27/03/2017
ALFIRDAUS TAHIR ALIYU DA UMMU MUSADDAD ISLAMIC QIESTIONS N ANSWERS AL- ASHMAAWIY Bismillah wassalatu wassalamu ala rasulillah. (21) BABIN AZUMI Azumin ramadan farilla ne, kuma ana tabbatar dashi ne da cikan watan sha'aban ko da ganin watan Adilai, ko jamaa masu yawa, haka ma lokacin shanruwa (ganin watan sallah wanda dashi zaayi amfani a aje azumi), kuma ana kwana da niyyan azumi tun daga farkonshi, amman basai ka cigaba da kwana da niyya ba asauran kwanakin ramadan, sa'annan ana cike azumin zuwa dare (faduwan rana), yana daga cikin sunna gaggauta bude baki da jinkirta sahur, kuma duk aka tabbatar da ganin wata kafin fitowan alfijir to azumi ya wajaba, in kuma baka tabbatar da ganin watan ba har sai bayan alfijir to kame baki ya wajaba, kuma dole arama azumin wannan ranan.(saboda baka jira atabbatar da aganin wata ba don ka kwana da niyyanka kenan baka da niyya.) Kuma yin niyya kafin atabbatar da ganin wata bataccene ko da kuwa kayi niyya kafin aga wata sa'annan ka tashi da safe baka ci ba baka shaa ba sai ya bayyana ganeka ai wannan ranan cikin ramadan ne (wato ai anga wata an fara azumi) toh wannan bai wadatar maka ba, zaka kame daga ci da shaa acikin wannan yinin saboda falalan watan (dukda kai baka da azumin wannan yinin) kuma zaka ramashi. Sa'annan bazaka azumci ranan shakka ba saboda ka hadeshi da ramadan (ranan shakka, shine misali baka tabbatar da cewa anga watan ba, sai ka dau niyya cewa in ya tabbata dai anga watan to ina azumin ramadan, in kuma baa gani ba to ina azumin nafila, to baa yin haka kana shakkan niyya atsakanin abubuwa biyu) amman ya halatta ka azumci ranan shakkan don yin azumin nafila in yadace da ranan (misali ka saba duk alhamis ko litinin kana azumi to yau sai gashi anasa rai da ramadan din toh in bai tabbata ba babu laifi ka cigaba da azumin da ka saba) ko na alwashi. Kuma Mustahabbi ne kame baki afarkonshi saboda mutane su tabbatar da ganin watan, idan har rana ta d**o amman babu labarin anga wata to sai mutane su ci abinci. Wanda amai ya kwace mishi bazai ci abinci ba azuminsa na nan sai in shine ya qaqaro aman toh zai rama azumin wannan ranan, wanda yayi mafarki azuminsa bai karye ba, haka wanda akayima qaho, amman an karhanta yin qaho ga mara lafiya saboda tsoron kar ya tagayyara. Nan zamu dakata in shaa Allah. Abinda muka fada daidai Allah yabamu ladansa, wanda mukayi kuskure ya gafarta mana, ya fahimtar damu kuma yabamu ikon gyarawa. سبحانك اللهم وبحمدك نشهد أن لا إله إلا أنت نستغفرك ونتوب إليك.