ita halittarka ce, daga nan sai ka cigaba da ambatonta akan lamirin mace domin kalmar "Annasamah" ya qunshi mace da namiji. Idan kuma Sallar jana'izar na yaro ne sai kayi abinda ya gabata na niyya da kabbarori da addua. Saidai Mustahabbi ne kace bayan kayi yabo ga Allah da Salati wa Annabi SWA: اللهم إنه عبدك وابن عبدك أنت خلقته ورزقته وأنت أمته وأنت تحييه. اللهم اجعله لوالديه سلفا وذخرا وفرطا وأجرا، وثقل به موازينهما، وأعظم به أجورهما، ولا تحرمنا وإياهما أجره، ولا تفتنا وإياهما بعده. Yaa Allah lallai shi bawanka ne, Dan bawanka, Kai ka halicceshi kuma ka azurtashi, Kuma kai ka karbi ransa Kuma kai zaka sake rayashi. Yaa Allah kasanyashi ya zama wani taska wanda ya rigayi iyayenshi kuma ya zame musu alkhairi alahira, ya zama sunsami lada (na haqurin rashi) wanda zai nauyaya a ma'aunansu, ka girmama ladansu dashi, Kuma kada ka haramta mana mu dasu ladanshi, Kuma kada ka fitinemu dasu abayanshi. Zamuji qarshen addu'an amako mai zuwa in shaa Allah. Abinda muka fada daidai Allah yabamu ladansa, wanda mukayi kuskure ya gafarta mana, ya fahimtar damu kuma yabamu ikon gyarawa. سبحانك اللهم وبحمدك نشهد أن لا إله إلا أنت نستغفرك ونتوب إليك.

27/03/2017

UMMU MUSADDAD DA ALFIRDAUS TAHIR ALIYU AL- ASHMAAWIY Bismillah wassalatu wassalamu ala rasulillah. (18) Yan uwa in baku manta ba satin da ya gabata mun tsaya ne a babin janaza inda muke kan adduoin da ake ma gawa alokacin da ake mai sallah, yau zamu cigaba daga inda muka tsaya in sha Allah. Malam ya cigaba da cewa: Allahumma in kana muhsinan fazid fi ihsaanihi wa in kana musi'an fatajaawaz an sayyi'aatihi. Allahumma innahu qad nazala bika wa anta khairu Manzulin bihi, faqirun ila rahmatika wa anta ganiyyun an azabihi. Allahumma thabbit indal mas'alati mandiqahu wala tabtalihi fi qabrihi bimala daqata lahu bihi, wa alhiqhu bi nabiyyihi Muhammad sallallahu alaihi wasallam. Yaa Allah in ya kasance mai kyautatawa to ka qara acikin kyautatawansa, in kuma ya kasance me sabo toh ka gafarta masa laifuffukanshi, Yaa Allah lallai gashi nan ya sauka gareKa kuma Kai ne mafi alkhairin wanda zaa sauka gareShi, mabuqacine ga rahamarka Kai kuma wadatacce ne ga barin azabtar dashi, Yaa Allah ka tabbatar da harshensa lokacin tambaya (ka bashi ikon amsa tambayoyin qabari), kuma Kada ka jarabceshi aqabarinshi da abinda bazai iya ba, kuma Ka sadashi da Manzonsa Muhammad SWA. Allahumma la tahrimnaa ajrahu wala taftinnaa ba'adahu. Ya Allah kada ka haramta mana ladansa kuma kada ka fitinemu abayansa. Zaka fada haka ne ayayin kowane kabbara, bayan kabbara ta hudu kuma sai kace: Allahummagfir li hayyina wamayyitina wa hadirina wa gaa'ibina wa sagiirina wakabiirina wazakarina wa unthaana innaka ta'alamu mutaqllabana wamathwaana, wagfirlana waliwaalidaina waliman sabaqanaa bil iimaan magfiratan azman, walilmuslimina walmuslimaati walmuminina walmuminati al'ahyaa'i minhum wal'amwaati. Allahumma man ahyaytahu minna fa'ahyihi alal imani waman tawaffaitahu fatawaffahu alal islami wa as'idna biliqaa'ika wadayyibna lilmauti watayyibhu lana, waj'al fihi raahatana wamasratana. Sannan sai kai sallama. Yaa Allah ka gafarta ma rayayyenmu da mattaccenmu da wanda yake nan da wanda baya nan, da qarami cikinmu da babba, da mace da namiji, lallai kai ne kasan jujjuyawanmu da kuma makomarmu, Kuma Ka gafarta mana da Iyayenmu da wadanda s**a rigayemu da imaani gafara mai girma, da Musulmai maza da Musulmai mata da kuma Muminai maza da Muminai mata rayayyu cikinsu da matattu. Yaa Allah duk wanda ka rayashi acikinmu toh ka rayashi akan imaani, wanda kuma ka dauki ranshi to ka dauki ranshi akan Musulumci, Kuma ka faranta mana da Haduwa da Kai, ka sanyamu mu zama mutanen kwarai kuma ka sanya mutuwa tazo mana da sauqi (ta yanda zamu ga Mala'ikun rahama ba na azaba ba) Kuma ka sanya ta zama (mutuwar) hutu agaremu da Kwanciyan hankali. Sai kayi Sallama. Zamu dakata anan in sha Allah sai karatu na gaba in Allah ya kaimu zamu cigaba daga inda muka tsaya. سبحانك اللهم وبحمدك نشهد أن لا إله إلا أنت نستغفرك ونتوب اليك

27/03/2017

ALFIRDAUS TAHIR ALIYU DA UMMU MUSADDAD ISLAMIC QIESTIONS N ANSWERS AL- ASHMAAWIY Bismillah wassalatu wassalamu ala rasulillah. (16) Cikin karantunmu na wannan littafin mai albarka in bamu manta ba yau zamu tashi akan ladubban Sallar jumaa'a. Malam yace: LADUBBANSA KUMA GUDA TAKWAS NE:- 1-Yin wanka dominta, kuma Sunnace agurin jumhur, sannan daga cikin sharadinsa shine ya kasance hade yake da tafiya masallaci, da zaiyi wankan sannan ya shagala da cin abinci ko barci toh zai sake wankan akan abinda yake mashhuri. 2-Yin asuwaki. 3-Aske gashi. 4-Yanke farce (qumba). 5-Nisantar duk abinda zai haifar da warin da baaso. 6-Yin ado da kaya masu kyau. 7-Yin kwalliya dominta/sanya turare. 8- Tafiya ga sallar aqafa banda hawa abin hawa sai in akwoi uzurin da zai hana hakan. UZURUKAN DA KE HALATTA RASHIN ZUWA MASALLACIN AKWAI:- -Ruwan sama mai tsanani -Ta6o me yawa -Kuturun da warin kuturtan ke cutar da jamaa -Rashin lafiya -Me jinya, ya zamana yanada wani mara lafiya cikin ahalinsa kamar Mata ko Da ko daya daga cikin iyaye, kuma babu wani da zai kula dasu sai shi toh yana buqatan ya tsaya yayi jinyarsa. Hakama idan mutuwa ta halarto ma daya daga cikin makusantansa ko 'Yan uwansa. Malik yace akan mutumin da ya mutu ranan jumaa sai wani cikin en uwansa ya tsaya don kula da sha'aninsa (kula da shaaninsa na daga wanka da sutura da birnewa) toh wannan duk babu laifi ciki. - Haka wanda yajiyema kanshi tsoron bugun wani azzalumi ko atsareshi a qwace mashi dukiyanshi, ko wanda ake binsa bashi yaji tsoron kar wanda yake binshi bashin yakamashi duk yahatta akan (magana) mafi inganci. -Haka makahon da bashi da me mai jagora, amman in yanada me jagora ko yana cikin wanda basai anmusu jagoranci ba ze iya zuwa to baya halatta yaqi zuwa. ABABEN DA AKA HARAMTA DANGANE DA JUMAA -Kuma an haramta tafiya (zuwa wani gari) lokacin da rana tayi zawali ranan jumaa ga wanda jumaa ta wajaba akanshi -Haka yana haramta yin Magana ko Nafila lokacin da liman ke huduba duk dayane ko hudubar farko ko ta biyu. Mutum zai zauna ne bazaiyi wata sallaba (nafila)sai in yana cikin yin nafilan ne kafin liman ya shigo to sai ya qarasa yinta (in kafara kafin liman yashigo to bazaka katse ba ko liman ya shigo sai ka qarasa, abinda baaso shine dacan kana zaune baka tashi yiba saida liman yashigo sai ka miqe zakayi nafila toh wannan shine Malam yace ya haramta). -Haramun ne cinikayya lokacin kiran Salla na biyu, kuma ana warwareshi ko anyi. MAKRUHAAT/ABINDA BAASO DANGANE DA JUMAA -Makruhi ne barin aiki ranan jumaa. -Da yin nafilan liman kafin huduba -haka ankarhanta wanda yake zaune (cikin masallaci) yayi nafila lokacin kiran sallar farko. -Haka an karhanta budurwa ta halarci jumaa. -Haka yin tafiya bayan alfijir. Allah shine masani. Abinda muka fada daidai Allah yabamu ladansa, wanda mukayi kuskure ya gafarta mana, ya fahimtar damu kuma yabamu ikon gyrawa. Subhanakallahumma wabi hamdik nashhadu anla Ilaha illa Anta, nastagfiruka wa natubu ilaik.

Address

Yola

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jibwis Yola West posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share